Chapter 62
Chapter 62
Bayan komawar su kaitsaye gidan Adda Zainab suka isa sannan duk 'yan sanda ne a bakin gate din gidan,cikin gidan,kofan parloun da cikin palour,dama or ready family din Alhaji iliyasu sun hadu,su Ummie kawai ake jira,aiko nan police din ya dubi Adda Zainab"Hajiya ke muke sauraro,nan Adda Zainab ta cigaba da bada labarin sannan tace"babban sake dinkewar alaqar mu da Hajiya Aliya shine sanadin bilkisou,kowa kallon Ummie yayi nan ta cigaba tana duban Ummie"tunda na mallake hankalina nafara jin tsanar bilkisou a dalilin komai da tafini yasa nakejin tsanan ta,tsanan ta besake nunkuwa ba sai da tasamu miji daga ahalin da suka fi nawa sannan nasake jin wata iriyar tsanar ta,alhalin mahaifiyar ta bata ta6a nuna cewa ba itace ta haifeni ba,hasalima ta fifitani akan bilkisou,daya ke bilkisou ta rigani aure a lokacin hankalina yatashi wanda har Amma taso a fasa bikin Bilkisou abari nima na samu miji ko kuma Sadeeq ya aure ni ya hakura da bilkisou, Allah yajikan baban mu shine ya hana hakan a lokacin naji matsanancin haushin sa,ana haka ne na hadu da Hajiya Aliya inda ta hadani da wani boka da yake nijar,salati aka Sanya gabadaya palourn, Ummie kuwa kuka kawai takeyi. Ta cigaba da cewa"Nice nasa akayi miki farraqu da Zuhra nayi amfani da kyallen jininki na kaiwa boka akayi asiri,tun daga lokacin kika tsane Zuhra,nan fa Adda Zainab tadinga bada labarin irin abinda suka dinga kullawa da hajiya Aliya har asirin da tasake yi mata da wancan ya karye,har zuwa sanda hajiya Aliya ta aure Alhaji iliyasu,da irin rigimar da sukeyi sannan tayi shiru tana jan shasshekan kuka, Ummie ma kuka takeyi tare dasu Amma,cikin kuka Amma tace"Zainab dama kece duk kike musu wannan farraqun?mahaifinku ya mutu da fushin bilkisou akan haka, fisabilillah kin kyauta kenan?cikin tu ajjabi hajiya kareema tace"lallai Zainab shedancin ki yakai inda yakai,yo wanda yayi wannan aikin ai kisa bazai mishi wahala ba,domn tuni aka cire miki imaninki"Adda Zainab cikin dasasshiyar muryan ta tana kuka tace"wallahi bani ce na kashe su Alhaji ba, wallahi"Ammar cikin muryan kuka yace"idan bake bace wanene Mom?please wanene?yayi maganar cikin muryan tsawa,islaha da kuka yaci karfin ta tace"why?why Mom?kinja mana abin fade Mom innalillahi wa Inna ilaihirraji'un ya Allah,babu 6ata lokaci aka sanya ma Adda zainab ankwa a hannunta wata mace,kuka sosai takeyi haka yaranta dasu Amma, Ummie ta dubi police din tace"Please yalla6ai yanzu ina zaku kaita?dan sandan yace"hajiya kaitsaye daganan state CID zamu wuce da ita domin gudanar da bincike yanda ya kamata,munyi muku alqawari muddin babu saka hannunta zamu saketa,idan dasa hannunta kuma zamu turata court a yanke mata hukunci"yana gama fadar haka aka tisa keyan Adda Zainab akayi waje da ita,kowa kaganshi bashi da kwanciyar hankali. ******** Yau a bedroom dinta ta kwana domin kuwa tayi alqawari bata sake kwana daki daya da Sauban,hakanne ma yasa tun kafin yadawo ta koma dayan palour kasa tare da shigewa daya daga cikin bedroom din ta kwana,hakan kuwa sosai ya sosa ma Sauban rai tare da yanke hukuncin yau da la'asar zaibi flight,ta online yasai ticket da komai nasa ya gama batare da tasani ba,da safe tana tashi ta shirya musu lafiyayyen breakfast,babu abinda ke tashi sai na room freshener da turaren rushi,gefe guda kuma ga kamshin girki,tasan Sauban ma'abocin son macaroni ne,dalilin hakan yasa tahada masa lafiyayyen macaronin sa da yaji dakakken nama yayi kyau da dadi,sannan ta dama masa kunun gyada, Ammi ma ta aiko da breakfast din kosai da custard sai wainan kwai,shiryawa tayi cikin riga straight gown,wanda ya fito mata da cikakken surar ta ko ina yacika Masha Allah, tayi kyau sosai,abinka da atamfa me dan duhu sai tayi kyau kwarai,daurin Aisha buhari ta murza mai kyau,kafarta sanye da high heel shoe brown, fitowan ta kenan daga kitchen hannunta dauke da plates taji alamun tafiyan sa,turaren sa me kamshi Arabian Oud ya buge hancin ta,dan lumshe ido tayi tanajin faduwar gaba,daurewa tayi ta cigaba da shirya dinning din. Karisowa yayi yaja kujera ya zauna,sanye yake da wata yadi me kyau tare da maiko brown colour,daka ganta kasan lallai anyi fitan nera wajen siyan ta,kansa murzazziyan kube ce,wacce kudinta zasukai dubu 35 face dinsa babu wani walwala kamar koda yaushe, Zuhra kuwa gabanta ne ya cigaba da faduwa,a hankali tayi karfin halin furta"Ina kwana Yaya"kura mata ido yayi babu ko kiftawa,almost 5 minutes sannan ya girgiza kai kawai,ajiyan zuciya Zuhra ta sauke kirjinta na cigaba da bugawa daurewa tayi tace"Yaya meza'a zuba maka?hannunsa dauke da wayar sa yana latsawa batare da yadago ba yace"meda menene akwai?Zuhra tace"akwai jallop din macaroni with kunun gyada nama nd custard wih kosai,sai wainan kwai.Dagowa Sauban yayi yana zuba idanuwan sa akan warmers din dake kan dinning din,duk da a rufe suke yace"kisamun macaroni nd kunun gyada kadan inci tukuna"yanada tabbacin itace tayi wannan, cikin nutsuwan ta take serving dinta,gabadaya ya tsareta da idanuwan sa jinta kawai take a takure, shikuwa Sauban baiki yaji Zuhra akan cinyar sa ba, wani irin shaukin son ta kawai yakeji,batare da ya ankare ba yaji maganar ta"bismillah Yaya"dan sake hade face yayi yana daukan spoon din tare da duban plate din,lumshe ido yayi yanajin wani sanyi da dadi a ransa don dakakken mama yaji a cikin macaronin Masha Allah,hadiye miyau yayi, bismillah yayi yafara cin abincin cikin mutsuwa,jiyayi wani dadi ya ratsa masa har kwakwalwan kansa,sosai yake daurewa gudun kada yayi santi,ganin ta zauna tatasa kosai da yaji tanaci yasa ya dubeta"bazaki kiyayi kanki da cin yaji haka ba?wallahi idan kikazo kina min complain din basir da ulcer ko?sai kawai yayi shiru ya cigaba da cin abincin, Zuhra kuwa dagowa tayi cikin marairaice face,tare da wata shagwa6a66iyan murya wanda ita kanta bata ta6a sanin tana da ita ba tace"kai Yaya kosai fa idan babu yaji babu dadi"wani tsam!yaji a dalilin yanda tayi maganar,batare da yayi magana ba yadaga mata kai kawai,atake anan ya cinye plate din,gyaran murya yayi mata, dagowa tayi ta kallesa,da ido yayi mata alamun akara,kara mishi tayi ba da yawa ba,itako kosan biyar taci ta basshi cuz takasa sakin jiki taci yana wajen,shiko ko a jikinsa sakin jiki yayi yaci abincin sa yayi katt,yana gamawa yadau kunun gyadan sa yafara sipping,lumshe ido yayi domin har ga Allah yaji dadin kudun sosai,be yadda yabiye ma dadin ba yadaka,don a haka ma jin cikinsa yake ya cika don dama shi ba ma'abocin cin abinci bane,tissue yadauka yafara goge bakin sa,ji sukayi anwani daka kofan palour. Da sauri suka mike, Akeela ce tashigo jikinta sanye da wata doguwar riga fitted sai dai ko kadan batayi mata kyau,sai taunar chwengum takeyi tana kare ma palour kallo,ganin canja wasu abubuwa da akayi tare da kara gyara sa,ta6e mouth tayi tana jan tsaki,nan tashiga takowa a gaban Sauban ta tsaya idanuwan ta cike tafff da hawaye tafara magana"Kaine na mijin dana fara so a rayuwa ta wanda akansa nasan menene so,amma munafukai sunyi nasarar rabani dakai a lokacin da muka kasance tare,inaso kasani wallahi bazan ta6a rabuwa dakai ba koda kuwa zanyi yawo tsirara ne sai na farauto soyayyar ka,sai nadawo cikin gidan nan matsayin mata"takarisa maganar hawayen na zubowa,duban ta ta maida ga Zuhra tana nuna ta,ke kuma inaso na Miki wata zazzafan gargani duk sanda kikasan mijina a matsayin miji wallahi babu ke babu kwanciyar hankali,banza kawai jak.....ai bata karisa
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87