Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 5

Chapter 5

Galadima Family Book 1 Complete Hausa Novel 1,281 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

sallar harma wasu masallatan sun tayar. Babu bata lokaci itama tazo tafara gabatar da sallan ta. Bayan sallar isha'i Sauban yasamu su Daddy a farfajiyar gidan don a ka'ida nan suke dawowa su cigaba da hira abinsu cike da qaunar juna,sallama yayi cike da mutumci irin na hadadden yaron tare da kamewa yaduqa yafara gaishesu. Suma cike da jin dadi suke amsawa saboda natsuwar Sauban da Kuma kamewarsa,wanda wannan dalilin ne yasa yakeda jama'a da dama a cikin family din nasu. Abba ya dubeshi yace"Sauban ya akayi ne?dan murmushi yayi tare da sake sunkuyar dakai yace"Abba dama sako ne dazu aka turomin daga can maleyshia kan suna son muje za'ayi mana interview mu goma Sha shida 'yan Nigeria,nanda 4days shine nace bari nazo nasanar daku. Ko wannensu cike da farin ciki Daddy yace"Masha Allah! Abbiel kuwa murna sosai kwance akan fuskar sa yace"Sadauki Masha Allah, congrats my son! na tayaka murna sosai,yayi maganar yana masa musabaha. Inda sabo Sauban yasaba da halin Abbie don tun yana yaro yake tare dashi,murna sosai sukayi. Daddy yace"ka fadama su Ammin naka? "A'ah Abba yanzu nakeso nashiga wajenta na fada mata sannan na fadama mom itama. Sake mishi fatan alkhairi sukayi,miqewa yayi cike da qasaita duk da cewa hakan halittarsa ce domin Sauban tsayayyen namiji ne a cike wanda dai² da maza ma 'yan uwansa yana musu kwarjini balle kuma mata. "Yanzu Sauban kasar maleyshia zakaje yin aikin?Koda Allah yasa hakan shine yafi zama alkhairi nidai abinda nakeso dakai kada ka kawomin wata 'yar qasan kacemin aurenta zakayi don magana ta gaskiya ba lamunce maka zanyi ba,don ga 'yan uwanka nan cike da dangi. Dan guntun murmushi yayi yace"sweetheart ko aikin ma ba'a samu ba kinfara kawo korafi? Ammi ta sake tsuke fuska tace"ai gaskiya ce na fada saboda nasanku ku maza shiyasa tun yanzu ma nake gaggawan taka maka birki kada naji ko nagani Koda kuwa andace ne. "Shikenan sweetheart hakama sam bazai faru ba gobe nakeso naje gidan Aunty falmata. Ammi tace"Allah yakaimu!da ameen Sauban ya amsa nan suka cigaba da hirarsu. Washegari da safe wajejen goma saura sai ga Guggo Laure itada Akeela,tsayawa nayi naqare mata kallo tasss,kyakkyawa ce sai dai ko kusa bata kamo kafar yaran gidan ba duk da cewa a ciki akwai qalilan da tafi kyau,sanye take da lutfaya baki mai ratsin jan flowers sai kafanta sanye da halfcover ja,hannunta riqe da handbag shima ja fara ce tass wanda a farin ma akedan karawa da man bleaching daga gani zatayi sa'a dasu mashahuda. Baba mansir mahaifin Akeela shine Guggo Laure tasa ya kawo su don baisamu shigowa gidan bane saboda ana jiransa ujila. Kaitsaye bangaren su bodejo suka nufa, Akeela kuwa tamkar bazata take kasa ba,Koda suka shiga sun cidda bodejo da Galadima,bodejo tana hada masa brabusko da miyar kuka Wanda yaji nama zallan tsoka daga bangaren Daddy aka kawo. "Assalamu alaikum!ga bakin sassafe fa. Guggo Laure tana fada fuskanta dauke da tsananin fari'ah saboda ganin motocin yaran gidan da alamu ma basu fitaba hakan ne yasata sake fari'arta. Galadima yace"Laure!kece a gidan?lallai jiki yayi sauqi sosai tunda gashi kin iya fitowa yayi maganar fuskansa kadaran kadahan. A inda Akeela take tsaye ta gaishesu ko rissinawa babu qiqam ta gaidasu. Cike da mamaki su bodejo ke duban ta, Galadima yace"ke haka akace miki mata na gaida mijinta?duqawa akeyi har qasa bawai atsaya a tsaye kerere ba kinji? Akeela ta wayance ta hanyar cewa"toh ai saboda bana auren tsoho irinka yasa na gaisheka a haka saboda kada tsohuwar matanka ta huramin hanci. Bodejo kuwa Sarai ta ganeta sai cewa tayi"to ai tunda kikama wannan angon haka babu irin angon da bazakiyi wa ba. Guggo Laure tace"musake gaisawa kundawo lafiya?ya gajiya Yaya bodejo? Bodejo tace"ai gajiya tabi jiki Laure Kuma marasa lafiya kun fito balle kumamu? Guggo Laure tace"wallahi fah kedai Bari jiya najuya yafi sau nawa? narasa gabadaya abinda kemun dadi a gidan duniya naqosa gari ya waye nazo saboda nace da zafi zafi ake bugun karfe shiyasa,tadubi Galadima tace"kada dai agaji dani akan kokari na nason aikata alkhairi. "Maganace dai akan yaran nan Akeela da Sauban shiyasa ma nace Akeelar tashirya tazo muje ayi komai a gabanta. "Shima kuma Sauban din ayi komai a gabansa. Cike da mamaki duk suke duban ta. Galadima kuwa abin duniya ne ma ya isheshi yayi dan murmushi irin nasu na manya yace"Laure kenan kekam akwaiki da wutan ciki, gashi yaran ba dukansu ne suke nan ba don shi sadeeq yau ya koma kaduna,shikuma Hasheem yaje ta'aziyyar amininshi da yarasu. Guggo Laure tace"toh nidai Yaya hakanan za'ayi hakuri ayi maganar nan yau a wuce wajen. "Yarinyar nan tana tsananin son Sauban,duk cikin jikoki na babu mafi soyuwa agareni kamar Akeela. Galadima yace"toh shikenan bari nakira taleeb din,hannunsa yakai gefen lumtsememen leaderseat dinda yake zauna yadakko wayarsa kirar sumsung yafara nemo number,baiwani dau lokaci ba yakira har takatse ba'a daga ba,ko kafin yasake danna kiran,Kira yashigo wayan nasa. Dauka yayi tare da sallama,daga can bangaren Daddy yagaishe shi,amsawa yayi kaitsaye yace"inason ganinku kai da Aliyu idan anyi sallar azahar,daga can bangaren aka amsa da toh insha Allah,sannan Galadima yakatse wayan. Guggo Laure kuwa murna takeyi kamar yakasheta,dakin da take sauka wanda aka mata nan tanufa harzata shiga sai Kuma tajuyo tace"ke Akeela zo muje mugaisa da matan gidan tukuna koh? Akeela kuwa farin ciki takeyi kamar anmata kyautan hajji,aranta kuwa fadi take itace zata mallaki Sauban jinin GALADIMA FAMILY?tabbas tayi sa'a,don Sauban namiji ne wanda da dama mata ke bibiyan sa,don ko a yanar gizo maganar sa mata keyi namiji ne mai tsadan gaske. Kai tsaye apartment and Ammi Guggo Laure tashiga,sallama tayi itama Akeela tayi cike da kissa. Su mashahuda ne a farlon,hada idon da muneefa zatayi aiko tamike da gudu tanufi Akeela tace"Kai lallai ma Akeela yau kece a gidannan haka? Akeela ta watsa idanuwa tace"aiko gani ai muneefa bakida kirki ko Guggo bakizuwa gaishewa. Mashahuda ta dubi Guggo cike da mutumtawa ta gaisheta,inda kallo daya tama Akeela ta watsar don sam ita Akeela bata burgers barin yanda take ganin tanasa pic dinta a Instagram na shirme. Muneefa tace"Tabb yaushe zaki ganmu so kike ya Sauban ya babballamu?dariya sukayi. Kujera Guggo Laure tazauna, Akeela da muneefa kuwa daki suka shige inda mashahuda tashiga kitchen don kiran Ammi,Ammi bata zama duk da masu aiki suke aiki Amma girkin mijinta ita takeyi tunda yanada suger,masu aiki kuma suyi na gida gabadaya ko da ita bata dauki wata mai aiki tayiwa mijinta girki ba. Mashahuda bajima ba tafito kitchen hannunta dauke da tray inda ruwa kekai da lemo. Ammi ce tafito fuskanta dauke da murmushi tace"Guggo ce a gidan? Guggo ta amsa fuskar ta dai kadaran kadahan tace"yauwa sannu Aisha nice. Ammi tace"inayini Guggo,kunzo lafiya? Guggo Laure tace"lafiya lou,munsameku lafiya? Ammi tace"lafiya ALHAMDULILLAH ya karfin jiki?jiya zamuzo da Rabi sai mazan sukaci mubari suje mu mazo yau Ashe jikin ma yayi sauqi? Guggo tace"jiki Alhamdulillah sai dai tasowar na dole nayi saboda mahimmiyar maganar dake tafe dani. Ammi tace"Allah sarki sannu da zuwa. "Yawwa Aisha,inasu Yaya na muhammadu? Murmushi Ammi tayi tace"Sauban yana dakinsa anata shirye²n tafiya Malaysia. Guggo cike dason jin Karin bayani tace"mekuma zaije yi can? Mumushi ammi tayi tace"zaije interview ne idan da rabon yasamu aiki a wani company a can ne

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});