Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 17

Chapter 17

Abdulmalik Bobo Book 1 Complete Hausa Novel 1,195 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kuma tayimusu biyayya, saidai tunkan ayi nisa tafara hangen tarin matsaloli a rayuwar auren nata. Domin kuwa alissafinta yau kwana takwas da kawota gidannan, saidai tundaga randa aka kawota gidan bata sake saka angon nataba a idonta, saidai taji motsin shigiwarsa dakuma fitarsa, kocin abincinsa, idan tatuna kulawar dayayta bata awajen taron bikin saitaita mamaki wlhy, mutum tamkar mai aljanu, kodayake saitaga kamar itama akwai laifinta, tunda ad'aki take wuni, saidai idan taji yunwa tadameta tafita tad'ebo abincin da Ammi ta aiko musu, gidan kansa takasa nutsuwa taimasa kallon tsaf........ Kwala kiran sallar asubane yadawo da ita hayyacinta, tamik'e domin gabatar da sallar, jitayi jikinta duk yayi nauyi saida tayi wanka sannan ta d'auro alwala. Tana idar da sallah taji wani irin barci na d'ibarta, tashitai ta haye gado ta kwanta, cikin 'yan mintuna barci yay gaba da ita. A6angaren bobo kam yamaida dukkan hankalinsa wajen binciko Wanda yayma yarinyarnan fad'e, sukansu 'yansandan dukya addabesu da masifar basusan aikinsuba, sanin shi d'an babban mutumne yasasu dagewa sosai kuma ana hangen nasara zuwa yanzu. Rahma kam yana buk'atar ganinta amma aganinsa ita yakamata tafara nemansa tunda shine babban, ganin kamar tana shamasa k'amshi shiyyasa yafita harkarta ya maida hankalinsa akan aiki. .*.*.*.*.*.*.*.*.*.*.*. Sai k'arfe d'aya Rahma ta tashi, takai dubanta kan agogo, kai harnakai haka ina barci?, lallai nasha barci sosai. Wanka tashiga, bayan tafito tashirya cikin Riga da siket na atanfa kayan sun bala'in mata k'yau, tayi sallar azhur sannan tanufo kicin Dan cikinta yafara kiran ciroma, gashi jiya tacema Ammi adaina kawo musu abinci zata cigaba da girkawa, Dan aganinta yakamata tamik'e wajen juya akalar mijinta zuwa gareta. Alokacin Bobo yana gidansu, Nawal tamak'ale masa saita biyoshi yakawota wajen momynta. Ammi ta ce, "Mukarram inaga katafi da ita kawai nasan insha ALLAHU Rahma zata rik'eta da Amana, kasan yarinyarnan kullum burinta ta kasance da mamanta akullum. Bobo yahad'iye yawu Ammi ba tafiya da Nawal bane matsalar ina ganin kamar idan nad'auketa ban k'yauta mukuba. Ammi tayi murmushi Wlhy ko d'aya mukarram aii munsan ba k'waceta kayiba, dama tunjiya Appanku yay maganar yau idan kazo kawuce da ita. To shikenan Ammi ngd, ahad'a mata kayanta to muwuce. Ammi tahad'o mata kayanta, wasu kam sai ahankali aringa kaimata. Nawal kam sai murna take yau zata wajen momynta. Ammi bari mutafi naga Appa haryau bai dawoba, gobe idan ALLAH yakaimu ma had'u, Dan zan koma aiki. Ammi ta ce, tom ALLAH yatsare, yakaimu lfy, tazo gefen Nawal tana d'aga mata hannu. Bobo yatada mota, yauwa Ammi idansu khairy sun dawo suhad'amin kayana duka Nima. To zan Sanar musu agaidamin da d'iyar tawa. " zataji." Haka suka fice ammi da Nawal suna d'agama juna hannu. .*.*.*.*.*.*.*.*.*.*. Rahma na zaune a falo tazurama filet d'in indome idanu, dukda 'Yar Karen yunwar datakeji amma abincin yagagara ciyuwa agurinta. Tabi falon da kallo, caraf idanunta suka sauka akan wani hoton Bobo yana zaune akan wata kujera, fuskarsa d'auke da tsadadden murmushi mai kashe zuciya, saina kusadashi shida Nawal, wanikuma a can gefe shida yayyensa maza dasu Ammi da khursiyya da khairiyya, sunyi k'yau sosai, daka gansu Kasan ciki d'aya suka fito masha ALLAH.... DA gudu Nawal tashigo tana kiran Momy! momy!!, da Sauri Rahma tamik'e Nawal tafad'a jikinta, itama saita rungumeta. Ahankali Nawal ta ce, momy I miss u. Miss u too my baby Rahma tafad'a tana mamakin 'Yar waye kuma wannan?. Nawal takatse mata tunani da fad'in , momy inakikaje kika barni?, kullum saina tambayi baby da Ammi sai sucemin kina zuwa amma baki zoba. Cikin mamaki Rahma tad'agota daga jikinta tana kallonta, gata 'Yar mitsila sai zance irin na manya. Bobo na a tsaye yana kallonsu, Wanda azahiri kallonsa akan Rahmane, Ashe k'yan dayake kallonta dashi awajen taron biki tafi k'yau a Natural batareda kwalliyaba..... Maganar Rahmace takatse masa tunani, ta kuma rungume Nawal tana fad'in tom gani nadawo babyna kiyi hak'uri kinji. Ita sai yanzu tatuna ance mata Bobo yanada d'iyama, jitayi tausayin yarinyar ya mamayeta, ALLAH sarki Rayuwa, ALLAH baya Barin wani Dan wani yaji dad'i, tafad'a acikin ranta. Nawal tazare jikinta tanufi Inda Bobo yake, hannunsa takamo cike da murna tana fad'in baby naga momyna yau. d'an murmushi yayi ya ce, "natayaki murna babyna, karasowa cikin falon sukai yazauna. Rahma ta daure ta ce, ina yini?. Lfy ya amsa batareda ya kalletaba. Rahma ta ta6e baki aranta ta CE, " dama baka amsaba aii, dama na gaidakaine saboda kana gaba dani. Maganar Nawal ce tasakata dawo da hankalinta Kansu, Nawal ce takai bakinta Kusada kunnen Bobo wai zata masa Rad'a, amma kuma kanajin maganar tata. "Baby mikayima momy tak'icin abinci?, koka duketane?. Da sauri Bobo ya kalli Nawal a'a baby ban daketaba, k'ila batada lfyane. Tamaido dubanta kan Rahma, momy waibakida lfy inji baby. Rahma tayi d'an murmushi A'a lfy ta k'alau, to momy idan lafiyarki k'alau miyasa bakici abinciba?, ko kinaso baby yabaki dakansane?...... Kafin Rahma tayi magana Nawal tamaida dubanta ga Bobo, baby kabama momyna abinci abaki kamar yanda kake bani idan nak'ici. Bobo ya ce, "to baby idan banda abinki....... Da Sauri ta ce, "baby indai baka bama momyna abinci abakiba mun 6ata daga yau, ta tashi daga kusadashi takoma kan cinyar Rahma data daskare azaune danjin furicin Nawal. Rahma tadaure ta ce, ''kinga babyna zanci dakaina, Dan lfy ta k'alau, kibar Dady yahuta kinga ya gaji ko, tashima muci tare. Nawal ta tashi zaune, Rahma taringa bata abincin itama tana dannawa badan yaymata dad'iba, saboda damuwar dataima zuciyarta yawa. Bobo yanad'an satar kallonsu, tabbas yaji dad'in yanda Rahma takar6i d'iyar tasa wadda akullum yake zullumin sama mata madadin mamanta data rasa...... Yanata tunaninsa harsuka mammala, Nawal ma tafara barci, mik'ewa Rahma tayi da ita zuwa d'aki, dama zaman dukya gundireta. Yabita da kallo k'asa k'asa babu laifi tanada k'yau daga na fuska harna jiki, saidai bazai sotaba Dan Ni'imarsace kawai keda gurbin zama azuciyarsa. "na ce, "hummmm ALLAH yasa." Itakam Rahma koda takwantar da Nawal saitayi zamanta bata sake fitiwaba, sai bayan sallar la'asar. Sannan baya falon, tanufi kicin tana fad'in baridai yau nayi girki kodan Nawal, had'ad'd'en abinci na gargajiya tahad'a mairai da lfy, tagyara kicind'in tsaf kamar ba'ayi komaiba, hakama falon takuma bad'e ko ina da nau'in turarurrukan wuta. Saida tayi Sallar magriba sannan tayi wanka tayima Nawal, shiri tayi cikin wando dariga na Pakistan sky blue, rigan iya cinya sai wandon yakamata sosai, amma tayi k'yau kamar kasaceta kagudu, itama Nawal tasaka mata 'Yar Riga Mara nauyi. Harzasu fito Nawal ta ce, "saita goyata, Rahma taduk'a Nawal tad'ane. Falon suka fito inda ta tarar da Bobo zaune akan kujera mai d'aya ya d'ora k'afafunsa saman k'aramin tebir na gilas yana karanta jarida, gefensa lemo na kwali da Kofi anzuba rabi, yana sanye da wando 3/½ fari da riga ja Mara hannu. Masha ALLAHU Rahma tafad'a azuciyarta. Baby kalleni Nawal tafad'a tana d'agama Bobo hannu. d'an d'agowa yayi ya ce, " naganki baby yamaida Kansa. Rahma tasauketa tana fad'in tonima gobe saikimin goyon. Nawal tawaro idanu waje kamar wata babba, lah momy bazan iyaba saidai baby yay miki, taje tadafa bobo, baby. Ya ce, "na'am. Zaka ramama momy goyon data minko?, kagani ban girmaba, bazan iyaba.. Bobo yakalli Rahma dake zaune tana mamakin wayau da surutu irinna Nawal, Dan yau d'aya tafahimci Nawal d'in tanada

Table of Contents

Chapters

83 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});