Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 19

Chapter 19

Abdulmalik Bobo Book 1 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

cikin ido sukaima juna shida ita saikuma suka dawo da kallonsu kan Nawal. Baby ka ajiye jaka ka goya momy kawai. Da sauri Rahma ta ce, " nikam Nawal na yafe. Nawal ta k'ya6e fuska tana fad'in um um nidai sai yayi miki goyon, saikitacewa kin yafe kullum kullum. Kan Rahma ak'asa ta ce, "toki bari yahuta kinga yazu yadawo daga aiki, tajawota jikinta tana lallashi. Bobo yawuce d'akinsa yana murmushin darun Nawal. Bayan yayi wanka yafito sanye da wando iya guywa da Riga k'arama, Rahma tamik'e kanta ak'asa ta ce, " ga abincifa. Baice mata komaiba yanufi dinning, itama baya ta take masa, bayan ya zauna tafara had'a masa komai, sai satar kallonta yake k'asa k'asa, tagama takoma falo taja Nawal suka koma tsakar gidan dansu sha iska. Bayan kamar minti 30 suka dawo, sannan bobo ya kammala yanazaune da jaridar tasa ta fama. Nawal ta ce, "yauwa baby tashi kagoya momyn to. Da sauri Rahma tanufi d'aki dantaga rigimar Nawal bazata k'areba. Bobo yajawo Nawal yad'ora kan cinyarsa, kinga babyna kibari zan goya momynki amma ba yauba, kinga yau nagaji, yak'are maganar da sumbatar kumatunta. Nawal ta k'ya6e fuska ita adole bata yardaba. Ganin zata takura masa, shikuma soyake yahuta saboda yagaji sosai, ya ce, "to tashi muje na goyata, tamik'e yarik'e mata hannu suka nufi d'akin Rahma. Tana zaune bakin gado tana wasa da wani d'an babyn Nawal, suka shigo, ta d'ago kai tana kallonsu, suna had'a ido da bobo ta kauda idonta. Nawal ta ce, " momy tashi baby yamiki goyonki. Rahma tabud'e baki zatayi magana Bobo yad'aga mata hannu, karki damu yarinyar nan taki ba k'yalemu zatayiba inhar ba'ayi goyonnanba, Dan haka taso kawai nayi muhuta. Da sauri Rahma takallesa danjin furicin bakinsa, yama za'ayi harta iya yarda ya goyata saikace wata yarinya. Bata ankaraba taga ya tsugunna yana jiran tahau kenan. Cikin sanyin murya ta ce, "Dan ALLAH kayi hak'uri bazan iyaba. Juyowa yay yana kallonta fuska a d'aure, ya ce, "amma dai kinsan Nawal dashegen naci, indai ba goyonnan nayiba ba barina zatayi na hutaba, nikam natsani adameni da hayaniya. Ganin yanda yake magana cikin fad'a amma hakan baihana muryarsa fita cikin nutsuwa da taushiba yasa dole tasakko daga gadon, amma tayi tsaye takasa hawa saboda tana matuk'ar jin kunyaarsa. Momy kihau baby yana jiranki Nawal tafad'a tana kallonta. Hararar da Bobo ya watso matace tasata saurin d'anewa bayansa. Shikuma yamik'e yanufi falo da ita, Nawal nabiye dasu tana dariya. Yajuyo yana kallon Nawal to nagama ko baby?. Lah baby saikaje d'aki da'ita sau uku kana dawowa, haka yayta zarya daga falo zuwa d'aki harsau uku, ana ukunne yadireta saman doguwar kujera yana fad'in wash bayana, wlhy momyn Nawal kincika nauyi. Rahma tayi k'asa dakai cike da kunya, yabata dariya wlhy, sai wani yatsine fuska yake da rik'e k'ugu tamkar zaiyi kuka, amma saita gimtse, wai yau itace namiji yagoya, da gudu tabar wajen tanufi bedroom. Shikam dariyama tabashi Dan haka yad'an murmusa tareda zama saman kujerar, wani nishad'i na musamman yatsinci kansa aciki, yajingina kansa da kujera tareda lumshe fararen idanunsa yana cigaba dasakin lallausan murmushi. Har aka kira sallar magriba yafita Rahma bata sake fitowaba, gani take bazatama iya had'a ido dashiba aii. Saida akayi isha'i yashigo gidan dakayan kwalam da mak'ulashe, Rahma najin motsin dawowarsa ta tura Nawal itakam tayi kwanciyarta tak'i fita. Nawal taje tafad'a jikinsa tana masa oyoyo, shima rungumeta yayi yana fad'in babyna kinyi sallah?. Eh nayi nida momy, harta koyamin karatu. Ya ce, "iye kaga 'Yar gatam momynta, ina momyn taki to?. Tana d'aki wai zatayi barci, nikuma nazo wajenka nayi fira. Murmushi yayi Dan yagano tanajin kunyane dankarsu had'u, ya ce, " jeki kiramin ita. Da gudu tanufi d'akin, tafad'a saman Rahma dake kwance kan gado, momy kizo baby na kiranki. Rahma tadafe kai banace kice masa ina barciba?, kuma daga yau kiringa cemasa dady ba beby ba kinji babyna. To momy zandinga fad'a tashi muje to. Badan Rahma tasoba tasakko suka nufi falo itada Nawal. Yana zaune idonsa akan Tv yana kallon labarai ta ce, "sannu da dawowa. Yauwa yafad'a batareda ya kalletaba, ya ce, "ga wannan yamik'a mata ledan kayan motsa bakin. ALLAH yasaka da alkairi tafad'a tana kar6a, kicin tanufa itada Nawal suka juyo afilat, wad'anda bazasu ciyuba tasaka afirij. Takawo masa nasa itakuma tad'auki nasu danufi sutafi d'akinta suci, ya ce, " ina zakuje kuma?. Kanta ak'asa ta ce, "d'aki. sabodani zakuje d'aki cin abinci?. Dawowa tayi tazauna batareda tabashi amsaba, saidai akunyace takeci, shikuma yana satar kallonta har suka gama tashige d'aki tabarsu shida 'yarshi. Shirin barci tayi tai kwanciyarta, dama kayan barcine ajikin Nawal. Yana gama kallon labarai shima yamik'e da Nawal ajikinsa datai barci, yakashe komai sannan yanufu d'akin Rahma. Ahankali yasauke Nawal akusada ita, yay musu addu'a sannan yaja bargo yarufesu idonsa akan Rahma, yanda take barci hankali kwance sai fuskarta tayi wani wasai. Jiki asanyaye yanufi d'akinsa yay shirin barci shima yakwanta............... *_luv u oll my fan's_* *_(((S)))........2017_* [11/12, 2:24 PM] mrs bilkisu: 👩🏻‍💻typing........ ❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣ _•{BoBo}•_ *_NA_* _*Bilyn Abdul*_ _sadaukarwa_ *_Abba Gana_* *_Batul mamman_* *_Billy giro_* 3⃣3⃣=3⃣4⃣ "K!, ina zakije da sassafennan?. Safna ta kwa6e fuska, ummi munafa da Lectures k'arfe 7:30am kuma malamin baida kirki wlhy, gashi ya CE, " test zai mana, tak'are maganar da turo baki gaba. Ummi ta ta6e Baki, ta ce, " shikenan jeki, amma idan kin dawo inason magana dake nida mahaifinku. Gaban safna yafad'i ta ce, "ummi magana kuma?, tami to?. " idan kindawo k'yaji, Dan inama son aikenki gidan Rahma. Kai ummi gidan Rahma fa kikace?, saikace wata k'anwarta. To tunda tarigaki aure aikin zama k'anwar tata aii, ko kina nufin dankince bak'yason mijinta bazakije gidantaba?. Nifa Bahaka nake nufiba ummi, kawai INA dai ganin da kunya. Harara ummi tasakar mata, o sai yanzu kika San kunyar?, alokacin dakikai shirin wulak'antamu kin manta da kunyar. Nidai ummi ALLAH yabaki hak'u, ALLAH fa yariga yarubuta itace matarsa kawai, amma ni ban wulak'antakuba, kawai ina gudun kar asakamin kaina atunkunya ne, saina dawo, tayi saurin ficewa, Dan batason jin amsar ummi, tasan halinta sarai, yanzu saita hau sama ta 6ata mata shirinta, itako awannan lokacin bata fatan abinda zai hanata fita. Ran ummi yak'ara 6aci, duk cikin 'yayanta babu Mara kunyar irin Safna, ita bata iya tauna magana ga mahaifaba, ta maidasu tamkar wasu k'awayenta, kodan gatan dasuka nuna matane abaya?. Tana fita taci karo da Baseera ak'ofar gida. A'a kice kina nan?, dafa shirin shiga gidanku nakeyi, to waima inbanda iskanci miye natsayawa anan?, gidan bak'onkine?. Baseera tarufe murfin motar tana fad'in Bahaka baneba, banason nashiga mu 6ata lokacine kawai. Dariya safna tayi, haba k'awata aganinki zan 6ata lokacine?, kenifa k'agara nayi gari ya waye, yanzun haka jinake tamkar nayi tsuntsuwa na ganni agaban malaminnan. Baseera ta tuntsure da dariya kai k'awata kemafa bakida dama akan abinda kikeso, lallai guy d'innan yayi babbar sata. Safna tak'ara dafe sitiyarin motar, ai wlhy Basee guy d'innan ba k'aramar sata yayiminba, wlhy gaba d'aya ya haukatani, saidai idan natuno kafinni harya zauna da mata biyu nakanji raina ya 6aci, badan ina sonsaba sosai da watsar dashi zanyi. Shiyyasa Nima na d'auki alk'awarin saina mallakesa amatsayin miji kota halin k'ak'a, ke namiki mai kankat wlhy har yarinyarsa saina rabashi da ita, Dan

Table of Contents

Chapters

83 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});