Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 52

Chapter 52

Abdulmalik Bobo Book 1 Complete Hausa Novel 1,194 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Kasan hakane. Bakomai zan rama, yanzudai miye na kirana?. Dama zan tambayrkane ko kana office?. Kabari kawai wlhy namakara, yanzudai INA hanyar zuwa gidan Appa, amma daganan office d'in zan wuce. OK to kabiyo tanan mana idan bakada wani uzuri. Kai nifa Kasan banason zuwa office d'inka, wannan masu bak'ak'en kayan daka wani baza suyita kallon mutum. Hhhhh toka had'une shiyyasa suke kallonka, Inda basu sankabama bazasu barka ganinaba ehe, ato bara nayi zamana Idan kamatsu kazo office kasameni. Hhhhhh to yi hak'uri na Ammi kodayake yanzu kazama na Rahma. Dariya bobo yayi ya yanke wayar, baikai ga ajiyewaba kiran Ya Sulaiman yashigo, yad'aga suka gaisa. Bobo ya ce, "yaya dama wlhy INA niyyar kiranka, magani nake buk'ata. Maganinmi bobo?. Ummm saidai Nazo, inafata kana asibiti. Eh, amma kai kana ina?. Gani zanje gaidasu ammi, OK nima yanzu nabar gidan babu dad'ewa nida ya ishaq da Hamza. Ayya tosaina shigo. Okey, ina jiranka. Bayan ya ajiye wayar yakalli Rahma kad'ain ya kauda kai, murya k'asa k'asa ya ce, " gara naje na k'ar6o miki magani wannan tafiyar taki tadawo daidai, damma kinki hak'ura ne amma yanzu haka zakije gidan Ammi kina tafiyar 'yan kaciy...... Bai k'arasaba yay saurin rufe bakinsa da hannunsa yana dariya. Rahma taturo baki gaba, yakuma kallonta yashek'e da dariya. Ba Rahmaba har Safna da Nawal saida suka kallesa, suna had'a ido da Safna ta madubi ya gimtse fuska. Aranta ta ce, ''zakazo hannune malam. Itakam Rahma ta ce, "mugu d'an masa sai ALLAH yasakamin aii. Da hakadai suka k'arasa gidan AMMI. Safna da Nawal suka fice, Rahma na niyyar fita bobo ya kulle motar, juyowa tayi tana kallonsa shima ita yake kallon, ya ce, "yadai 'yammata namiki k'yaune?. Kauda idonta tayi daga kansa, ta ce, " Dan ALLAH kabud'emin. Aidama zan bud'e miki, sonake nacemiki kiyi k'ok'ari koyaya kid'an gyara tafiyarki inba sokike kowa yasan miya faruba. Kallonsa tasakeyi, saikuma tayi k'asa da kai tana turo baki gaba, nifa wlhy zafi nakeji awajen. Shiyyasa nace ai kiyi zamanki sai gobe amma kikak'i, amma babu damuwa bara na kar6o miki magani wajen ya sulaiman, yanzudai muje ciki, amma idan kinje kiyi kwanciyarki ki huta kinji. Batace komaiba takama k'ofa zata bud'e yarik'o hannunta haba tawan ko sallama babu?. Tokai bazaka shigaba?. Jawota jikinsa yayi yana fad'in zan shiga mana, amma ai bazan dad'e ba, k'ok'arin saka k'wayar idonsa yake anata itakuma tak'i basa dama, saima talumshe idanunta gaba d'aya, wani murmushi yayi Wanda har tanajin sautinsa, jin bakinsa kan nata yaskata saurin zabura, amma ina tamakaro yarigada yayi nasarar cafkar harshenta. Na ce, "humm bara nakoma daga waje najiraku." Ak'alla sunkai minti biyar sannan naga Rahma tayi saurin fitowa tana murmushi, shima bobo yafito yana dariya, gaba tayi abinta hartana had'awa dad'an gudu, bin bayanta yayi yana fad'in matsoraciya kawai. Ak'ofar falo tatsaya ta daidaita nutsuwarta sannan tashiga. Gaba d'aya yaran suka taso suka tareta, itama tahad'asu tarungume tana dariya, Rahma akwai San yara shiyyasa duk inda taje saikaga yara suna sonta. Bobo yana shigowa suka saketa suka nufeshi, zama Rahma tayi suka gaisa da su aunty Rasheeda, aunty ummy, aunty sameera, khairiyya da khursiyyama suka gaisa. Bobo yak'araso shima suka gaisa su aunty Rasheeda suna tsokanarshi, Rahma dai mik'ewa tayi tanufi d'akin Ammi itada khairiyya. Bobo ya ce, "ALLAH idan baku daina matsaminba saina saka mazanku sun k'ara aure. Da sauri aunty Sameera ta ce, " a'a Abdulmaleek wlhy nikam nabari yi hak'uri, tashi yayi yana murmushi ya ce, "waiku mata miyasa kuke tsoron kishiyane?. Aunty Rasheeda ta ce, " jeka katambayi Rahma, d'akin Ammi yanufa yana fad'in ai ita bata tsoron kishiya. Dariya suka saka gabad'aya shikuma yashige d'akin Ammi da sallama. Ammi ta ce, "a'a mukarram d'ina kaine?. Wlhy nine Ammi wad'ancan 'ya'yan naki duksunbi sun rainani, nakusa daina musu dariya. Dariya Ammi tayi ta ce, " kunfi k'asa aii. Shima dariyar yayi sannan yagaida Ammi cikin girmamawa, yanayi yana satar kallon Rahma dake zaune kusada Ammi suna ware wasu kaya itada khairiyya. Ya ce, "Ammi yunwa nakejifa. Kallonsa Ammi tayi tana dariya, haba mukarram aii gwauro aka sani da zama da yunwa, murmushi yayi shima, ya CE, " Ammi nima tawa matarce babu lfy." Ayya, Ammi tafad'a tana kallon Rahma, nima tunda tashigo nake kallonta duk naganta sukuku babu walwala sosai, ga idonta sund'an kumbura, mike damunta?. Sosa kansa yayi yana fad'in em...em.. Ammi zazza6ine. Dariya Ammi tayi ta ce, " mukarram magana da in ina kamar mara gsky. No Ammi inada gsky kawai inaso natuna sunan zazza6inne. To ALLAH yabata lfy kunje asibitine?, a'a ammi jiya da daddare zazza6in yasameta, dama yanzu zanbiya tawajen ya sulaiman na kar6o mata magani. Okey to Aida tayi zamanta agida tahuta ko. babu yanda banyi da ita tazaunaba amma fir tak'i wai itadai saitazo, yayi maganar yana kallon Rahma. Tana jinsu amma tashare kamar batasan zancen da akeba, Ammi ta ce, "khairiyya jeki had'omusu break fast ko, suma su Safna haka. To Ammi khairiyya tafad'a tana mik'ewa. Ammi da bobo suna 'Yar hirarsu khairiyya takawo break fast, bobo yalangyare wai saidai Ammi tayi feeding d'insa. Rahma tad'ago ta kalleshi saiya yimata gwalo, Ammi na kallonsa, danhaka tayi murmushi had'eda girgiza kai, koba komai tasan d'anta yasamu farinciki daga matar tasa,. Rahma d'auke idonta tayi daga kansa tana d'an murmushi, aranta ta ce, " Indai ta6arace kaganta salo salo ga daddyn Nawal, wani abunma idan yayi saiya baka dariya wlhy. Ammi kam dakanta tabama bobo abincin yaci, saida yak'oshi sannan yamik'e, AMMI bara nad'anje office naga mike tafiya. To ALLAH yabada sa'a yatsareka babana. Amin ammina. Ya kalli Rahma, ya ce, "my cute nawuce. ALLAH yabata kunya amma saita dake ta ce, " ALLAH yabada sa'a, ameen yafad'a yana fita, idon ammi kawai yahanashi mata kiss. Afaloma yamusu sallama yafice. Da sauri Safna ta tashi tabi bayansa.................. *_luv you oll_* *_(((S))).......2017_* [11/12, 2:57 PM] mrs bilkisu: πŸ‘©πŸ»β€πŸ’»typing........ ❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣ _β€’{πŸ…±πŸ…ΎπŸ…±πŸ…Ύ}β€’_ *_NA_* _*Bilyn Abdul*_ _sadaukarwa_ *_Abba Gana_* *_Batul mamman_* *_Billy giro_* 5⃣8⃣ Bobo dabaisan Safna nabinsa abayaba yabud'e mota yashiga, harya tada motar yaji ana kwankwasa masa gilas. Sauke gilas d'in yayi ahankali Dan atunaninsa Rahma ce kosu khursiyya, had'e fuska yayi Dan ganin safnace, baice komaiba ya kauda kai daga kallonta. Rik'e k'ugu tayi tanamai jifansa da shu'umin kallo, cikin narkewar murya ta ce, "haba my jaan wai miyasa kakeson wulak'antanine?, aiko bakomai ance kaso mai sonka, yanzu Dan ALLAH abinda kamin agaban Rahma d'azun yadace?. Tsaki yaja tareda yatsine fuska tamkar Wanda yaga kashi, ya ce, "ke awa? dabazan miki abu agaban Rahma ba?. Ya nunata da d'anyatsa wlhy kifita hanyata, karki yarda kibari na nunamiki asalin colour d'ina, ina d'aga miki k'afane saboda 'Yar uwarki, amma zakisha mamaki idan kikacigaba da bibiyata....... Kafin ta ce, " wani Abu yaja motarsa yafice, dama tuni mai gadi yabud'e masa gate. Hawaye suka kwararo afuskar safna, wani d'an lungu tasamu dagacan baya ta zauna, saida tad'anyi kuka sannan tad'auki waya takira baseera, bata d'agaba takuma kira nanma haka, ajiye wayar tayi tazabga tagumi cikeda damuwa. Su Rahma suna ciki basusan bikin da akeba, bayan sungama ware kayan da ammi tasakasu suka dawo falo wajen sauran 'yan uwansu suna hira, saidai hankalin Rahma yana kan tunanin ina aunty Safna?, gashi batason tashi Dan gudun karsu fahimci halin datake ciki,

Table of Contents

Chapters

83 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});