Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 63

Chapter 63

Galadima Family Book 1 Complete Hausa Novel 1,307 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ba taji saukar gigitaccen mari Sauban ya shimfida mata a fuska,sannan yana huci ya nufi wajen extension wear ya ciro cabel din caja,ai Akeela na ganin haka ta nufi kofan palour tana fita da gudu,aiko binta Sauban yayi cikin zafin nama, Zuhra kuwa da taga ma tsorata da kalaman Akeela binsa tayi jikinta na wani irin rawa.Wallahi babu macen da ta isa ta haifa maka yara saini,ke kuma kijira kiga abinda zai sameki"tana kare fadan haka tafice kamar wata zararriya, Zuhra kuwa kuka ta fashe dashi tana juyawa don ta tsorata da kalaman Akeela gani takeyi tabbas kamar wani zai farun,babu zato taji Sauban ya mata wani irin runguma,ai a haukace ta fisge jikinta tanaja baya,tsayawa kawai yayi yana kallon ta,jiyayi ta saki kuka tana hade hannayen ta waje guda,kuka yasa ta gaza furta komai,nufota Sauban yayi da mugun sauri ta kuma jan baya,tsayawa yayi kawai yana kallonta"Naroke ka da Allah yaya ka sakeni,ni bazan iya auren nan ba inajin tsoro please kasakeni nac..... batare da taji sanda yakariso ba kawai saukan mari taji a kuncin ta me azaban zugi,wani ihu tasa tana dafe kumatun tare da duban sa,jikinsa ne ke wani irin shaking,idanuwan nan nashi sunyi jajawur bakinsa na rawa"Du....dduk..duk ranar da kika sake cewa na saki wallahi sai nayi miki dukan mutuwa"yana kare fadar hakan yajuya yana maida kwallan dake kokarin zubo masa,tabbas a yanzu ya tabbatar da yarinyar nan bata son sa, kaitsaye palour yafice jikinsa na cigaba da rawa,ita kuwa Zuhra inda yabarta nan ta zube tana sake fashewa da wani irin kuka( _Nikaina Zuhra kinfara bani haushi akan kalmar sakin nan da kike fada,da mene zaiji?_ ). Tana bedroom tana sallah taji shigowan sa yahaye upstairs,har taji sanda yake sakkowa da alaman ana jan trolley bag,cikin sauri ta mike tafito,shi tagani sanye da kananun kaya, security dinsa na daukan akwatin yana fita,kafadun shi dauke da wani jakan, Zuhra lokaci guda zuciyar ta tatsinke taji kuka kawai yataho mata,a hankali ya tako har inda take,face dinsa kadaran kadahan,hannunta ya kamo duka biyun tare da sumbatan goshinta"Zan tafi insha Allah zandawo nan bada jimawa ba,Zaki koma wajen Ammi before nadawo,ina miki fatan alheri"yana kare fadar hakan yajuya yafice,sai a lokacin makalallen hawayen da Zuhra ke makalewa suka samu damar sirnano mata,tana me zama kan sofa din sharaf,tana fashewa da kuka. Shiko Sauban a tunanin sa Zuhra zata biyo sa a baya amma sai yaga akasin haka,girgiza kai yayi yana sake yarda da lallai Zuhra bata son shi,mota yashiga driver yaja,dama ya masu Ammi sallama kaitsaye sai airport, Zuhra kuwa tasha kukan ta ta koshi sannan ta mike tashiga tayi wanka sosai ta kwanta atake wahalallen bacci yayi awon gaba da ita,sai wajejen biyar ta farka tasake wanka ta shirya cikin turkey gown me yankakken hannu,tadau hijjab tasanya,abubuwan bukatan ta tadauka,dama ba komai aka kawo mata ba na kayanta,fita tayi ta kashe kowane socket nd switch na sashen har saman shi sai da tahau ta kashe komai sannan ta rufe ko ina tafito tanufi Galadima house. Cikin sanyi tashiga sashen Bodejo tafara nufa,suka gaisa nan Bodejo tafara mata tsiya tana cewa ta canza lokaci daya saboda mijinta yayi tafiya sam babu walwala tattare da ita, Zuhra kuwa da baki be iya shiru tace"Cab Allah ya kyauta,ni wannan har nayi irin wannan shakuwan dashi ne? Allah yatsare a gayas,dariya Bodejo tayi tace"hmmm yaro yaro ne koma me zakice ba yarda zanyi ba. Nan suka ta6a hira ta mike ta nufi sashen Mom,tagaishe ta aiko nan ta cidda Rammat ai zama sukayi suka sha hirarar su sosai,duk da Rammat sa'an su Aunty Mashahuda ce amma akwai saukin kai gashi nasu ya hadu da Zuhra,ba ita tashiga wajen Ammi ba sai after magrib,aiko nan Ammi tafara nan-nan da ita,duk kulawar da take bata ada sai yakaru, Ammi kuwa sai taga kamar Zuhra na cikin damuwa ne na tafiyan mijinta yasa tace"ki kwantar da hankalin ki Zuhra, yayan ki baze dade ba zaidawo kuma idan zaidawo dake zai koma gaskiya"Zuhra tace"a'ah Ammi nifa ba komai,kawai dama Akeela ne..sai kuma tayi shiru,kallon ta Ammi tayi tace"dama Akeela mene?me Akeelan tayi miki? Zuhra tayi raurau,hawaye na silalowa,nan taba Ammi labarin abinda yafaru dazu da safe,sannan cikin muryan kuka ta cigaba"ni Ammi inajin tsoron abinda zatayi mun ne,tace"idan nasan shi,duk da ban fahimci me kalmar take nufi ba,kuma ninasan shi,ba Yaya na bane? Ammi ta sauke ajiyar zuciya don ta fahimci tabbas Zuhra bata gane me hausar idan kika sanshi yake nufi ba hakan yasa taji natsuwa tace"ki kwantar da hankalinki,kinfa je islamiya Akeela ke saukakkiya ce,kinsan bawa baya wuce kaddarar sa, Akeela bata isa ta miki abinda Allah be miki ba,kisa hakan a ranki, sannan kuskure ne Wanda kema kinsa ni nacewa miji ya sakeki,kinsan zunubin hakan,sannan kinsan wani irin so Sauban ke miki? Zuhra tace"Ammi wallahi Yaya beso na kawai ya aure ni ne. Xahratty CEπŸ₯° Lallai Alqalami πŸ–ŠοΈ yafi takobiπŸ—‘οΈ. [7/15, 10:35] π—πšπ‘π«πš π—πšπ‘π«πšπ­π­π²πŸ₯°: πŸ‘¨πŸ½β€πŸ¦³ *_GALADIMA FAMILY_* πŸ‘¨πŸ½β€πŸ¦³ https://chat.whatsapp.com/Cz6pFHyd9N68OmqNx3Vpqs Page:75/76 ____Ammi murmushi kawai tayi tana jinjina ma yarintar Zuhra,haka Zuhra ta cigaba da zaman ta a apartment din Ammi tama mance da wani Sauban sai idan taji suna waya da Ammi take tunawa dashi,sannan tasake yarda da baya sonta tunda ko kiran ta yakasa yi yaji ya yabarta,sosai taji zafin hakan,da yake sun dan samu hutun sati biyu na school hakan yasa taji tanason zuwa wajen Ummie. GALADIMA kuwa jiki Alhamdulillah don sosai aka fara ganin sauyi don har mikewa yakeyi da kansa cikin yardan Allah kuma yana dan maganar sa,lokacin da yaji Zuhra ta tare da Sauban ba karamin farin ciki yayi ba shiyasa koda Sauban din yazo nasiha yadinga masa kan ya kula da Zuhra ya riketa amana,sannan dui abinda zai gani ya mata uzuri harda yarinta. Shi kanshi Sauban din yaji dadin ganin Galadima don jiki kam Masha Allah tunda maganar ba sosai yake fita kamar da ba,sai dai ana sa ran nanda 3 days za'a sallame su gabadaya, Bodejo ita kanta tayi farin cikin hakan don da sukayi video call da Galadima har kukan farin ciki tayi mara misaltuwa. ***** Bangaren su Adda Zainab bincike sosai akeyi,inda taki amsa lefin kisan,tadai ce taje sashen marigayi Alhaji iliyasu saboda tunda suka dawo kwana biyu be lekota ba sai taje taduba ko lafiya shine tana shiga ta cidda gawansu don har kumburi sun fara,ganin da sukayi kamar Adda Zainab tafara musu yawo da hankali ne yasa aka fara wahalar da ita,don har farcen ta sai da aka cire mata,wuyan da taji ne yasa ta amsa lefin don cewa itace ta kashesu,ta barbada musu guba a abinci,dama abinda jami'an suke so kenan hakan yasa suka tattare duk wani takardun ta suka mika court inda gobe itama za'a wuce da ita,sai dai mummunan abinda yafaru da Adda Zainab shine a daren tayi mafarkin wasu irin halittu sunzo suna amfani da ita ta bayan ta,sai sai farkawar da zatayi ta farka da hauka tuburan,don tsirara tayi ma kanta haihuwar uwarta,wasu tsutsotsi suna fito mata ta bayan ta,hauka sosai Adda Zainab keyi tana sanar da abubuwan da suka dinga aikatawa da nemanta ta baya da matan nan da sukayi,nanfa hankalin jami'an yayi kololuwan tashi,a a dai-dai lokacin Kuma Ammar da Taufeeq sunzo state CID din a dalilin hujjan da suka samo na ba Adda

Table of Contents

Chapters

87 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});