Chapter 23
Chapter 23
Page 23/24 _Bismillahir-rahmanir-raheem. _____Acan gida kuwa bayan Daddy sun dawo daga sallar magrib anan suka sake tattaunawa inda Sauban ya daddage akan shine zai ciro duk abubuwan nan da akace don Taufeeq sosai ya tsorata yakuma nuna tsoron nashi a bayyane. Duk sunji dadi,anan aka yanke hukuncin jibi Sauban zasu koma dasu Aseef don daga Aseef har mahaifiyar shi babu wanda yasan halin da ake ciki. ***** "Gaskiya Guggo kiyi dagaske inba haka ba Sauban na gab da subucemun, Akeela tayi maganar tana turo mouth gaba. Dan harara Guggo Laure ta aika mata dashi tace"inyi dagaske?ko kema kiyi da gaske?bari kiji inaso ki shirya kikoma gidan da zama sannan ba sasan kowa zaki sauka ba saina Aisha,ke bakisan zamanin ba saida kissa da kisisina? "Amma Guggo kinsan Daddy da wuya ya yarda sai dai idan ke zakiyi mishi magana. "Badole ya yarda ba?yanzu kije kihada duk wani abin bukatanki yanzu zansa waya nakirashi,saboda da wuri nakeso kije gidan,koda nida kaina ma zankaiki. Akeela tayi murmushi tace"yawwa Guggo dama ke yakamata kikaini. "Aiko zankaiki kedai jeki hada kaya yanzu zankira manseer din a wayata,cike da farin ciki Akeela tafita tanufi gate kaitsaye dama ana jiranta a waje,Suby tabita da wani kallo tace. "Wallahi kina ruwa akeey kinsan mommy daharatu tana fushi dake tunda taji ansa miki ranar aure?tace kin munafunce kungiya? wallahi babu ruwana. A razane Akeela take duban Suby wani mulmulallen ashariya tasaki"kutumar ubancan uban waye yafada mata? wani munafuki ne zai sanar mata? Wani banzan kallo Suby tayi mata tace"lallai ma akeey kinmanta abubuwan da kika dingayi a tiktok da IG dinki?magana tariga tanata trending a social media?har 'yan bakin ciki suna bayyana kawunansu. "Mtsewwww to wallahi babu Wanda ya isa ya hanani aure kamar yanda babu wanda ya isa yahanani neman mata da binsu,ina son aure don kinsan nidama nimai son harkan nanne inason wancan abinma,haka kuma inason madigo,to aknme ban matsama wani ba wani yanemi matsamin. Kinga rakani naje wajen mommyn inshawo kanta nasan harda takaicin rashin ganina da batayi bane kwana biyu. Suby murmushi tayi tace"lallai akeey wai kinmanta mommy da sharrin ta kenan?juyar dakai Akeela tayi inda banda bugawa babu abinda kirjinta keyi. "Hmmm Suby nifa inaso ma nadena wannan harkan kwatakwata tunda Allah yabani miji wanda babu abinda yarasa. Suby tace"kina nufin zakibar kungiya?to kindebo ruwa kuma komai tayi miki kece kikaja. "Naji don Allah mubar maganar nan. Washegari wajen karfe 7:30 su ya Sauban suka nufi filin jirgi,a lokacin ne babu jimawa Guggo Laure da Akeela suka isa Galadima family,sosai Galadima da Bodejo bsukayi mamakin ganinsu,don shi Galadima ma yana bedroom dinsa Zuhra na matsamai kafafuwa. Cike da natsuwa take tafiya koda tashigo parlon kallo daya tama su Guggo Laure ta kauda kai saboda wani irin kallo da Akeela ta aika mata dashi,cikin natsuwa tasamu kusa da Bodejo ta zauna tace"Bodejo barka da safiya Ina kwana? "Lafiya Lou Zuhra harkin gama matsa masa kafafuwan? "Ea nagama don har na hada masa ruwan wanka yashiga kema yanzu zanje na hadamiki. "Yawwa Allah yamiki albarka yabaki miji nagari mejin kanki da kaunar ki. "Ameen Bodejo na,tayi magana kaitsaye tare da mikewa tace"bari nashiga wanka saboda zanje school"duban Guggo Laure tayi tace. "Guggo kune da sammako haka?sai kace wacce ake koranki daga gida?tayi maganar cike da zolaya. Guggo Laure tace"nida gidan mu?ai babu maganar sammako anan Fatima kinsan da zafi-zafi ake bugun karfe. Murmushi Zuhra tayi tace"gaskiya ne to sannu da zuwa,tana gama fadar haka tanufi dakinta. Basu dade da zama ba Galadima yashigo inda Bodejo tashiga hada masa breakfast,duban Akeela tayi tace"tashi kihado muku abin kari. Dan yatsina tayi tana mikewa tanufi kitchen din Bodejo tana wani karairaya uwa zata balle tanufi kitchen din. "Laure kece da safennan haka? Allah yasa lafiya dai? Dan murmushi Guggo Laure tayi tace"Yaya muhammadu kenan kunata fadin sammako kamar wacce tayi asibanci?nikam maganar yaran nan yakawoni......au Wai kaji,tayi subul da baka. "Au Akeela nakawo nan ta zauna koda sati biyu ne zuwa uku tayi anan tafara sabawa da gidan duk da gidan su ne. Kallon kallo aka shiga yi tsakanin Bodejo da Galadima. Sauke ajiyan zuciya Galadima yayi yace"toh ai Shikenan sai su zauna da Zuhra a dakin zuhran koh? Da sauri Guggo Laure tace"A'ah ba haka za'ayi ba,ni nace taje can,tanufi wajen Aisha ta zauna tadinga tayata ayyuka abubuwan bukata ko kuwa? Gwalo idanuwa Bodejo tayi cikin mamaki tace"a bangaren surukar tata zata zauna?tun kafin akawo ta gidan? Dan tabe baki Guggo Laure tayi tace"Toh menene aciki? Aisha fa uwarta ce koda kuwa ba maganarta da Sauban. Dan murmushi GALADIMA yayi yace"Laure kenan ninakan rasa a Ina kika samu wannan wayewar kamar jinin fulani baya yawo a jikinki,ita Aishan tanuna miki bukatan son akeela tazo ne?koko tace miki bata da maid's ne? Guggo Laure tatsuke fuska tare da kankantar da idanuwa tace"yanzu munkoma gida kenan?to ai shikenan babu komai takarisa maganar tana latso hawaye tare da mikewa. "Dakata!!! Inazaki a haka?Akeela dai kika kawo ta zauna koh?to Shikenan kidauke ta kikaita wajen Aishan. Guggo Laure tamike inda Akeela kuwa tuni taja trolley dinta tafice cikin jindadi. *******KADUNA******* Sosai Ummie taji dadin ganinsu ya Sauban tarasa inda zata Sanya kanta don murna,haka tasa me aikinta takawo musu breakfast don wajen 9:30 suka iso shikuwa Aseef kaitsaye BQ yanufa batare da yaje gaida Ummie ko Mommy ba,koda yashiga wanka yasakeyi yacanja kaya,don sunyi da wata yarinya zasu hadu zai kama mata daki daga adamawa. Gidan tsohon governor jahar kaduna sukaje shida Taufeeq wajen abokinsa Hamid anyi biki Sauban baisamu zuwa ba kuma sosai ran Hamid yabaci,don ko zuwan baisan dashi ba. Basu suka shigo gidan ba sai wajejen Tara nadare shiyasa Ummie tarufe ido yadinga yimusu fada sosai,abinci tace suje dinning suci ita tawuce bangaren Abbie don tunda tadawo acan take kwana. Sunji dadin hakan sosai,sai da suka jira dare yayi nisa sosai misalin karfe sha daya sannan suka nufi bedroom din Ummie kaitsaye, Taufeeq yamiko ma Sauban man da su Daddy suka bayar sukace wanda zai dakko da hannunshi a cikinsu yashafa. Ansa Sauban yayi ya shafa tare dayin wasu addu'o'i sosai kana yaduka yakai hannunshi. Jikinsa ne yakama rawa saboda damko tukunyar kasan da yayi,kokarin fadi takeyi daga hannunshi kuma tabbas idan tafadi da matsala,jikinsa kuwa jiyake tamkar anjona mishi shock kota ko ina. Taufeeq bakaramin tsorata yayi ba saboda yanda yaga Sauban nayi,gashi duk wata jijiya dake kansa tafito banda zufa babu abinda yakeyi. Sauban kuwa jikinsa jiyake kamar ana yankan naman sa,jiyake kamar yasaki tukunyar amma taurin zuciyar shi bazaisa yayi hakan ba. Cikin yardan Allah dai yajawo tukunyar yadaukota,wani irin hayaki ne ke fita daga tukunyar,cikin sauri Taufeeq ya watsa garin maganin da malama Baba yabada a watsa,zuwa can kuma hayakin yafara raguwa,haka rawar da jikin Sauban keyi shima yafara raguwa,a hankali kuma komai ya lafa. Da sauri Taufeeq ya nannade tukunyar da wata bakar kyalle da aka basu, Sauban kuwa kamar jira yake a amsa yazube kan gadon,kansa namasa wani azababben sarawa. Ruwa Taufeeq yadauko masa anan fridge din Ummie dake dakin,da qyar Sauban ya iya tashi hannunsa dafe da kansa,idanuwansa sun kada sunyi jazur,sai da Taufeeq yatsorata daganin idanuwan Sauban. A haka Taufeeq yakamasa suka nufi bq yakaishi dakinsa don kowa da nashi dakin,sannan yace zai kwana anan don bazai iya tafiya yabarshi
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87