Chapter 16
Chapter 16
don Mom ita inda dayanda za'ayi kashe mata Sauban kawai za'ayi. _________**________ Yauma kamar kullum tashinta kenan dai² karfe hudu a dalilin wani mummunan mafarki da tayi wai anyi rasuwa ga mutane nan cike a Galadima fam sai dai bataga gawar ba sosai hankalinta yayi kololuwan tashi,koda tamike bathroom tashige tadauro alwala tafito tare da shimfida praymat tatada sallah. Koda ta idar lokacin anfara kiraye-kirayen sallar farko,sosai tayi addu'ah. Tadauki tsawon mintuna tana lazimi zuwa can aka tayar da sallar asuba don haka sai itama tamike tatada sallar. Acan gidan Guggo Laure kuwa Akeela ce ta tasata agaba wai ranar da akasanya yayi tsayi da yawa ai 'yan kauye ne kecika ranar aure ita gaskiya a rage. Guggo Laure kuwa sai lallashinta takeyi takuma tabbatar mata da cewa suna zaune ma Sauban din da kanshi zaizo yana neman alfarmar a rage. Dan yatsine face Akeela tayi cike da rashin jin dadi a ranta tace"Ni Guggo ina tsananin kishin sa ne wani irin zazzafan so nake masa,wallahi nida da yanda zanyi kan kada yaso ko wacce mace zanyi saboda ina tsananin kishin sa. Dariya Guggo Laure tayi"mekike ci nabaka nazuba 'yannan?kisa a ranki zai soki kedai kidage da kissa da kisisina sannan ki tabbatar da kin jawosa a jiki ya zamana babu macen da yake gani a matsayin mace saike. Dariya Akeela tayi tace"yanda kikajin nan Guggo kuwa sai dai nayi tsananin yarda dasu Suby su kansu zasu tayani shawo kansa. Mere baki Guggo Laure tayi"Hmmm kesam bakisan sharrin kawaye ba koh?ina gargadinki Akeela amma sam bakiji. "Wallahi Guggo basu da matsala don kawai bakisan su bane domin duk suna tsananin sona wallahi. Murmushi Guggo Laure tayi tace"Yaro yaro ne to shikenan Allah ya kyauta. Xahratty CE🥰 Lallai Alqalami 🖊️ yafi takobi🗡️ 25/2/23. [3/21, 22:27] Xahratty (OUM AJMAL): 👨🏽🦳 *_GALADIMA FAMILY_*👨🏽🦳 Story&Written By *FATEEMA ZAHRA LAWAL* Marubuciyar⤵️ A DALILIN'YAR TSINTUWA. MIJIN ZAHRA. DIAMOND LADIES ( Daukar fansa)paid book. RUHIN AMRITA (FATALWA CE). Now *_GALADIMA FAMILY_* Page 13/14 _Bismillahir-rahmanir-raheem._ ______Ummie abin duniya duk yataru ya mata yawa taje wajan Amma don bata hakuri amma gabadaya taki saurarenta tasake jaddada mata cewa muddin bataja'yarta a jiki ba to tamance itama tana da uwa a raye. Kiran number Aunty Zainab tafada mata duk yacce sukai da Amma,itama fir tarufe Ido tama Ummie sol. Tsakanin Ummie da hajiya Zainab tazarar shekara daya da rabi ne. Haka dai Ummie tadawo gida jikinta sam babu kwari tarasa wanda zataje wajensa suyi magana taji dadi ita ba kawaye ba,a yanzu duk wanda zataje wajensa neman shawara kara mata takaici zasuyi,banda huci babu abinda takeyi a fili tafurta"Natsaneki Zuhra tabbas bacin nice dakaina na haifeki zan iya tsine miki saboda kina daf da rabani daduk wasu masoya na,na haifawa kaina masifa na haifawa kaina jaraba? Sosai hankalin ya Taufeeq yatashi don yana gaf da shigowa parlon yaji zan tuttukan da Ummie keyi, idanuwansa sun kada sunyi jajazur juyawa yayi yafasa shigowa parlon,kaitsaye bq dinsa yanufa a daddafe, Aseef sai masa magana yake amma Ina baiji ba. Da harara Aseef yabishi a fili yafurta"Idiot"cikin murya kasa kasa. ****** Zuhra ce cikin shagwaba da sangarta take latso wasu hawaye mere dan mitsitsin mouth lip dinta tayi tana muttsike Ido cikin muryan son kuka tace"Toh yanzu Abbie idan kuntafi yaushe zaka dawo?ni wallahi bangaji da ganinka ba fah. Dan dariya Abbie yayi tare da shafa kanta yace"zamu dawo azumi mana kinmanta azumin saura 1month?so insha Allah I think sai lokacin zamu sake zuwa. Daddy ne suka kariso shida Abba da Baba Hasheem, Daddy ya dubi zuhra yace"A'ah mamana kema yau zaki koma ne bamu da labari? Dan sinnar da kai zuhra tayi cikin girmamawa tana wasa da yatsunta tace"A'ah Daddy narako su Abba ne da zasu tafi. Dan murmushi sukayi gabadaya Abba yace"hmmm kya fadi gaskiya,Yaya kuka take nema tamaka koh?yakarasa zancen cikin zolaya. Dan rissinawa tayi tadauki ledan dake gefenta tamika ma Abbie tace"Abbie gashi abaiwa Ummie na da mommy,akwai sweet da chocolate na maimoon da Ateek. Abbie ya amsa yace"toh shikenan Allah yamiki albarka. Da Ameen ta amsa tare da matsawa saboda gabadaya sun nufi mota daya motar Daddy kenan da ita zasu fita, Baba Hasheem ne ke driving gefensa kuma Abba ne,sai baya Daddy da Abbie cike daso da kaunar junansu suka fita,zuhra natsaye har Baba mudi yabude musu gate suka fice,hawaye ne ya zubu mata da sauri tasa hannu ta goge,saboda shigowar Aunty muneefa datagani da wasu 'yanmata biyu. Abangaren Abbie shima runtse idanuwa yayi yabude tare da sauke ajiyar zuciya yana mejin tsananin tausayin diyarsa duk Daddy na lure dashi shima girgiza kai kawai yayi,kaitsaye motar airport tanufa. Zuhra murmushi a face dinta tatare Aunty muneefa. "Aunty muneefa barka dama kece?muneefa na murmushi tace"Eah zuhra kwana biyu bananan ina school shiyasa. Haka kawai Zuhra taji sam wacce suke tare da muneefa batayi mata ba don haka ko kallonta batayi ba,a gefen ma haka ne don lokaci daya taji tsanar zuhra ta dirar mata,sake shaqa tayi a dalilin ko inkular da zuhran tanuna mata,yarinya qarama da sanabe,tafadi hakan a ranta. "Dawowata kenan yanzu nabiya gidan Guggo Laure shiyasa ko hutawa banyi ba,murmushi zuhra tayi. "Eyya Aunty nima apartment dinku zanshiga don ko jiya danazo gaida Mom batanan. Muneefa tace"ok muje koh? Dayar ce tayatsine face"Muneefa bari naje nafara miqa gaisuwa ta ga Ammi kafin nadawo. "Kai Allah don Allah kizo muje mu warware gajiya dududu yaushe muka shigo?dayarl budurwar tafAdal Zuhra kuwa ko sauraren su batayi ba tanufi sashen Mom,a kaikace budurwar ta dalla mata harara. Muneefa tace"Don Allah rabu da ita Suby kinsan Akeela da rawar kai. Zuhra kuwa koda tashiga sashen Mom tagaisheta sosai Mom din taji dadi don Allah yadora mata son zuhra tun sanda Ummie ta haifeta sannan takema Aseef sha'awar auren ta. Tana gafda shiga apartment din Ammi Akeela tafito, Zuhra dauke kai tayi kamar bata ganta ba itako Akeela wani banzan kallo ta watsa mata. Koda zuhra tashiga kai tsaye ta nufi kitchen don tasan Ammi tana can,ilaikuwa sunata aiki itada Aunty Mashahuda da maid dinta Amina. Murmushi kwance a face din Ammi ta tarbe Zuhra,dan rissinawa tayi ta gaishe da Ammi. Dan turo mouth tayi alamun shagwaba tare da karyar da wuya tace"kai Aunty shine ko ki aiko nazo nataya aikin?nasan Daddy akema abin shan ruwa. Hararar wasa tawatsa mata sannan tace"Aiba sai nace kizo ayiba keda kanki zakizo"takarisa maganar tana dan murmushi. "Ammi wallahi namanta Daddy yana azumi saboda naje raka Abbie ne shiyasa duk na shagala. Kallon ta Ammi tayi fari'a kwance a saman fuskarta tace"Don Allah kirabu da wannan Auntyn taki,aikinma da sauki don mesa ana masa girke girken bashi nan. Dan dariya kadan zuhra tayi batare da tayi magana ba tafara yanka cabej din dake kan mable din. Mashahuda tace"Hmm ai Yaya akwai shi da iyasa aiki ni wallahi tausayi matar sa kebani. Sallaman su muneefa ne yasasu juyawa gabadaya,kallo daya zuhra tamusu tadauke kai saboda ganin yarinyar nan tadazu. Da murmushi Akeela tamatso kusa da Mashahuda tace"sis kawo in tayaki goge carrot din,dan yatsine face kadan Mashahuda tayi tare da dan sakin yaqe tace"No kada kidamu munkusa gamawa ma ai tunda ga zuhra na gyara cabej. Akeela badon taso ba haka tahakura,ita kuwa Suby gabadaya hankalin ta yakoma kan zuhra faffadan kugunta kawai take kallo( _acewarta_).
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87