Chapter 27
Chapter 27
Lallai Alqalami 🖊️ yafi takobi🗡️ 14/4/23. [5/4, 14:37] Xahratty (OUM AJMAL): 👨🏽🦳 *_GALADIMA FAMILY_*👨🏽🦳 Story&Written By *FATEEMA ZAHRA LAWAL* Marubuciyar⤵️ A DALILIN'YAR TSINTUWA. MIJIN ZAHRA. DIAMOND LADIES ( Daukar fansa)paid book. RUHIN AMRITA (FATALWA CE). Now *_GALADIMA FAMILY_* Page 29/30 _Bismillahir-rahmanir-raheem._ *BARKAN KU DA SALLA MASOYA FATAN ANYI SALLAH LAFIYA,WADANDA SUKA RIGAYEMU GIDAN GAAKIYA ALLAH YAJIKANSU.....YAWWA NACE BA GORON SALLAH KADA A MANTA DUK WANDA ZAI BADA YAZO A BASHI ACCOUNT NUMBER😁HAR NAMAN SALLAH DA CIN-CIN ZA'A IYA TUROWA TA ACCOUNT.* *DUBUN GAISUWA A GAREKU MAMAN ASLAM,MMN TAUFEEQ,UMMU MEE'AD,GODIYA DA TARIN KULAWA.* ________Gabadaya dakin daga masu tayasu kuka sai masu juriya haka suka kasance, Zuhra kuwa wani irin nishadi takeji wanda tunda take bata tabajin irin sa ba. Nan Galadima yake sanar dasu abinda yafaru,babu wanda baishiga shocked ba, Ummie haka ta taso ta rungume Sauban tana me sake zubda hawaye cikin muryan kuka tace. "Nagode son Allah ya saka maka da mafificin alherinsa bazan taba manta kaba a rayuwa ta, Allah ya dafa maka a lamuran ka. Amma tace"ubangii Allah ya baka mata tagari me kula dakai Allah ya daukaka duniya da lahira. Gabadaya dakin sai amsawa akeyi da amin,ita kuwa Mom takaicin irin addu'o'in da ake kwaranyo ma Sauban takeji,domin ji take kamar ta shake shi ya mutu kowa ma ya huta,banda yaqe babu abinda takeyi. Anan suka sake godiya ga Allah akayi addu'o'i suka dunguma kuma jabi road don Ummie sarai ta warke, Zuhra na maqale a gefenta. Ko kafin su iso Abba yasa anyimusu oder lafiyayyun kalolin abinci,tuwon shinkafa miyan egusi,jollop din shinkafa,sakwara da miyan alayyahu sai snack's da drink's. A babban sashen Galadima suka zauna wanda idan yashigo da kaduna yake zama,matan kuma suka nufi sashen Ummie. Amma tace"Niko lafiya hajiya Zainab gabadaya number ta baishiga?nakirata ban sameta ba nakira number farida tace batanan tayi tafiya. Ummie tace"toh ina Adda Zainab taje ne?tayi tafiya kuma takasa sanar dake Amma? gaskiya da mamaki. "To nima dai shi nagani,ita takanta taci burin zuwan wannan ranar shiyasa nake nemanta fa, Allah ya kyauta bari zuwa anjima nasake gwada kiranta. ****** Hajiya Aliya da hajiya Zainab kuwa basu da wani choice da yawuce amsan bukatan boka,haka hajiya Zainab tanaji tana gani wadannan kattin matan sukayi amfani da ita sannan a gaban boka hatsabibi yana watsa musu wani irin ruwa yana cigaba da surkullen sa. Sai da suka shafe awa daya suna abu guda zuwa can suka kyale ta,boka yace suje zuwa anjima tazo ta amsa saqon magungunanta,su kuma matan suka zauna anan. Banda dariyar keta babu abinda hajiya Aliya keyi ganin yanda aminiyar ta ke tafiya a tattale,sosai hajiya Zainab ta kulu ta dubeta da niyyar tayi magana amma sai ta rigata. "Kada kice komai don tun kafin ayi hakan dake akayi dani fin sau goma,ke nifa idan har akan biyan bukata ne zan iya komai,ke ko boka hatsabibi ne yace yana son kaina zanbashi,ke ko dan mutum yace nakawo zankawo. Takarisa maganar tana taunar chwengum"kas kas kas". Sai yau hajiya Zainab tasake yarda lallai aminiyata hatsabibancin ta ko shedan tsoron ta yakeyi. "Nikam mu amsa maganin nan mutafi don wallahi Alhaji baisan da fitana ba kuma kowane lokaci zai iya dawowa,gashi layina ba za'a iya samu ba. Hajiya Aliya tace"toh mukoma mu gaya masa mukam tafiya zamuyi yanzu. Haka suka sake komawa inda babu abinda ke tashi a dakin sai hayaqi da wani irin wari,sun dauki minti biyar a tsaye kafin boka hatsabibi cikin muryan tsawa yace. "Tsayuwar me kuke musu a hanya alhalin zasu wuce,wallahi duk Wacce aka gurgunta babu ruwa na,duk cikansu jikinsu na rawa suka fada dakin. Zama sukayi a kasa,wani bakin kwarya boka hatsabibi ya dauko tare da yin wasu yare sai ga kullin magani guda biyu sun bayyana,hannu yasa ya dauka inda yadaure face tare da duban hajiya Zainab yace"Kinga wannan hajiya,kije kisamu dai-dai kan inda 'yar uwanki ke kwanciya ki barbada wannan garin maganin,babu wanda zai gane kinsa wani abu,ni kuma ina tabbatar miki da muddin anyi aikin yanda ya kamata to fa 'yar uwanki zata kamu da mummunan ciwon barin jiki(paralysis)wanda har tabar gidan duniya babu maganin shi. Sai kuma wannan kisamu abincinda kikasan shine abincinda tafiso duk cikin abinci ki barbada mata hhhhhhhhhhh....daga zarar kika barbada mata taci kowa gudunta zai dingayi harta 'yan uwanta da uwanta ke da kowama nata,don zata dinga magana ne bakinta na wani irin aman wari tare da fitar da wasu tsutsotsi. Wani irin dariya hajiya Aliya da hajiya Zainab suka sanya najin dadi. "Idan wadannan basuyi ba to dole sai munyi mummunan aiki akansu. "Ayi boka hatsabibi ka kasheta inaso ta mutu natsani in daga ido naga bilkisou. "Hhhhhhhhh kisa a ranki aikinki ya kammala gashi kutafi yanzunnan. Da sauri suka mike ko gidan da suke sauka basu koma ba don dama bawai sunzo da kayan canji bane,hand bags ne shima suka tura driver hjy Aliya yaje ya dauki musu,nanfa suka fafaro hanyar dawowa lajeria🤪 ______ *NIGERIA*______ Haka wadannan ahalin suka kasance cikin farin ciki inda a washegari Sauban zai koma Malaysia,ummie ma tace zataje maidugri kusa da diyarta ta kwana biyu ta dawo. Tunda babu daman ita ta zauna kodan school dinta,inda Amma itama atake anan tace zata bisu taje sosai sukaji dadi babu bata lokaci Abba da Daddy suka fita nema musu jirgi Wanda zaije borno kona 5:00 pm ne. Cikin yardan Allah kuwa suka samu jirgin inda nan suka tafi suka bar su mommy da Abba da kewarsu,maimoon ma sai rigima suke kan sai sun bi Ummie. Washegari tun 7:00 am Kareem yadauki Sauban don kaishi airport,jirgin 7:30 zaibi hakan yasa basu wani jima da isaba aka fara neman matafiya aiko nan Sauban yatafi suna ma juna waving hannu shida Kareem. Anan ma wani sabon kwarkwaryan walima aka hada don su Mashahuda sunyi farin ciki haka su nihal saboda babu wanda besan 'yar tsaman dake tsakanin Ummie da Zuhra ba. Duk da tasan yatafi Amma sai ta nemi walwalarta tarasa tunda taji labarin shine mutumin da yayi aikin haqo asirin da aka mata itada Ummien ta sai taji wani kiman sa da darajar sa a zuciyar ta,musamman da taji irin kasada da hadarirrikan dake cikin aikin tare da wahalar da yasha sai mutumcin sa ya ninku a idon ta,duk da tasan bawai yinsa take ba hasalima ba birgeta yake yaba yasata jan tsaki akasar ranta ta furta " _to meye abin damuwa da tafiyar nasa?kekam wawuya ce._" Yinin ranar kwanan farin ciki wadannan ahalin keyi,don saura kiris Zuhra tayi lattin School ko wanka batayi ba ta sulale tatafi gashi suna da test. *MALAYSIA* Yauma kamar kullum sanye yake cikin suit gray sosai yayi kyau duk da fuskar sa babu alamun fari'a ko kadan amma hakan 'yan matan company din nan keta binshi da mayataccen kallo,dan tsaki yayi kasa² tare da sake tamke fuskar a hankali ya isa office dinsa. Nan aka fara shigowa yimasa barka da zuwa maza da mata. Aiki yakeda shi sosai akan wani designer shoe da yafito wanda sam bema bayyana ba shine take su hada don ko babu komai a fara gani a company nasu shysa take so busy yaudin kam,don duk wanda yazo nemanshi ma baya ma samunsa saboda ya gayama secretary dinsa cewa duk wanda yazo tace yana aiki. Bashi yabar office ba sai kusa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87