Chapter 66
Chapter 66
toshe ma Mom din Akeela mouth"maimuna!maimuna!!please kada kitara mana jama'a don Allah"jin wannan maganar da Mom din Akeela tayi yasata dawowa hankalin ta, Guggo Laure ta matso tana"meke faruwa ne ake kada a tar......shiru tayi takasa karisawa a dalilin tozali da tayi da Akeela da Suby haihuwan uwar su day ubansu, gefe guda kuma al'auran maza ne irin na roban nan daure a kwankwason Akeela"innalillahi wa Inna ilaihirraji'un innahu min sulaimanu wa innahu bismillahir rahmanir rahim,nashiga uku ni Laure na lalace,Ashe dama da gaske ne?kuka wiwi Alhaji Mansir,mom Akeela,da Guggo Laure keyi, Guggo Laure ta cigaba"wallahi Akeela kin cuce mu, yanzu da wani ido zan kalle Yaya Muhammadu da 'yayansa?dama sunce mune da jin kunya ashe da gaske ne"takarisa maganar tana wani irin kuka,da wani irin mugun fusata Alhaji mansir yadauko wayan radio aiko ya rufe ido yana dukansu kota ko Ina,ihu Suby da Akeela keyi suna rokonsa,amma ina dukan su yakeyi bayaji baya gani sai da ya musu jina-jina sannan ya rabu dasu don ko motsin arziki basu iyayi sai numfarfashi,sannan yadubi Suby yace kafin ya kirga ashirin ta tashi tabar masa gida,ko ya fice da ita tsirara,jin haka yasa Suby a hanzarce saka kayanta tadau long hijjab dinta tasa tafice tana kuka,baki ya kumbura yayi suntum! Komawa dakin Alhaji mansir yayi ya cigaba da dukan Akeela,gabadaya Baba Sani yakasa kwatanta, Guggo Laure kuwa fadi take"ai Akeela da haihuwar ki gwara asarar cikin ki,maimuna ta haifa mana kamiyamiya ta haifa mana annoba, cikin kuka Mom Akeela tace"kiji tsoron Allah Guggo,ki tuna akwai mutuwa akwai hisabi,duk abinda Akeela ta zama kinada kamasho,don duk cikin jikokin ki babu wacce kika sangarta kamar Akeela,kece bakiso a kwa6a mata,kika nuna duk abinda zatayi dai-dai ne,idan kin manta niban manta shekaru 24 baya Akeela ta zubar min da mangyada daga na dungure ta kika dinga fada har sai da takai ga Alhaji ya sakeni saki daya,ko kin mance ni?wallahi kece silar lalacewan Akeela"kuka Guggo Laure tasa takasa furta komai,domin duk abinda maimuna ta fada gaskiya ne. Sai da yaga tadena numfashi ya rabu da ita,don sai da ya zubar mata da hakora biyu na gaban bakinta,kuka wiwi kamar yaro haka yakeyi,duk cikan su suna zaune jigum-jigum,wani yaro ne yayi sallama,bayan sun amsa ne yake cewa wai mutane na sallama da Alhaji mansir a waje,gabansa ne yafadi aka shiga kallon², Baba Sani yace"mutane kamar yaya? yaron yace"su Malam sahabi ne dasu Malam Gaddafi"Baba Sani yace"tohm kace yana zuwa,su uku suka fita har da mujaheed,nan suka tadda dandazon matasa su shidda sai manya uku,hannu suka mika suna musabaha,su kuwa matansa sai wani ciccin magani sukeyi, Baba Sani yace"Malam sahabi lafiya kuwa?wanda akakira da Malam sahabi yace"Gaskiya ba lafiya ba kuka ganmu haka,wani video ne mummunan video,babu kyan gani yau muka wayi gari yanata trending a social Media,videon Akeela na wajen ku,videos kusan uku anwatsa a duniya tana aikata madigo,tsirara,zindikiya,haihuwar uwarta da ubanta? innalillahi wa Inna ilaihirraji'un,shine matasa sukazo suna cewa su bazasu yarda ba kada ta lalata musu yaran anguwa. Shiru duk su Baba Sani sukayi saboda sun shiga wani hali na kunya da tozarci,a dalilin yanda hankulan mutane yafara dawowa kansu, baba Sani yace"malam sahabi don Allah kuyahakuri anjima idan anyi bincike sai a tabbatar da komai"aiko nan matasan nan suka botsare inda kowa yadinga bada labarin irin shedancin da Akeela keyi,dakyar aka samu komai ya lafa sai dai magana fa ta tabbata Akeela 'yar madigo ce,kuka sosai Alhaji mansir yakeyi, duban Akeela yayi cikin muryan kuka"Allah ya isa tsakanina dake Allah, Allah sai yamin sakayya a irin tozarcin da kikamin,Baba Sani cikin 6acin rai yace"wai me kake fada ne haka mansir?idan fa hankali ya gushe hankali ke nemosa,wani Allah ya isa zaka mata? addu'ah shine mafita amma ba baki ba,cikin kuka Mom Akeela tace"kadai fada masa Yaya Kuna kallo a gidan nan,shida Guggo ne masu 6ata Akeela sai kuma da talalace ne yake kokarin mata baki?takarisa cikin fusata,shima Alhaji mansir yace"wallahi kika sake magana maimuna sai na mugun sa6a miki"cikin kunan zuciya Mom Akeela tace"duk abinda kamin abakin auren ka,don dama ni aka cuta don Akeela kadai na mallaka"tana kare fadar hakan ta wuce tana kuka,sukam sunga tashin hankali. ***** Cike da gajiya suke tunda suka dawo Zuhra ta kwanta bata farka ba sai yanzu don dama tanajin zazza6in sai dai bekai na jiya ba, toilet ta shiga ta watsa ruwa sannan ta sauko daga stairs din, kitchen tashiga saboda wata irin yunwa da take kwakular ta,dambun naman da Ummie ta musu ta zubo sai yoghurt da tadauko a fridge, bomshort ce a jikinta da vest,kasan carpet ta zauna sannan tafara shan magungunan ta,door bell taji yafara ring hakan yasa ta mike,budewa tayi aiko cikin farin ciki da harka tace"Aunty Rammat kece?sannu da zuwa shigo,itama Rammat murmushi takeyi zama tayi a dayan palour ba na baki ba, Rammat tace"nashiga ne shine naji ance baki da lafiya shiyasa nace bari na dubaki"cikin jin dadi Zuhra tace"Gaskiya naji dadi bari na kawo miki lemu da snacks wallahi banyi girki bane"Rammat tace"eyyah kada kidamu a koshe nake ma da kinbarshi"Zuhra bata saurare ta tawuce cikin kitchen,a tray ta hado mata komai tajawo stool ta ajiye tray din akai. "Aunty Rammat biki nata gabatowa sai jiya naga anko a wajen Mom,gaskiya lace din yayi kyau,atamfar kanuri day da za'ayi itama tayi kyau ga biki saura 3 week's"Rammat tace"Aikuwa dama ba wani events za'ayi ba banda wannan,shima don na matsane"Zuhra tace"ayya Allah ya nuna mana"Ameen Rammat ta amsa dashi sannan suka cigaba da hirarsu abinsu,sai wajen 2:00 Rammat ta tafi,shiru Zuhra tayi tana mamakin inda ya Sauban yaje haka bedawo ba,mikewa tayi tahau saman sa ta fara gyara masa duk da ba wani datti ba,juyawan da zatayi taci karo da wani dan book me kyau da tsaruwa,hannu takai ta dauka tana budewa cike da sha'awa,zaro idanuwa tayi a dalilin abinda taci karo dashi,pic dinta tagani ranar tana sanye da wata Dubai gown a kasa anyi rubutu kamar haka _My heartbeat_,cike da mamaki ta bude wani page din,cikin sauri ta samu waje ta zauna don ganin wani pic din nata akasa shima anyi rubutu kamar haka _Itadin duniya tace kuma rayuwa ta ina tsananin son ta tun randa Allah yakawo ta duniya har zuwa wannan lokacin,ina kaunar ta da dukkan rayuwata,cuz itadin numfashi na ne,duk wata mace dazan mallaka a bayan ta take,bata kaita ba kuma bazata ta6a kaita ba domin itadin ta musamman ce....i love you my Surur Qalbeey🥰_,ga date shima tun 12/4/2018. Zuhra zaro ido tayi a fili tace"shekaru masu yawa haka?cigaba tayi da budewa tana ganin abubuwa masu tsananin al'ajabi da mamaki wanda lokaci daya taji wani irin mugun tausayin yayan nata don har bayani yake akan yanda yakasa tunkarar ta da maganar soyayya shi kuma bazai zuba ido ta aure wani bashi ba,cigaba da karantawa tayi har zuwa randa aka kirasu ana sanar da ita an daura mata aure dashi,wani hawayen tausayin sa ne ya kamata a fili tace"Allah sarki Yaya dama duk abinda yakemin ba kiyayya bane tsantsar kishi ne?sorry yaya na,duban frame din gefe wanda pic dinsa ke jiki tayi,sanye yake da kayan cricket da sandar a kasar Malaysia ne yayi masifan kyau,shafa photon tayi tana juyawa da niyyar cigaba da aikinsa. Gabanta ne yayi wani mugun yankewa ya fadi a dalilin Ido hudun
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87