Chapter 12
Chapter 12
k'auna, ALLAH yabar zuminci, Alkairin ALLAH yakai muku aduk inda kuke."_* Luv u oll⛹🏻♀. 2⃣1⃣&2⃣2⃣ Jiki a sanyaye Rahma tak'arasa cikin falon, tamaida k'ofar ahankali tarufe. Ajiyar zuciya ummi dake zaune a fallo tana jiran dawowar Rahma ta sauke. Dama ita take jira dantaga kowa yashigo amma banda Rahma. "Lah ummi bakiyi barciba?, Rahma tafad'a a sanyaye. Mik'ewa ummi tayi tana murmushi, inani ina barci auta bata dawoba. Murmushi Rahma tayi kanta ak'asa. Ummi ta taso takama hannunta suka nufi d'aki, mutane duk sunyi barci, wasukuma suna gidansu ya Kamal. Rahma tarage kayan jikinta sannan tazauna bakin gadon inda ummi take zaune itama da wasu tarkacen robobi agabanta. Ummi miye wad'annan?, Rahma tafad'a tana d'aukar wata robar Zuma tana kallo. Maganin basirne, kinga k'ar6i wannan takardar kiduba, d'azu malam saddiqu na islamiyyarku yakawo bayan fitarku. Cikin mamaki Rahma takar6a tana bud'ewa, murmushi tayi tareda d'agowa tana kallon ummi da itama kallonta takeyi, ummi wai kinsan miye?. A'a saikin fad'a. Sak'one daga islamiyyarmu, wai gobe idan ALLAH yakaimu sun shiryamin walima k'arfe 9:00am to 12:00pm, dukda abin yazo babu shiri. ALLAH sarki bayin ALLAH, ummi tafad'a cikeda jin dad'i, aiko mun gode musu da wannan karramawa. Aiko dai, Rahma tafad'a. Abubuwa ummi ta rink'a dannama Rahma a darennan, harsaida Rahma ta ce, " ALLAH ummi nak'oshi cikina zai fashe. Dariya ummi tayi ta ce, "to barshi haka saida safe. Daga nan wasu kayan gyaran jiki ummi ta murjema Rahma jiki dasu sannan suka kwanta. *_BOBO._* suna Isa gida yanufi d'akinsa, kayan jikinsa yafara ragewa, yana k'ok'arin zaro wayarsa a aljihu saiyaga ta Rahma, Kansa ya dafe O ALLAH, namanta ban bata wayartaba, zubesu yayi a durowar gefen gadon harda tasa, daganan yacire kayan jikinsa, bayi yashiga, bayan wasu 'yan mintuna yafito, badai wanka yayiba. Shirin barci yayi ya kwanta, saidai barcin yak'i d'aukarsa, fuskar Rahmace take MASA gizo, k'yawawan idanunnan NATA yake hangowa, yasaki wani lallausan murmushi Wanda bansan na miyeba, saikuma yaja siririn tsaki yana gyara kwanciya. Nima waje nayo nabarsa. *_Washe gari_* Tunda sassafe Rahma ta tashi tai wanka kasancewar tana fashin sallah, Basama tafara yarfa mata k'unshi, masha ALLAHU nafad'a Dan k'unshin yana bada ma'ana. Jikin Rahma duk yayi sanyi, ta tabbata yau babu fashi saita bar gidansu, cikin dabara take share hawayenta dankar Basma tagani dansukad'aine a d'akin. Zuwa 8:00am angama k'unshin, yayi k'yau sosai, 8:30am akasa Rahma yayi wanka agurguje dantafiya walimar makarantarsu. Shiri tayi cikin zani da riga na atanfa pink, ta d'ora bak'ar alk'yabba mai shara shara wadda amaren zamani ke yayi, tayi k'yau sosai dukda yau babu kwalliya afuskarta, dak'yarma tayarda Basma tasaka mata pink d'in janbaki Wanda shiga da kwalliyar alk'yabbar. Wajen walimar yayi k'yau sosai, acikin harabar islamiyyar za'ayi, malaman sunyi k'ok'ari gsky dukda abin yazo babu shiri. Wajen da'aka tanada na musamman dan d'alibai su Rahma suka zauna, iyayen yara dayawa sun halarci wajen, su Abba ma duk sunje, su ya kamal ya muneer ya shaheed, da sauran matasan anguwar da iyayensu, dan Rahma mutuniyar kirkice, tsakaninta da kowa a anguwar sai girmamawa, batada hayaniya wannan yasa takasance mai jama'a kowa yana sonta. Gurin yayi tsit ana addu'a, shigowar wasu motoci hud'u yaja hankalin mutane kowa soyake yaga suwaye?. Appa yafara fitowa shida wasu dattijai uku, da alama abokansane, mota ta biyu kuwa matasan family nasune, ta ukuma haka harda ya ishaq da wasu zasukai sa'anninsa, motar k'arshe kuwa, ya Hamza da sulaiman, Lukman da tauheed ne, sai Bobo Wanda yakashe kala cikin manyan kaya, purple d'in shaddace mai haske ajikinsa, rigar iya guywa d'inkin zamani, yayi k'yau sosai harda d'ora bak'ar hula. Wow! Wasu 'yammata dake gefen Rahma suka fad'a, d'aya tace kai Ruma guy d'incan ya had'u wlhy, dama ya ce, "yana sona?. Rahma tad'ago dantaga wanene wai suketa kurantawa haka?, gabantane ya fad'i tayi saurin kauda kanta. Abbane yataso shida abokansa da shuwagabannin makarantar suka tarbi su Appa. Masauki maik'yau aka basu kamar ansan da zuwansu. Bayan gaishe2 akaima bak'i barka da zuwa. Itadai Rahma tunda tamusu kallo d'aya bata sakeba. Dukda da daddare yaganta hakan bai hanashi ganetaba, babu laifi yarinyar tanada k'yau da nutsuwa, bobo yafad'a azuciyarsa. Mayun idanunsa yadasa mata batareda ya saniba. Rahma datakejinta atakure, jikinta yana bata kallonta akeyi, tana d'agowa sukaima juna kallon ido cikin ido, Dan suna fuskantar junane. Da sauri ta janye nata gabanta na fad'uwa, hular alk'yabbar taja takuma rufe fuskarta. Samun kansa yayi da sakin lallausan murmushi, ya sauke ajiyar zuciya yana kauda kai daga kallonta. Addu'a aka fara gabatarwa sannan aka buk'aci Rahma tafito tayi karatu. Gabantane yafad'i, tatuna d'unbin mutanen dake wajen amma acikinsu akeso tafito tayi karatu?....muryar malaminsu taji yana k'ara nanata sunanta. Ihsan ta ta6ata Rahma kitashi mana. Ihsan inajin kunya wlhy. Kinga saka wannan gilas👓 zaki rage jin kunyar. Siririn farin gilas d'in takar6a tasaka, o ALLAH nafad'a danganin k'yawun da gilas d'in ya k'ara mata. Ahankali tamik'e tak'araso har inda ake buk'atar ganinta, malam jamilu yabata abin magana. Tunda tatsaya gaban tebir d'in da aka ajiye alkur'ani mutane ke kallonta, wasukam halittar ALLAH suke yabawa da nutsuwa Rahma. Appa sai dad'i yakeji Dan yarinyar tashiga ransa. Gurin yayi tsit danjin zazzAk'ar muryar Rahma tafara fidda sautin karatun alkur'ani mai girma cikin suratul Maryam. Bobo yalumshe idanunsa danjin muryar Rahma na ratsa ko ina na sassan jikinsa, ALLAH ya albarkaci rayuwarki yafad'a azuciyarsa, ahankali yabud'e idonsa yasauke akan Rahma dake karatu tana hawaye Wanda gilas d'in bai hana agansuba. Masu hotuna sai k'allata suke, wasu kuma da waya suke mata, harda masu vedio d'inta. Saida takai har k'arshen surarar sannan taje ta zauna tana cigaba da share hawayenta Wanda narasa namiye?. Angabatar da nasiha ga amarya da Ango mai ratsa jiki da 6argo, har malam yana tsokanar Rahma da ALLAH yasa wata shekarar su taru haka a sunan baby, dayawan mutanen wajen sunyi dariya dafad'in ameen, (bobo kam murmusawa yayi kawai). Angabatar da k'yaututtuka ga amarya Rahma, Wanda makaranta suka karramata da yaba k'ok'arinta na hazik'ar d'aliba mai ilimi da girmama manya da rashin karya dokar makaranta. Abba sai dad'i yakeji. Cikin abokan Appa dasukazo tare yamik'e shima ya ce, "yayma Rahma k'yautar mota sabuwa dal saboda namijin k'ok'arinta. (Kabbara akayi da tafi). Rahma tamik'e tayi godiya, takuma godema iyayenta da malamanta dasuka taka rawar gani arayuwarta, ta ce, ''iyayena sune gatana dasuka tsaya tsayin saka Dan ganin ingantuwar ilimin mu na addini dana zamani, tana kuka tana godiya ga iyayenta abbanta da umminta da yayyaensu da malamanta,....... Kuka mai k'arfi yaci k'arfinta takasa magana sai shashsheka." Ahankali bobo yamik'e yataka har Inda take, hanky yamik'a mata fari tas daketa tashin kamshin daddad'an turarensa. Jiki a sanyaye takar6a idonta ak'asa ta ce, " ngd tafad'a cikin shashshekar kuka. Abin maganar yakar6a daga hannunta, yafara mik'a godiya ga iyayensu da kuma malamai da 'yan uwa da abokan arzik'i dake wajen taron, yahad'a da sakama Rahma albarka da yaba mata. Kabbara akayi da tafa MASA, abin ya burge mutane gsky, Rahma taji dad'i sosai, dukda tasan ba Sonta yakeba tunda had'asu akayi, amma yay mata wannan karamcin. Abba da yayuntama sunji dad'i abinda bobo yayi. Hakama su Ya Hamza bobo yaburgesu, fatansu ALLAH yasa yad'ore haka har gidan aurensu. 'Yammata kam dayawa sun k'yasa saidai sun 6oye kodan Rahma. Bayan jawabin manyan bak'i da
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83