Chapter 84
Chapter 84
da Safeena ba taji hakan ba,a ranta tashiga gode ma Allah. Don haka yasa duk suka shiga ɗakin har lokacin tana bacci sosai,lokaci ɗaya tayi wani fayau ta faɗa,nan suka dudduba jikin ta inda duk suka tafi aka bar Sauban da Mom don su Taufeeq sunyi² ya taso suje yaƙi. Acan gidan biki kuwa anbar jama'a da jimami,koda suka koma nan suka cema mutane jikin nata da sauƙi, Ummie ce kawai aka sanar da ita abinda ke faruwa,nan fa su Mashahuda suka dasa chapter tsegumi wai dama ai wannan haske kwana biyu da tayi ga ƙirjin ta daya cika,nan dai suka dinga. A hospital kuwa Zuhra bata farka ba sai wajejen magrib,shima tana farkawa aman tafara ga cikinta da babu komai da ka kalleta kasan a matuƙar wahale take, Sauban kuwa gabaɗaya ya ruɗe har sai da yabawa Mom tausayi,da ƙyar aman ya tsaya,anan Mom ta kamata suka shiga toilet tayi alwala tayi sallah la'asar,sannan aka ɗan jinginar da ita saboda complain ɗin da takeyi na jiri da take gani. "Yaya yunwa nakeji"ta furta cikin wahalallen murya wanda daka ji kasan na marasa lafiya ne, Sauban cikin kulawa yace"mezaki cine baby?Girgiza kai Zuhra tayi tace"ina jin yunwa amma banjin cin komai"Mom tace"A'ah Zuhra ai dole kici wani abu ba zai yiwu ki zauna da yunwa ba fa gaskiya"ZUHRa wani wahalallen ƙwalla ne ya ziraro mata daƙyar tace"Mom idan naci amai zanyi na sani Kum.....ai bata ƙarisa ba aman kuwa ya taho ga uban wahala,don cikinta babu komai sai kakarin aman da takeyi,a lokacin nurse's ɗin ɗazu dake ta gulma ne suka shigo,nan suka shiga yi ma Zuhra ya jiki,a gefe guda suna satar kallon Sauban wanda ya tsuke face,ya tattare gabaɗaya hankalin shi ya koma kan matar sa. "Yaya nidai a maida ni gida bansan warin asibitin nan amai yake saka ni"tayi maganar a wahale, miƙewa Sauban yayi yace"Okay so bari nama Dr Ahmad magana gaskiya"sannan yasa kai ya fice,daga Mom har nurse's ɗin da kallo suka bita,kamo kafaɗun ta mom tayi tace"Zuhra kidaure kici wani abu koda zakiyi amai saboda idan cikin ki da akwai wani abu bazaki wahala kamar irin wanda kikeyi da cikin ki babu komai ba"ɗaga ma Mom kai Zuhra tayi,a dai-dai lokacin ne kuma Sauban suka shigo shida Dr Ahmad,hakan yasa nurses ɗin ficewa. Dariya Dr Ahmad yakeyi ya dubi Zuhra"Madam kinfi dai son komawa gida right? ɗaga mishi kai Zuhra tayi don har ga Allah warin asibitin damun ta yakeyi,a take anan kuwa ya rubuta mata sallama,inda Dr jamila zata dinga zuwa dubata, sannan sai ruwan hannun ta yaƙare zasu wuce. Godiya Sauban yama Dr Ahmad a kuma take anan ya tura masa 250,000 tukwicin sanar da wannan daddaɗan albishir ɗin,wani baccin Zuhra ta koma sai wajen magrib lokacin ma Sauban na masallaci, Mom ma sallan takeyi sannan Zuhra ta farka,yunƙurin miƙewa take yi amma jirin dake nema kada ta ne yasa takoma ta jingina tare da rintse idanuwan ta gam. Muryan Mom taji"Ya yadai Zuhra?jikin ne? ɗaga ma Mom kai tayi tace"jiri ne ke neman wahalar dani Mom,ga aman da nakeji har yanzu nina rasa meke samun jin aman? Mom tace"Ai haƙuri zakiyi Zuhra yanzu keda jin dai-dai kuma sai Allah ya sauke ki lafiya"wani kallo Zuhra ta ma Mom na rashin fahimta don har ga Allah bata son abinda ke faruwa ba,dariya Mom kawai tayi a lokacin Sauban yayi sallama ya shigo duk cikan su suka amsa,nufo su yayi tare da zama gefen Zuhra yace"Mom Yaya jikin nata?ta sake aman ne?? Mom tace"Jiki alhamdulillah Sauban complain ɗin ta ɗaya jirin da take gani ne kuma Dr Ahmad yace insha Allah zaiyi sauƙi a hankali tunda Dr jamila zata dinga zuwa gida kula da ita,don bayan fitan ka ma ta shigo mun daɗe da ita lokacin ma Zuhran tana barci". "Masha Allah, Allah ya ƙara lafiya,to ai sai muyi shirin tafiya ko Mom? Mom tace"Okay muje Toh. Duban Zuhra Sauban yayi yace"hey beb zaki iya tafiya?Zuhra tace"ka mance nace ma ina ganin jiri kawai kama ni zakayi muje"kama ta yayi Mom ta gyara mata mayafin ta sannan suka fice,har mota ya saka ta don yaso shiga office ɗin Dr Ahmad but ya tashi. Haka ya ɗauko su,suna tafiya da yake hanyoyin akwai street light hakan yasa duk inda ka wuce haske ƙau,har zasu wuce ya jiyo muryan ta,da yake suna baya ne kanta na kan kafaɗar Mom"Yaya ga me balango can"dakata wa yayi yace"zaki ci ne? ɗaga masa kai Zuhra tayi,samun waje yayi yai parking sannan yafice, yaɗau almost 4mint sannan ya shigo,hannunsa ɗauke da ledoji uku ɗaya madaidaici, ɗaya ya fishi, ɗayan kuma duk ya fisu yawa,haka suka ƙarisa, dai-dai wani shagon da ake saida yoghurt ya tsaya ya sai manyan robobi huɗu sannan ya dawo ya shiga motan ya tayar. A haka suka isa kaitsaye Galadima family ya wuce da ita sashin Ammi,kama ta yayi ya kaita, Mom kuwa apartment ɗin ta tawuce saboda Hajiya Biba tana nan,don biyo su Ammi sukayi suka dawo ɗazu. ******** Kowa tambayar jikin nata yakeyi,haka amare duk sun shisshigo sun tasa ta a bedroom ɗin da aka sauke ta,su Aunty Maryam da Aunty labeeba duk suna tare da ita sai sannu ake mata masu sharri nayi,ita dai Zuhra kunya ta saka ta a gaba duk bakin ta takasa furta komai. Sauban da kanshi ya kaima Mom na manta har apartment ɗin ta da yoghurt,godiya sosai tayi masa,inda shida Kareem suka ɗauki Hajiya Biba don maida ta gida,suna zaune har kusan 9:00 sannnan ya shigo,hakan yasa siɗif² suka fara ficewa cikin su na ɗuran ruwa,turo mouth gaba, Zuhra tayi tace"ƙarfi da yaji ka zama kaman wani mala'ikan mutuwa da angan ka sai a shiga taitayi"harara Sauban ya galla mata yace"kema ai saboda kin ganni tsirara ne shiyasa kika rainani haka,kuma zanyi maganin ki"dariya Zuhra tasa tace"Sorry Babyn Baby". "Kinci abinci?yayi mata tambayar tare da jawo ledojin, Zuhra tace"ai baka zo ka bani balangon ba"ɗan murmushi Sauban yayi sannan ya buɗe komai ya shiga bata tana amsa idanuwan ta akan shi tana jin wani soyayyan shi,sai da yabata yaga taci ta ƙoshi sannan ya ƙyale ta suka cigaba hira,wanda rabi da kwata duk romance ɗin junan su sukayi,har sai da Zuhra ta mishi abinda ya samu natsuwa( Su Sauban manya😁🙄). Sai wajen 11:43 ya tashi shima sai Ammi ta shigo ta kora sa sannan wanda Zuhra kuwa a lokacin amai ta dinga sheƙawa,basuyi wani kwanan daɗi ba daga ƙarshe bedroom ɗin Ammi ta koma. *WASHEGARIN BIKI* Nihal da Laila kuka kawai sukeyi kamar ransu zai fita don sai da suka tayar ma da mutane da dama hankali sun saba komai tare gashi aure zai raba su duk da Laila after 2weeks zata koma saboda school hakan yasa Shuraim ya sama mata gidan haya a can,duk weekend zai dinga shiga kaduna, Nihal ita ta raka Laila gidan ta wanda yayi kyau ɗan dai-dai kasha Allah,wajen 10 aka kaita,ana dawowa ƴan k.d suma suka ɗauki amarya tare da duk wanda zai tafi motoci bakwai suka wuce. Zuhra dai nata ido don Sauban wayo ya mata anfito tafiya da amarya yaja ta gidan su,yaci karen sa babu babbaka,wanda sosai zubar ke kuka don wani mugun tsanar abin ta tsinci kanta daji duk da kuwa itama ta samu natsuwa,ko kaɗan bata
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87