Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 67

Chapter 67

Abdulmalik Bobo Book 1 Complete Hausa Novel 1,196 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

tatafi gida batareda nasaniba?. Idonta ta rumtse tareda sauke sassanyar ajiyar zuciya, wlhy bani nakori aunty Safna ba, kuma bansan abinda akai mataba tatafi, nidai naganta da kaya kawai. To miyasa baki hanata tafiyaba?, Ko kuma ki sanarmin?. Inatsoron kartamin masifane, kuma gashi acikin mutane Muke. Huci yafitar daga bakinsa, yasaka hannu ahankali yana shafa kanta, suduka sukayi shiru nad'an lokaci, jin shirunta yayi yawa yad'ago yalek'a fuskarta saiyaga barci yakwasheta. Maida kansa yayi ya kwanta shima ya lumshe ido amma ba barci yakeyiba yafad'a duniyar tunanine kawai, tundaga randa Appa yay masa maganar auren Safna harzuwa canjamasa da akayi da Rahma, bikinsu, rayuwarsu tanesa nesa, har zuwa yau dasuka zama Abu guda, yad'anyi murmushi dantuna darun Rahma, yasan kishine kawai kecin zuciyarta, jiyayi yak'ara k'aunarta nikin baninkin, yad'ago ahankali yana kallon fuskarta, ahankali take sauke numgashi ak'irjin nasa, fusakarta tayi fayau gawani annuri namusamman datake fitarwa, shiru yayi yana sauraren yanda Nawal take buga k'ofa tana kiran momy! papa!. Tashi yayi ahankali da Rahma ajikinsa, cikin hikima yazameta daga jikinsa ya kwantar da ita tareda kara mata filo, kafin yagyara mata kwanciyarma harta gyra kanta tareda jawo filo tarungume. Murmushi yayi yana mai kallon k'yak'yk'yawar fuskarta, azuciyarsa ya ce, "ragguwa da anta6aki sai barci. Jin Nawal takuma bugawa yamik'e yad'auki tawul yad'aurama k'ugunsa sanan yanufi k'ofar yabud'e. Tana tsaye abakin k'ofar, ya ce, " baby miya faru?. Papa ina momyna?. Saida yajuya yakalli Rahma sanan yadawo da kallonsa kan Nawal, momynki tana aikine jeki kijirata afalo kinji d'iyar albarka. Kanta ta jinjina, ta ce, ''papa nakalli cartoon?. Eh babyna jeki saka MBC 3 kigani, muma yanzu zamu fito. Tafiya tayi abinta tana murna, shima yamaida k'ofar yarufe harda saka key. Bathroom yashiga yay wanka, dama Rahma tahad'a masa ruwan wanka, bayan yagama k'alk'ale k'alk'alensa yafito. Kujerar madubi yaja yazauna, yana cikin shafa mai yaga Rahma yatashi afirgice tana sambatar aunty Safna! Aunty Safna!!, Dan ALLAH karki mutu, A'uzubillahi minashshaid'anirrajim!, sai jikinta ke rawa, da Sauri. Bobo yamik'e yaje yajata jikinsa yarungume, yana kiran my Nusfulhayat nutsu kinji, mafarki kikeyi ba gske bane, nutsu. Hawaye tafara zirarwa, a'a my Nurulk'albi Dan ALLAH ka kaini na ganta, kacemin bata mutuba, wayyo aunty Safna karki tafi ki barni......... Kafin tarufe baki wayar bobo tafara wringing, dak'yar tayarda ya janyeta daga jikinsa yatashi yad'auki wayar, gabansane yafad'i shima Dan ganin sunan ya Shaheed 6aro 6aro akan screen d'in wayarsa. Haka kawai yasamu zuciyarsa dayin rawa, dakuma k'ok'arin gaskata mafarkin Rahma, shiyyasa ba'ason barcin la'asar yafad'a azuciyarsa yana kallonta. Ganin kallon dayake mata saita sake fashewa da kuka, cikin muryar kuka ta ce, "yan gidammune ko?, namasan zasu fad'amin aunty Safna na tarasune kawai...... Tasaki kuka maiban tausayi da tsuma zuciyar mai saurare. Kiran ya Shaheed ne yakuma shigowa, jiki a sanyaye yad'aga yakara akunne, muryar ya Shaheed kawai dayaji yasaka zuciyarsa karaya, bayan sungaisa ya Shaheed yasanarma bobo abinda nikaina banjiba. Cikeda tashin hankali ya ce, "ya Shaheed gamunan zuwa, koda suka yanke wayar.. Innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un kawai bobo ke iya ambata, Rahma tataso ta warce wayar, ganin sunan Wanda yakirashi yasakata fashewa da kuka, matsowayayi Kusada ita ya ce, " addu'a Safna take buk'ata yanzu agaremu Rahma, kinga tashi kiyi wanka muje. Kasa tashi tayi, saishine ya d'auketa yakai bathroom yaymata wankan dakansa, dak'yar yasamu tayi wankan tsarki sanan suka fito, d'akinta yaje yad'akko mata wasu kayan, babu zancen shafa mai zirawa kawai tayi, shima yasaka doguwar riga kawai yakama hannunta suka fito. Afalo suka d'auki Nawal sai gidansu Rahma. Amotama sai kuka take, shima yakasa lallashinta Dan duk arud'e yake, tuk'i kawai yakeyi cikeda damuwa.............. πŸ€”πŸ˜­πŸ˜­πŸ˜­πŸ˜­ *_"Hummm masu karatu akwai damuwafa, mikuke tunani gameda Safna??????."_* *_Luv you oll_* *_(((S)))........2017_* [11/12, 2:59 PM] mrs bilkisu: πŸ‘©πŸ»β€πŸ’»typing........ ❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣ _β€’πŸ…±πŸ…ΎπŸ…±πŸ…Ύβ€’_ *_NA_* _*Bilyn Abdul*_ _sadaukarwa_ *_Abba Gana_* *_Batul mamman_* *_Billy giro_* 6⃣6⃣ Ganin yanufi wata hanya daban yasa Rahma tsura masa idanunta dasuka k'ank'ance saboda kuka, yana kallonta tagefen ido kuma yakula magana takesonyi amma takasa, shima bai iya cemata komaiba, gudu kawai yake shararawa, ganin sunshigo cikin asibitin Rahma takuma yarda mafarkinta ya tabbata, guri bobo yasamu yay fakin kowa yafito jiki a sanyaye, banda Nawal dabatasan wainar da'ake toyawaba, cikin asibitin suka shiga kowa da abinda yake sak'ama zuciyarsa, Rahma takan share hawaye lokaci lokaci. A Reception suka tsaya bobo yakira ya shaheed. Babu dad'ewa saigashi yazo, Rahma tana ganinsa tafad'a jikinsa tana kuka, cirota yayi daga jikinnasa yana fad'in haba Autar Ummi bakisan kin girma bane?, kinga share hawayenki kinji. Cikin shashshekar kuka ta ce, ''yaya waye bashida lfy?. Ya ce, "safna CE." K'ara share hawayenta tayi ta ce, "yaya nasamma aunty Safna tarasu ko?. Idanunsa yazaro ya CE, "haba auta wayace miki tarasu?, a'a tana nan da ranta har yanzudai tana tareda doctor's ne. Ta share hawayenta tana kallonsa, to yaya miya sameta?. Muma bamu saniba Rahma saidai idan likitoci sun fito muji. To muje kokin manta bake kad'ai baceba?. Ita saima yanzu ta tuna tare suke da bobo Dan haka takalli Inda yake tsaye rik'eda hannun Nawal dake kuka tunda taga Rahma na kuka. Da sauri tazo taja Nawal jikinta ta rungumeta tana lallashi, bobo dai da ya Shaheed suna tsaye suna kallonsu. Ganin abun bana k'are bane yasa bobo matsawa kusada ita ya CE, " yakamata mu k'arasa ko. d'agowa tayi ta kalleshi saikuma takama hannun Nawal suka shiga ciki. Acanma tana ganin su Abba taje tafad'a jikinsa tana kuka, dak'yar ya lallasheta tayi shiru, bayan sun gama gaggaisawa suma sukabi sahun 'yan zaman tagumi. .*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*. Har akayi sallar magriba likitoci nakan Safna, su bobo dasu Abba suka nufi masallacin cikin asibitin, sudai su ummi da matansu ya Shaheed duk suna nan zaune jigum jigum, Nawal kam tuni tayi barci, ummi taciro d'ankwalin kanta dayake yanada girma tabama Rahma ta ce, "ta Goya Nawal, amsa Rahma tayi tacika umarnin ummi, gama goyon babu dad'ewa saigasu ya Muneer sun dawo daga masallaci, hakan kuma yayi daidai dafitowar doctors d'in kowa yana yarce gumi, da Sauri kowa yanufesu yana tambayar halinda safna take ciki, duk zame jiki sukai suka gudu akabar doctor Kaleel kawai, kallonsu yayi d'aya bayan d'aya yana share gumi, ganin duk 'yan gidane ya sauke ajiyar zuciya, ya ce, " Alhmdllh munsami nasarar ceto ranta, yanzu haka tasamu barci, yanzuma za'a wuce da'ita d'akin Hutu danhaka Ku kwantar da hankalinku alhaji, komai yazo da sauk'i aii alhaji, sauran bayani kuma sai zuwa gobe idan ALLAH yakaimu. Alhamdllh suka fad'a gaba d'aya, godiya sukaima doctor Kaleel sannan yawuce office d'insa. Tafiyarsa babu dad'ewa aka gunguro Safna a d'an gadon marasa lfy, kwance take sharkaf tana barcin wahala, cikeda tausayi da addu'ar samun lafiya suka bita. Zuwa yamzu fuskokin kowa garage damuwa bakamar d'azunba. Bobo yamatso kusada Rahma ya ce, "My Nusfulhayat ki sauketa mana, aii yanzu Nawal tawuce goyo karkizo k'irjinki yana ciwo. Girgiza MASA kai tayi ta ce, "bafa tada nauyi ALLAH. YA munnir dake kusadasu yana jinsu ya ce, "aidama gida kuka tafi tunda anga yanda jikin NATA yake. Abba ya ce, " gaskiyarka muneer, Abdulmaleek kutafi gida hakanan, kuma su Muneer kud'auki iyalanku Ku tafi gida saboda yara dakuka bari.. Rahma ta turo baki gaba cikin shagwa6a ta ce, "Abba nidai anan zan kwana gsky. A'a auta bazai yuwuba, idan anbarki kin kwana anan mijinkifa, bobo

Table of Contents

Chapters

83 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});