Chapter 7
Chapter 7
dago suna duban Guggo Laure,dayake Galadima Sarai yasan halinta. Mikewa tayi a zafafe tacema Akeela" ki mike mutafi. Fuuuu kuwa suka kama hanya suka fita. " _Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un! Allahumma ajirni fi musibati wa'aklifni khairan minha_. Kalmar da Daddy yafada kenan tare da duban Sauban. "Yanzu Galadima ya za'ayi a shawo kan wannan matsalar? matsala cefa wacce idan ba'a ma tufkar hanci ba to zai iya taba zumuncinmu da Guggo Laure. Jinjina kai Galadima yayi"Hasheem narasa ma mezamuyi,daga bodejo har Lauren kaf sun dauki zafi yakamata ace daya a cikinsu ya sauko,duban Sauban Galadima yayi yace"muhammadu Kaine sanadin wannan rikicin don haka kai zaka gyara. Sauban ya sauke wani nannauyan ajiyar zuciya don shi mutum ne mara son hayaniya yace"Galadima bana son ta Allah ma yasani kuma. "Keep quite Sauban! Daddy yafada cikin bacin rai. Bakaga abinda ke faruwa bane?meye yashiga kanka?kasan kuwa wacece Guggo Laure?kakuma son me ake nufi da zumunci?hmmm katashi kabamu waje,don mune muka haifeka bakai ne ka haife muba,kaje duk hukuncin da muka yanke zakaji. Mikewa Sauban yayi tare da rissinawa yace"Allah yahuci zuciyarku nabarku lafiya,yana gama fadar haka yajuya cike da mazantaka da salon tafiyarsa mai burge duk Wanda ke kallo yafita. Baba Hasheem yace"gaskiya Yaya kada kashiga haqqin Sauban. "Don Allah Hasheem kadena wannan maganar bana fatan abinda zai bata sunan GALADIMA FAMILY,kakira su Sadeeq a waya akwai meeting ranar Friday insha Allah,mukuma kafin lokacin mungama magana da bodejo don shawo kanta. Gabadaya jinjina kai sukayi, Galadima kuwa sosai yaji dadi don matansa da kanwar tasa sun gwara mishi kai. *KADUNA JABI ROAD* Gabadayansu zaune suke akan dinning din suna dinner cike da farin ciki zuhra tace"Abbie nayi missing dinka sosai. Murmushi Abbie yayi yace"nima nayi missing dinki mama na ya gida ya shirye²n jamb kuma? Zuhra tace"alhamdulillah munanan munayi. "Toh alhamdulillah agama cin abinci sai muje parlona inji wani jami'a kika cike a slip din jamb din. Dariya sosai zuhra tayi tace"toh shikenan Abbie. Ummie kuwa tsaban takaici jitayi tamkar tayi Aman wuta 😡 saboda bacin rai. ( _Ko na menene oho._ ) Basu jimaba suka kammala,duk suka hallara a parlon Abbie, Taufeeq, Laila, Aseef, Nihal, ZUHRA. "Abbie nafiso nayi Dan fodio don haka shinasa. Murmushi Abbie yayi irin nasu na manya yace"meyasa bakisa ABU Zaria ba ko Kuma KASU mamana? Dan Jim zuhra tayi sai Kuma tace"Abbie banason ABU nikam,kuma abinda yasa banason KASU afa kaduna nayi nursery, primary, secondary, shiyasa nakeson nacanza gari Amma nafison Danfodio Abbie. "Bakiga duka 'yan uwanki ba suna ABU?ga kuma yayanku Aseef,inaganin zakisamu kulawa sosai sannan zakiji dadi. Dan rau rau zuhra tayi da ido dama ita abin kuka baya mata kadan muryan ta na dan rawa tace"please Abbie nikam banason ABU don Allah. Laila tace"Abbie wallahi kada abari tayi Danfodio tazo ABU zataji dadi fa,takarisa maganar tana dariya kasa² Cikin barkwanci ya Taufeeq yace"wallahi Abbie yarinyar nan tana mana bakin cikin dan jellof rice dinda zata dinga mana ne. Gabadaya dariya aka Sanya,nihal tace"da dan sululu Koh Yaya?aka Kuma sa dariya. Ya Aseef yace"Abbie aiba sai abinda takeso za'a biba dole umarnin iyaye zatabi ko 'yar jarida. A kaikace zuhra ta dalla masa harara. Fira sukayi sosai da Abbie kafin kuma kowa yawatse yaje kwanciya bacci. *OLD MAIDUGRI* "Aunty wai don Allah dagaske kikeyi?inafa son sa wallahi bazanyi fatan Sauban ya kubucemun ba,idan nashigo zura'ar GALADIMA FAMILY wallahi cele zan sake zama a wajen kawaye na da abokaina. Wacce tayi maganar bazata gaza 27 yrs ba. Mom tace"Rammat kenan nafiki son shigo cikin wannan family din don arziqi yaci uban nada kinsan kuwa waye Sauban?hmmm awajen dangin Aisha kawai idan kikaga gatan da Sauban ke samu sai kin gigice, Rammat da arziqi agidan wasu gwara a gidanku a gidanku ma a dakinku,hmmm wai Akeela. Wani tsanar Akeela Rammat taji har cikin ranta saboda tsananin son da takewa Sauban. "Aunty nidai gaskiya asanar ma da Mama halin da ake ciki don ni babu dalilin da zaisa nayi zaman kishi da Akeela ( _Sauban kaga takanka,tun yanzu anfara maganar zaman kishi a dalilinka._ ) Mom tace"Ea zanje bari ko zuwa anjima idan su Yaya (Daddy) sun fita sallar la'asar sai mufita don kinsan dokar gidan nan namu. "Gaskiya kuwa Aunty don da zafi² ake bugun karfe. A gidan Guggo Laure kuwa banda kuka babu p abinda Akeela takeyi gabadaya ta tadarma jama'ar gidan da hankali, Guggo Laure kuwa sai girgiza kafa takeyi. Xahratty CE (ÕÙM ÃJMÃL )🥰 Lallai Alqalami🖊️yafi takobi🗡️ 15/2/2023 [3/21, 22:27] Xahratty (OUM AJMAL): 👨🏽🦳 *_GALADIMA FAMILY_*👨🏽🦳 Story&Written By *FATEEMA ZAHRA LAWAL* Marubuciyar⤵️ A DALILIN'YAR TSINTUWA. MIJIN ZAHRA. DIAMOND LADIES ( Daukar fansa)paid book. RUHIN AMRITA (FATALWA CE). Now *_GALADIMA FAMILY_* Page 06 _Bismillahir-rahmanir-raheem._ *NAGA SAKO NAGODE SOSAI MY SOFY ALLAH YASAKA DA ALKHAIRI UBANGIJI YAKARA RUFA ASIRI DUNIYA DA LAHIRA😊ALLAH YAKARA GIRMA ACEMA OGA SAUBAN MUNA GODIYA TARE DA AJMAL🙏🏽🙏🏽🙏🏽* https://www.facebook.com/profile.php?id=100074816894956 Guggo Laure tace"Haba Akeela meyasa kikeso tayarmin da hankali ne?nace miki indai ina raye Sauban mijinki insha Allah idan Kinga baki aure Sauban ba ki tabbaci hakikan bana numfashi ne. "Wai Guggo meke faruwa ne?tundazu kunshigo gabadaya Akeela tahana kowa sukuni a cikin gidannan,har yanzu bazata dena tabara ba kamar wata karamar yarinya?shekara ashirin da biyar Amma ace har yanzu mutum bai girma ba wallahi waje tasamu. Harara Guggo Laure ta aika mata dashi tare da watsa yatsu tace"Maimuna kinsan Allah kikiyaye ni kifita idona,to ina ruwan wani kokuwa nina nemi wani yazo?inbanda munafunci da tsugudidi meyakawo ku? Guggo Laure tayi maganar tare da watsama mama hajiya zainab harara matan baba sani,ganin hakan yasa sumi² tajuya tabar wajen. "Guggo kada fa kimanta tun Akeela na qarama mujaheed kesonta wallahi idan akayi haka ba'a ma Yaya sani da Aunty zainab karaba. "Maimuna kinsan Allah zan batamiki a gidan nan,ina ruwanki?ko kinfini son Akeela da mujaheed ne?duk son da mujaheed kema Akeela tunda ita batason shi aiduk zance ne. Banga dalilin da zaisa ayi abinda za'a zo ana danasani ba,kinga kiwuce kiban waje. Cike da bacin rai mahaifiyar Akeela ta wuce flat dinta tare da matsananciyar bacin rai. Da daddare kuwa Guggo Laure tasa aka kiramata Alhaji Sani da Alhaji Mansir nan tazauna taratsa su tare da shirya musu karya wai Galadima ya nemeta akan yanaso a hada Akeela da Sauban aure. Sosai sukayi murna duk da cewa sunsan maganar mujaheed da Akeela, Alhaji Mansir yace"Amma hajiya kinmanta da maganar mujaheed da Akeela ne? Cikin sauri Alhaji Sani ya katseshi. "Haba Mansir meyasa kake hakane?neman alfarma fa wan mahaifiyar mu yayi kan yanaso a hada jikinsa da jikanta aure,ba Kuma don komai ba sai don karfafa zumuncinsu to mezesa ayi haka? Guggo Laure tace"Hmm rabu dashi Sani kaji,nan dai ta sallamesu. Akwana a tashi babu wuya inda Allah yakawo mu yau Friday,gabadaya family din Galadima suna MAIDUGRI idan kacire matan Adda Labeeba da Adda Maryam. Abbie yazo tare da kaf iyalensa,haka kuma Mommy ma sunzo dama da Abbie da Abba ne suke zaune a kd. Zaune suke a parlon Galadima gabadayansu,bodejo, Daddy,Abbie, Abba,Baba Hasheem. "Alhaji kunason shiga hakkin saudan da yawa,yanzu fa lokaci ne na kowani dan Adam nada 'yancin kansa Amma tunda kun rijayene shikenan Allah yasa hakan shiyafi zama alheri Amma sam ba'a yimana adalci ba,tayi maganar tana sake tsuke fuska. Duk cikansu sauke nannauyan ajiyar zuciya sukayi,domin da bodejo bata amince
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87