Chapter 60
Chapter 60
na Zina ya shany....a fusace Akeela tayi kan Zuhra tana cewa"nice kike gayama magana haka?da sauri Zuhra taja baya,aiko wani irin fusgota Akeela tayi tana shirin cacumar ta,jikake tassss! Sauban ne ya sauke wa Akeela lafiyayyun mari har biyu banda huci babu abinda yakeyi gabadaya kamsnnin sa sun rikide,dafe kumatu Akeela tayi tana sakin ihu"Ni ka mara akan wata banziya?nidin matark......daka mata tsawa yayi wanda duk wanda ke wajen sai da ya firgita"point of correction Akeela,you re not my wife,nadatse igiyoyin aure na akanki,sannan koda wasa kada ki kuskura kazantaccen hannunki ya ta6a jikin matata"Guggo Laure ne takariso tare da dauke Sauban da mari"kauu! Magana tafara"baka isa ba Sauban kayi kadan kaci zarafin jinina ina kallo dan iska kawai la'ananne. Cikin tsananin 6acin rai Baba Hasheem yace"Haba Guggo haba wannan cin zarafin naki yayi yawa,bazaiga la'anta ba,bazaiga la'anta ba Guggo"yayi magana cikin karaji,cigabawa yayi"me Mika miki haka da zafi?kin lalata zumunci,a dalilin ki mahaifin mu nacan kwance da barin jiki, Guggo mungaji da cin zarafin ki"yayi maganar cikin karaji,hannu ya hada waje guda yace"Don Allah Guggo kitafi,muddin ba alkhairi yake kawoki garemu ba so please nd please kidena zuwa kina tayar ma da ahalin mu hankali na rokeki"Guggo Laure kuwa sakin baki tayi tana kallon Baba Hasheem"Hasheem nikake fadawa magana son ranka?ka mance matsayin wa nake a wajenka?kafin yabata answer Aunty Maryam tayi carab cikin muryan kuka tace"Matsayi wani irin matsayi Guggo?kin mance keda kanki kin yanke alaqar dake tsakanin ki da ahalin nan?duk irin soyayyar da Galadima ke miki Amma haka kika rufe ido akan jika kika tozarta sa,duk akan wannan?tayi maganar tana nuna Akeela"meye ribar ahalinmu idan munma Akeela sharri alhalin mudin duk abu daya ne,wallahi Guggo indai shedaniyar yarinyar nan ne watarana sai kinji kunya. Shiru Guggo Laure tayi da alama jikinta ya danyi sanyi ganin haka yasa Akeela fashewa da kuka"Guggo kinajin su?kina jin irin cin zarafin da suke min?maida dubanta tayi ga Akeela"ke Kuma sai kinsan kin aurar wa kanki masifa da bala'i"tana kare fadar hakan tajuya,da sauri Guggo Laure ta take mata baya tana cewa"Allah ya mana sakayya! _Hoho Galadima family ko rikici family,nikam zanso naga randa wannan rikicin zai tsaya haka,gadai Sauban da Akeela ga kuma Kuma Zuhra a gefe guda,sannan ga alwashin da Akeela ta dauka akan zuhra._ Xahratty CE🥰 Lallai Alqalami 🖊️ yafi takobi🗡️. [7/12, 00:54] 𝐗𝐚𝐡𝐫𝐚 𝐗𝐚𝐡𝐫𝐚𝐭𝐭𝐲🥰: Follow this link to join my WhatsApp group: https://chat.whatsapp.com/Cz6pFHyd9N68OmqNx3Vpqs 👨🏽🦳 *_GALADIMA FAMILY_* 👨🏽🦳 Page: 71/72 ____Sosai Zuhra ke wani irin kuka me tsuma zuciya,gabadaya sun sake 6ata gidan,bayan sallar magrib aka fito da Zuhra Cikin shigan alfarma na lutfaya Army Green tayi kyau matuka,ita kanta lutfayan daka kalleta kasan nera tayi kuka,kuka takeyi sosai kaitsaye apartment din Bodejo aka nufa da ita inda gabadaya a halin ke a palour a zaune,zaunar da ita akan carpet Mommy tayi kusa da Sauban din,nan Baba Hashim yayi gyaran murya tare da sallama,bayan yayi addu'o'i sannan yace ma Taufeeq yakira su Daddy ta laptop din,aiko lokaci daya sai ga Daddy da Abba sun bayyana. Anan aka shiga gaishesu,tare da tambayan su jikin Galadima,hadasu da Bodejo akayi suka gaishe ta,bayan sun gama gaishe²n ne kuma Daddy yayi gyaran murya,nan yashiga nasiha,sosai yama Zuhra nasiha me shiga jiki wanda dole yasata cigaba da kuka Saboda tunatar da ita da yasake kan hakkokin miji akan matanshi da abinda idan tayi zata samu zunubi,sosai yayi mata raga-raga da nasiha daga karshe ya damkawa Sauban amanarta,sannan yace idan ya zalunce ta Allah ya isa,shima Abba nan yayi nasa inda shima daga karshe ya damka amanar Zuhra ga Sauban,na karshe Baba hasheem ne yayi nasa,me hade da fada² don ya lura Zuhra zuma ce sai da wuta a cewar sa,su Daddy nan akayi sallama dasu,cikin tsokana Ummie ta dubi Baba hasheem tace"wallahi da ka hada da duka ina tunanin Zuhra zatafi gane yaren,duk dariya aka Sanya,shima mikewa yayi tare dasu Sauban don zuwa suyi sallah yana cewa"kuyi ku gama mata nasihar da zakuyi mata,don muna dawowa masallaci za'a bashi matansa ya wuce da ita,da to mommy dasu Aunty Maryam suka amsa, Bodejo tace"munafuka munanan daku sanda zasu hade suna kwasar soyayyan su babu meji"dariya palourn akasa, Aunty labeeba tace"yanda kikajin nan Bodejo,nan Ammi tafara mata nasiha,sannan Mommy, Mom, Aunty Maryam, Aunty labeeba,duban Ummie Ammi tayi tace"bilkisou bakice komai ba,dan tamke face Ummie tayi tace"Allah yasa albarka,idan har kika bijerewa umarnin mijinki akan abinda be sabawa mahaliccin ka ban yafe miki ba"tana kaiwa nan tamike ta fice,duk sake da baki suka bita, Zuhra kuwa kuka tasaki. A hankali aka dinga raguwa a palourn,yarage daga Laila sai Nihal,cikin zolaya Laila tace"Oh mu ko dan siyan bakin nan baza'a bari muyi ba?cab wannan auren manya ne"Nihal tace"Allah yasa Yaya ya jiki,haka suka zauna su Laila na taya ta hira a gefe Bodejo na mata tsiyan kuka gulma takeyi,sai wuraren 10 sannan Sauban ya shiga palour da sallama hannunsa dauke da leda wanda aka RUBUTA Delicious Suya,sannu da zuwa suka fara masa yana amsawa sannan suka mike suka fice,kusa da Bodejo yaje ya zauna yana ajiye mata ledan a gefen ta,murmushi Bodejo tayi tana jawo ledan"me kuma kakawo min ne Saudan?tayi maganar tana bude ledan,cike da farin ciki tace"uhmmm aiko ka kyauta kamar kuwa kasan nagaji da cin wannan farfesun gwanda daka siyomin suyan nan,amma dai na rago ne ba sa ba ko? Sauban dake danne-danne a wayansa yace"Ea na rago ne nasan baki cin na sa ai,keda Amma na siya muku"murmushi Bodejo tayi cikin jin dadi tace"amma kuwa mungode Allah yayi ma auren ku albarka"tayi maganar tana kai suyan bakinta tare da lumshe ido tace"kai naji dadin naman nan sosai,ai ina gaya muku kuda kanku sai kunyi alfahari da auren nan"tana tauna namar tana magana,a kaikaice Zuhra ke zabga mata harara don ta gama ramfo Bodejo santin naman takeyi,mikewa Sauban yayi tare da zura hannayen sa a aljihu,wani mugun faduwar gaba Zuhra taji, shikenan wai dagaske akeyi bin ya Sauban zatayi yau?sai hawaye sharrrr,duban Bodejo yayi"mu zamu wuce sai da safe kici nama lafiya"cikin sauri Bodejo tace"ai ban ba matarka naman ba, Zuhra ungo zo ki amsa"ko kallon ta Zuhra batayi ba tana bin bayan Sauban cikin wani irin kuka, Bodejo tace"Oho dai algunguma anaso ana kaiwa marke(Wai market🤣) suna fita ya wani irin fisgota gabadaya tafada jikinsa,face din babu walwala ko kadan yace"Wallahi idan bakiyi min shiru ba sai na baki mamaki,uban waye yace miki nima inason ki da kike damun mutane da kuka?nima ban son ki kakaba min ke akayi"sake fashewa da kuka Zuhra tayi tana toshe bakinta don tabbas taji zafin kalman nasa(su Zuhra Ashe ba dadi,shida kike cemasa bakison sa fa?yafiki jin radadi fa.) Wucewa yayi haka tabisa har suka fice daga gidan nan securities din suka rufe ko ina,gidan sa ya shiga,gate man din shima yarufe ko ina,kaitsaye apartment dinsa ya nufa,cikin sanyin jiki Zuhra ke binsa,wani mahaukacin kamshi ne ya buge hancin ta, tabbas apartment din ya Sauban aljannan duniya ne don apartment din ya hadu,tamkar don ita akayi shi,gani tayi ya nufi stairs ya haye,samun kujera 1 sitter tayi arakube ta zauna tana lumshe ido a dalilin wani irin sarawa da taji kanta na mata,a haka ta cigaba da zama batare da ta ankare ba bacci yayi awon gaba da ita. Sakkowan shi kenan sanye da pyjamas masu matukar
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87