Chapter 6
Chapter 6
reras. Agidama khairiyya da khursiyya da Nawal sallar sukayi, ammi ma haka. Bayan an idar ammi tasakasu suka shirya abinci a tsakkiyar falon Dan yau duk su ya Is'haq anan zasuci abinci, suka gama shirya komai da taimakon 'yan aiiki sannan suka koma d'aki domin gabatar da sallar isha'i da aka kira. Basu dawoba saida akayi sallar isha'i, suka rankayo zuwa gida suna 'Yar hirarsu da tsokanar juna. Afalon suka zube Appa ya ce, ''aini zuwannan naku yamin daidai, kamar kunsan dama ina nemanku. Ya Hamza ya ce, "to Appanmu ALLAH yajishemu alkairi. Amin suka fad'a gaba d'aya. Ammi dasu khairiyya suka fito suma, rissinawa sukayi suka gaida Appa da yayyensu, Nawal taje jikin Appa tazauna. Yashafa kanta yana fad'in amaryata kinyi sallah?. Kai ta jinjina tana dariya. Tomi kika rok'amana?. Hannunta tasa abaki idonta na kallon p,o,p d'in falon alamar tunani, can takalli Appa tana washe wawulinta da hak'ori biyu yafad'i, ta ce, " Appa kasan mina rok'a?. Saikin fad'amin amaryata. Narok'i ALLAH ya kaimu Aljanna nida kai, da Ammi, da baby, da uncle Sulaiman, da uncle Hamza, da Uncle Is'haq, da aunty khursiyya da aunty khairiyya, da mom din gida uncle Is'haq, da momyn ya Ahmad da aunty Sameera, kuma nace ALLAH yasa muje makakka muduka sau dubu dubu babu iyaka muga kabarin Manzon ALLAH a madina. Tafi sukai mata gaba d'aya suna fad'in ameen mai sunan manya. Ya Is'haq dake kusada ita har sumbatar hannunta yayi. Appa ya ce, ''lallai na more da amarya Ashe. Ta ce, "Appa kasan mikuma na rok'a daga k'arshe?, ya girgiza kai yana murmushi, canayi ALLAH yasa nima naga momyna. Gaba d'ayansu kallonta sukayi, tabasu tausayi sosai, Appa ya rungumeta cikeda tausayi, Bobo kam k'asa yayi da kansa zuciyarsa tayi rauni sosai, jiyake tamkar yafasa kuka saboda tausayin 'yarsa, tausayinta yana d'aya daga cikin abinda yasa yak'i k'ara aure, bayason ya auro wadda zata takurama d'iyarsa sanyin idaniyarsa. Ya Hamza ya ta6ashi d'agowa yayi yana kallonsa, ya Hamza ya jinjina masa kai fuskarsa d'auke da tausayi. Murmushi bobo yayi. Saikuma ya kalli sauran 'yan uwannasa da iyayensa yaga dukshi suke kallo. Kansa yamaida k'asa yana cigaba da murmushi mai ciwo. Ganin haka Ammi ta katsesu da fad'in bismillah kusauka ga abinci. Kowa ya sakko tskkiyar falon in da abincin yake. Bayan Ammi tasakama Appa kowa yafa k'ok'arin zubama Kansa abinda yakeso. Falon yayi tsit bakajin motsin komai sai k'arar filat da cokali, saikam surutun Nawal lokaci2. Bayan sun kammala cin abincin 'yan aiki suka gyara wajen tsaf, Appa yakalli khairiyya ya ce, "auta zoki kaita d'aki ta kwanta. To Appa khairiyya tafad'a tana mik'ewa, d'aukar Nawal tayi daga jikin Appa tanufi d'aki. Falon yay tsit kowa ya maida habkalinsa kan Appa. Appa yamusu sallama suka amsa. Ya gyara zama cikin hikimar zance yafara musu nasiha da k'ara jaddada musu muhimmancin zuminci da hak'uri da juna, ahankali ya gangaro kan auren Bobo, Wanda tunda Appa ya ambaci sunansa gabansa yafad'i. Appa yabasu labari kamar yanda yagayama su Ammi da ya Is'haq jiya. Ya d'ora da fad'in yanzu dai mun yanke hukunci ranar juma'a idan ALLAH ya kaimu za'a tura dakomai har sadaki Dan badogon lokaci za'a d'aukaba, k'arshen watannan za'ayi bikin kowa ya huta. Zuface tafara fita addukan sassan jikin Bobo, yakasa koda motsi dukda tsokanarsa da 'yan uwansa sukeyi suna fad'in ango kasha k'amshi. Ammi ma sai dariya takeyi danjin dad'i, sai Alhmdllh take dad'i, su khursiyya kam harda 'yar bud'a. Bobo ya galla masu harara. Gaba d'aya akayi dariya harda Appa. Daganan suka cigaba da tattauna yanda biki zai gudana da shagalin daza'ayi. Appa ya ce, " suyi duk abinda sukeso bazai hanasuba, Dan Andad'e ba ayi wani shagaliba agidan. Har k'arfe tara suna gidan, saida Appa yace yakamata sutafi gida hakanan wajen iyalinsu sanan suka mik'e kowa yanufi gidansa. Bobo bayan yarakasu harabar gidan yanufi d'akinsa jikin a sanyaye, yama rasa wane irin tunani zaiyi shikam............. _Tofa masu karatu, Yaya kenan?, shin ina Safna?, gafa gwaninta zai angwance, kowacece amaryar Bobo?, ya wannan zama zai kasance?, kudai biyoni kawai, basirar aunty bilyn Abdul ce, nikam copy nakemuku masoya._ *_hummm wasa farin girki, masoya yanzufa aka fara, kumuje zuwa wai mahaukaci yasai kura, yanzu muka dasa alk'alamin labarin Bobo!._* *_masoya muna godiya ALLAH yanar zuminci._* [11/12, 2:15 PM] mrs bilkisu: 👩🏻💻 ❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣ _{Bobo}_ _Story & editin_ *_Aunty Bilyn Abdul_* ✍🏿 _Written_ *_Marak'isiyya_* _hak'in mallaka_ *_Aunty Bilyn Abdul_* _sadaukarwa_ *_Abba Gana_* *_Batul mamman_* *_Bily giro_* 1⃣3⃣&1⃣4⃣ *_Gidansu Safna_* Safna na kwance akan gado tana chart, sai faman murmushi takeyi, da alama tana jin dad'in charting d'in. Rahma dake zaune akan sallaya tana karatun alkur'ani ta waigo ta kalli safna dataketa 6a66aga dariya harda rik'e ciki, kai Rahma ta girgiza tareda fad'in ALLAH ya shirya azuciyarta. Kanta tamaida tacigaba da karatunta. Safna kam bamatasan tanayiba, dariyarta taketayi cikin farinciki, hira takeyi da Baseera akan nemomata Bobo, Baseera tana gayamata akwai wani guy a unguwarsu sunansa *boy shiyakama subama aikin, Dan tasan cikin sauk'i zai samomusu bobo da labarinsa. Tak'ara wani d'an ihun farinciki, tareda fad'in saini mata agidan Bobo. Rahma takuma kallonta cike da mamaki, ganin bazata barta tayi karatunta cikin Nutsuwaba yasa tarufe alkur'anin tayi addu'oin ta tamik'e ta ajiye alkur'ani ama'ajiyarsa. Hijjabinta tacire tana fad'in aunty Safna kofa sallar magriba bakiyiba har anyi isha'i amma kina kwance kina charting akan abinda k'ilama bazai amfaneki da komaiba. ALLAHU Akbar maikaratu nagaba, Safna tafa idonta akan waya, tacigaba da fad'in malama Rahma jawo wata ayar na haddace wannan. Ajiyar zuciya Rahma ta sauke, ta ce, "Niba malamarki bace, kuma ba wa'azi nake mikiba, ina tunatar dakene dannaga kin shagala. Wani wawan dundu safna tasaukema Rahma abaya, Dan ubanki idan aljanna takice ki hanani, shegiya 'Yar iska uwar tsari, kenikam daba agabana ummi ta haifekiba wlhy danace anmata canji a asibiti, anya kuwa acikin 'yan barka wata bata sace ainahin d'iyar da ummi ta haifaba ta ajiye mata ke?. Rahma tashare hawayenta ta ce, " kije kitanbayeta k'iladai kece aka canja mata, Dan halinki daban dana mutanen gidanna. Afusace Safna taduro daga gado tana d'urama Rahma zagi. Tuni Rahma tafice tabar mata d'akin. Afalo taci karo da abbansu yadawo masallaci, sannu da dawowa Abba. Yauwa d'iyar albarka ina zuwa haka?. Ba inda zani Abba, nadai fito falone nasha iska. Masha ALLAHU, ina 'Yar uwar taki to?. Tana d'aki Abba. Yauwa jeki kiramin ita zamuyi magana, ina umminku?. Ganinan Abba Shaheed ummi dake fitowa daga d'aki tafad'a. Tamai sannu dazuwa sannan tafara shirya musu abinci. Rahma tatsaya abakin k'ofa ta ce, "aunty Safna kizo Abba yana kiranki. Shegiya munafuka gulmata kina kaimasane?. Niba munafuka bace, yace dai kizo..., tana gama fad'a tafice. Safna tasakko daga gadon tana mita, zan koya miki hankaline 'Yar banza maikan dankali. (Araina nace kekuma maikan doya ko?.) Kusada Abba taje tazauna, Abba gani. Kanta yashafa yana murmushi haba safnan Abba miya faru kika k'unshe kanki a d'aki?. Zamanta ta gyara tana ballama Rahma harara, babu komai Abba nayi sallane INA zaune ina Azkar. Da k'yau 'Yar albarka. Rahma kam ido tazaro waje danjin k'aryar da safna ta gilla, saikuma ta k'unshe baki tana dariya. Safna na kallonta, Dan haka haushi yak'ara kamata. _(Hattara iyaye kuringa kula da addinin 'ya'yanku, akwai yara dayawa masu wasa da salla irinsu Safna, wata
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83