Chapter 77
Chapter 77
ajikinsa tamatsa gefe kanta asunkuye saboda kunya. Shima k'asa yayi da kai yana Susa k'eya. Sunbama ammi dariya amma saita gimtse. Fuskarta d'auke da murmushi ta ce, "Rahma kintashi?. Kan Rahma akasa ta ce, " eh ammi natashi tund'azu. Kodai mukarramne yatadaki?, dannasan halinsa sarai. Girgiza kai tayi cikeda kunya tana murmushi. Ammi tayi dariya, to tunda kintashi bara nakawosu ki basu abincinsu tun asuba yara basuci komaiba sai ruwan zam zam da Zuma aketa basu...... fita ammi tayi, bobo ya kalli Rahma baki bud'e, my cute wai kinanufin basuci komaiba yarannan harfa 12 tawuce?. Shagwa6e fuska tayi Nurulk'albi wlhy ina gama wanka na kwanta saboda barci danakeji sosai......... Kafin ya ce, "wani Abu Ammi tashigo d'auke da yaran ahannunta. Bobo ya kar6i macen, saida yasumbaci goshinta sanan yamik'ama Rahma ita. Cikeda kunyar Ammi ta kar6a Dan ita saima yanzu zata gansu tunda sukazo duniya, jitayi k'aunar yaranta tana ratsa dukkan sassan jikinta, Aranta Ta CE, " ALLAH sarki haka iyayenmu sukeji akanmu, ALLAH ka k'aramana k'aunar iyayenmu dakuma taimaka musu iya iyawa Dan bazamu iya biyansuba..... Ganin tayi shiru ammi ta ce, "Rahma bata tasha mana. Ajiyar zuciya Rahma tasauke, idanunta Akan k'yak'yk'yawar jaririyar daketa bud'e baki alamar tana Neman abinci, ga idanu kyar masha ALLAH, (Yaran yanzu haka ake haihuwarsu da wayensu, saidai fatan ALLAH yatsare manasu damu kanmmu). Tana saka mata abaki yarinyar tafara sha, da sauri tacire tana fad'in wash da zafi. Daga bobo har Ammi dariya suka saka mata, Ammi ta ce, "haka zaki daure kibasu, daga baya zaki daina jin zafin. Tasowa bobo yayi yadawo Kusada Rahma, ita kunyama yabata ga Ammi a zaune kan kujerar madubi, bobo ya ce, " kinga kidaure mana, kokin manta wahalar jiya tafi wannan. K'asa-k'asa yay maganar yanda ammi bazatajiba, ita tunima tad'auke kanta daga Kansu tana kallon baby boy d'inne Wanda take kallo amatsayin tarihi ya maimaita kansa, Dan tamkar bobo yana jariri haka take kallon yaron. Rahma takuma sakama yarinyar, tana kamawa tacire tana yarfe hannu dafad'in shiiiii wlhy da zafifa. Tabama bobo dariya amma awannan karon saiya dake, dakansa yasakama yarinyar akaro na uku, Rahma tarik'e hannunsa ga zafi ga kunyar Ammi data lilli6eta, kallon Ammi tayi sannan takalli bobo tamkar zatayi kuka, ammifa na kallonka Dan ALLAH kasaki zan bata da kaina. Ammi shima ya kalla yana murmushi, to aii bamu Ammin takema kalloba, hankalinta nakan angonta sabo fil. Dole Rahma tahak'ura har babyn tad'ansha amma sai matse baki takeyi da yarfe hannu harta sha da yawa. Ammi takatsesu da fad'in to abarta haka shima maigida yasamu yasha. Sosai kunya ta lilli6e Rahma, Ashe Ammi na kallonsu amma ta sharesu. Ammi tamik'ama bobo Namijin, itakuma takar6i macen, akafad'a tasakata tana shafa bayanta danson tayi gyatsa. Shikuma bobo yad'ora ma Rahma beby boy acinyarta, yanzuma haka yasaka masa shima abaki da kansa, Rahma nakukan zafi-zafi, ana cikin haka saisukaji sallama, ammi dake tsaye ta amsa, Safna tashigo cikin 'Yar fara'a, rissinawa tayi yagaida ammi, ammi ta amsa mata cikeda fara'a da tambayarta mai gidan?. Yana nan lfy Ammi, Ashe ansamu k'aruwa?, ALLAH ya raya. Ameen Safna, yaukam kunyi 'ya'ya gasunan masha ALLAH, ammi tafad'a tana mik'a mata baby gal dake hannunta. K'ar6a Safna tayi cikeda sha'awar babyn. Rahma ta ce, "Anty Safna sannu da zuwa, tana maganar tanad'an yarfa hannunta. Dariya Safna tayi, ke lfyarki kuwa?.. Zafi wlhy, Dan ALLAH kabarshi haka Nurulk'albi wlhy yak'oshi. Bobo yad'ago yanama Safna sannu dazuwa, ya ce, " wannan k'anwar taki akwai ragwantaka. Zama Safna tayi abakin gadon tana dariya, Ammi tafice abinta dama. Bobo yacirema babyn nono abaki yana dungure kan Rahma, raguwa kawai. Eh naji babu komai koma miye kufad'a, anjima kuma saiku nemi abinci awajen jaruma. Dariya bobo yayi ya ce, "koda k'arfin tuwo aii sai anbamu 'yammata. Rahma ta ce, " shikenan k'arfinku yabaku to. Kizuba ido mana zaki gani aii. Safna dai dariya take musu, Dan yanzu Alhmdllh son bobo yaragu sosai azuciyarta saboda k'ok'arin da ya Kamal yakeyi wajen mantar da ita hakan. Tal'ek'a fuskar baby boy dake hannun bobo, masha ALLAH yaran duk kai suka biyo kaida Nawal. Cikeda farinciki ya ce, " ko auntynmu?. Wlhy kuwa, Safna tafad'a tana dariya, ta kalli Rahma dake gefe tana jiyyar kanta, auta next time saiki haifa mana mai kama dake. Idanu Rahma tazaro Anty safna ban fito daga magagin wannanba amma kike zancen wata, yanzu kam saidai ku. Kallonta bobo yayi yana dariya, my Nusfulhayat aikema nanda next year nakeason ki k'ara haifo wasu biyun. Narke fuska tayi tamkar zatayi kuka, Dan ALLAH my Zuma kudainamin fatannan wlhy akwai wahala. Dariya safna da bobo suka saka mata..........adaidai nan kuma khursiyya da khairiyya suka shigo dagudunsu, rungume Rahma sukayi suna murna, suduka suka haye gadon khairiyya tazauna Kusada bobo tana amsar baby, itama khursiyya na hannun Safna ta amsa, sai dad'i sukeji sunata k'ank'ame yaran. Khairiyya ta ce, "yaya, su ya Hamza suna kirankafa. Mik'ewa yayi yana fad'in lah sunzo gidanne?. Eh yanzu suka shigo suma. Fita yayi yabarsu sunata hirarsu da dariya. Safna sai kallon yaran takeyi cikeda sha'awa, dayanzu itace ta haifesu, dayanzu ita bobo yakema wanan tattalin, ya ALLAH kaciremin son bawan ALLAHnnan gaba d'aya, nima namaida hankalina ga mijina kodan tattalina dayakeyi. Duk a zuciyarta takeyin maganar. To nimadai na amsata da Ameen, Dan yanzu tausayi take bani. _bayan kwana uku_ Aka kawo kayan barka, bobo yataka rawar gani, kayan sai sambarka a keyi, Appa da Ammi ma ba'a barsu abayaba suma da nasu, Rahma sai fad'in kayannan sunyi yawa takeyi, jitake k'aunar mijinta da 'yan uwansa nak'ara ratsata. Haka akaci gaba da kar6ar bak'i yan barka har zuwa ranar suna. Yara sunci sunansu, Namijin sunan Appa yaci, wato Aliyu haidar, macen kuma Ni'imatullah. Za'a ringa cemusu Shareeff da Shareefa, to saimuce ALLAH yaraya Aliyu & Ni'imatullah. 'Yan uwan Aunty Ni'ima sunji dad'in wanan karamci daga Rahma, Appa ma sai albarka yake saka mata, hakama sauran dangi. Suna yak'ayatar alhmdllh abin sai Wanda yagani, naga tarin masu karatu awanan suna masha ALLAH. kwalliya kam Ranar Rahma tashata, kamar kasaceta ka gudu, awajen yin hotunama bobo sai yabawa yakeyi, shima yaci wankan shadda sai k'yalli da k'yawun haiba kefita agareshi. K'yaututtuka kam sun samu bila adadin, gadon Ammi damk'am yake da kaya iri-iri. Zuwa dare taro yatashi mutane kowa yakama gabansa, sai su Ammi kawai, da Rahma bobo Nawal hibba, Appa da 'yan aiki, saikuma shareeff da shareefa. Bayan Rahma tafito wanka tashirya kanta cikin kayan barci. Tana zaune ak'asa shayi takesha, yayinda Ammi takeyima Shareeff da shareefa shirin barci, Nawal da heeba suna zaune kan gado sai k'irga kayan jariran da aka samu sukeyi da turame. Da sallama bobo yashigo d'akin shima sanye yake da kayan barci, zama yayi Kusada ammi yana fad'in Ammi shirin barci kukeyine?. Shirin barci mukeyi mukarram, suma sun gaji yakamata su kwanta su huta ko. Gsky ne ammi. Mik'a masa Shareeff tayi tana cigaba da shirya shareefa, umm my sweet dady, yau kunsha hayaniya ko?........ Nawal ta ce, "papa!. Na'am Mamana miya faru?. Kaga kayasu baby's d'inmu dayawa. Nagani kuwa, kunyi goshi, nawa kuka k'irga?. Papa bamu gamaba'ai cewar hibba. To kudage mugani nawa muka samu. To papa. Dubansa yamaida ga Rahma, ohni 'yammata dankina shan shayi saikiyita shama mutane k'amshi?. Murmushi Rahma tayi ta ce,
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83