Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 64

Chapter 64

Abdulmalik Bobo Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

cigaba da yawan kallonsa sai rankowa ya6aci awajennan Dan haka ku kama kanku. Wata ta ce, " amma ba gidannan yakeba?, Dan ban sanshiba. Dariya khairiyya tayi ta ce, "to k'arewar gidannanma shi muke bimawa, dagashi saimu. Cikin mamaki sukace amma dai wasu sun rasu a tsakaninku?, kumafa mudai bamu sanshiba, kai 'yan biyu kuji tsoron Allah. Hhhhhh lallai baku yardaba kenan?, to yagirmemu sosai Dan Ammi ta ce, " wajen ahekara 12 yabamu, bayan shi harma ta fiddarai da haihuwa saigamu mun wuntsilo, abinda yasa Baku sanshiba bashida hayaniyane, kuma bakowace sabga bace zaku ganshi aciki, shinefa wanda kukazo bikinsa wata biyar dasuka wuce baya. Idanu suka zaro, Zainab kabeer ta ce, ''wlhy bamu ganeshiba kinsan da daddare muka Ganshi awajen deener, masha ALLAHU, ina matarsa?. Tana nan bara zaku ganta aii. Bobo dabaisan sunayiba yahaye saman mota yazauna Dan bayason shiga falon saboda duk matane, harabar gidan tad'anfi k'arancin mutane tunda an ragu, Taufiq babban d'an ya ishaq yakira, ya ce, "my son ina auntynka?. Taufiq ya ce, "uncle aunty Rahma?. Eh, ita. Yanzu naganta itada heebba sunshiga falo. Yauwa jeka kiramin ita to. To uncle. Babu dad'ewa saiga Taufiq yadawo ya ce, " uncle tana zuwa. Okey my son, yanzu kuma sai ina?. Uncle muna tarene nida abokaina. Kaima gayyan kayo wajen taron mata?, maimakon kabari sai ranar d'aurin aure ko gobe wajen brother's Night. Uncle aii duk zasuzo shima. Dariya bobo yayi ya ce, "to na mata. Shima Taufiq tafiya yayi wajen abokansa yana dariya. Na ce, " masha ALLAHU yaron yafara zama saurayi, su bobo ankusa ajiye surukai, lol. Yana zaune awajen yana latsa waya saiga Rahma tafito. Kamshin turarenta kawai yaji yad'ago. Kallo d'aya tamasa ta kauda kai. Murmushi yayi yana kallonta, ya ce, "kai my Nusfulhayat kinyi k'yaufa, kamarma kece amaryar wlhy. Ganin ta kauda kai ya ce, "madam har yanzu fishinne?. Batace komaiba itadai, kuma fuskarta asake take gudun kar mutane su fahimci wani Abu. Ya ce, " my Nusfulhayat yunwafa nakeji, gashi duk mata agidan nama rasa yanda zanyi. Murmushi mugunta tayi ta ce, "ina Safnar tabaka abinci?, ko sak'one naje nafad'a mata?. Kallonta yayi ido cikin ido, tai saurin kauda kanta Dan bazata juri kallon cikin idonsaba, shima murmusawa yayi ya ce, " idanma kinyi hakan ai babu laifi, yadiro daga saman motar, ki kaimin falon su inna munacan nidasu ya Sulaiman. Baijira amsartaba yawuce............ *_"happy juma'at Mubarak."_*πŸ™‹πŸΌπŸ™‹πŸΌπŸ™‹πŸΌπŸ™‹πŸΌ *_luv u oll._* *_(((S)))......2017_* [11/12, 2:58 PM] mrs bilkisu: πŸ‘©πŸ»β€πŸ’»typing........ ❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣ _β€’πŸ…±πŸ…ΎπŸ…±πŸ…Ύβ€’_ *_NA_* _*Bilyn Abdul*_ _sadaukarwa_ *_Abba Gana_* *_Batul mamman_* *_Billy giro_* _a *RASHIN SANI* nayi *AUREN K'ADDARA ko BIYAYYA,* mizan d'auketa?, *K'ANWAR UWACE ko KISHIYAR UWA?.* San zuciya yakawo sa6ani *NI DA AMINIYATA*, salon *NAWAFF* yasani fuskarntar *SABON AL'AMAREE*, *KUKAN KURCIYA JAWABINE* dan haka kugane *BAN SAKETA BA* masoyan *ABDUL-MALEEK BOBO* mukasance tare a *BABU SO, MIYA KAWO KISHI?!!!*._πŸ‘ŒπŸΌ _wad'annan sune rukunin jerin books dani bilyn Abdul narubuta a social media._ Zaku iya samunsu a shafina kamar haka.πŸ‘‡πŸ» https://mrsbilkisa.blogspot.com *_sai kunjeπŸ‘ŒπŸΌ._* *_BAK'IN HAURE!_* zaizone a sabuwar shekarar 2018 insha ALLAHU, karku bari ayi babu ku😘. 6⃣4⃣ Binsa tayi dakallo tana k'unk'unai, amma baijitaba Dan yayi gaba abinsa. Safna tana dagacan saman kujera tana kallonsu, hawaye suka cika mata ido taisaurin saka handkyn daya bata jiya tagoge, ta Yanke shawara yau zatabi su Ameera sutafi gida, Dan inhar tana ganin bobo bata tunanin sonsa zai ragu azuciyarta barema ayi tunanin fita gaba d'aya, amma idan tayi nesa dashi k'ila taji sauk'in zuciyarta, Dan insha ALLAHU tayi tuba na gsky kenan. Rahma tahad'a musu abincin Wanda dama tun d'azu ta tanada domin su, ihsan da Basma ne suka tayata d'auka zuwa 6angaren inna. Duk sunacan harda Ammar dawasu mutum biyu dabata saniba, bayan sun ajiye suka gaidasu, idanun bobo nakan matarsa, itama tasaci kallonsa ganin idonsa akanta yasa ta kauda idonta tareda Jan hannun su ilham suka fice. ...........................Γ· Bayan sallar isha'i su anty Hafsat sukace zasu wuce, Safna data gama had'a kayanta tamik'e itama, kallonta kawai Rahma takeyi amma batace komaiba, su dama su aunty Ameera tafad'a musu zata bisu Dan gidan yacika damutane kuma Rahma anan zata kwana itama, basu kawo komai aransuba sukace eh gara kawai tatafi gida. Har harabar gidan tarakasu saida suka Shiga mota taga fitarsu sannan takoma ciki. Amota Safna cikin dabara take share hawayenta, wata zuciyarta tana fad'a mata anya zata iya daurewa kuwa?, da sauri ta ce, "insha ALLAHU zan iya. .+.+.+.+.+. Tafiyarsu Safna babu dad'ewa sosai bobo yashigo falon, wasu kallo sukeyi wasukuwama harsun kwanta, yagaidasu sannan ya haura sama, afalo yatarar dasu zaune sunata kulla kayan rabo, zama yayi yana fad'in wai Kodai yau anan zamu kwanane?. Kallonsa ammi tayi, ta ce, " nidama zaku barsu su kwanan Aida yafimin, idan bamu gamk'ullin nan yauba nasan zuwa gobe gidannan zai d'inke da mutane. Kansa yashafa yana d'an murmushi Ammi sudai gama kawai saimu wuce ko zuwa 12 ne. Hararsa Ammi tayi cikin wasa, ta CE, "fin k'arfi za'a nunamin akan 'ya'yana?. A'a Ammi mu mun isane. Hira sukaitayi har su ya ishaq suka shigo suka had'u gabad'aya sukayi k'ullin sannan kowa ya d'auki matarsa sukai gida. Biki yacigaba da kankama cikin farin ciki, komai yana tafiya yanda yadace, washe gari da safe akayi k'unshi, zuwa yamma gida kam ya d'inke da bak'i na nesa Dana kusa, su Rahma kam aii ko ganinsu ba'ayi Duk sun zama busy, to barema su bobo manya manyan yayye. Da daddre k'arfe takwas aka fara d'ibar mutane zuwa wajen brother's night dasu bobo suka shirya, abokansu sosai suka gayyato, taron 'yammata da samarine kawai saikuma irinsu bobo masu mata, amma babu yara bare tsofaffi. Taro yak'ayatar kam masha ALLAH, amare da angwayensu ansha k'yau abin sai Wanda yagani, su bobo suntaka rawar gani irinta manyan yayye, ko INA yashiga yana mak'ale da matarsa abin zak'yk'yau da burgewa, 'yammata kam dayawa sun k'yasa, saidai ganinsa mak'ale da matarsa yakansa sushiga taitayinsu. Alhmdllh dahaka taro yatashi lfy kowa Yakama gabansa. _washe gari_ Aka d'aura auren khairiyya Aliyu Abdulmaleek hamshak'i da angonta Ahmad m sadiq, sai Khursiyya Aliyu Abdulmaleek hamshak'i da angonta Zaharadden usman Aliyu. Masha ALLAH d'aurin aure yatara d'unbin jama'a nanesa Dana kusa 'yan siyasa da masu mulki, 'yan kasuwama ba'a barsu abayaba. To khairiyya da khursiyya saimuce ALLAH yasanya alkairi yabada zaman lfy da zaman hak'uri. Hummmm abun mamaki wai harda alhaji sunusi dala a 'yan d'aurin aure, (araina nace su alhaji sunusi anji yaji🌢🀣 ahanun bobonmuπŸ˜ŽπŸ˜‚πŸ˜œ) aiko bobo sai antaya MASA kallon banza yakeyi. Shidai baimasan yanayiba. Bayan kammala d'aurin aure su bobo sukaima anguna jagora zuwa cikin gidan, shidasu Yaya ishaq duk wankan farar shadda sukayi, masha ALLAH daka gansu kaga 'yan uwa jini d'aya. Har cikin falon suka Shiga anata gaisawa da 'yan uwa da abokan arzik'i, bakin anguna yak'i rufuwa hakama su ya sulaiman suna cikeda farin cikin yau k'annensu sunyi aure. Tunda sukashigo falon bobo yaketa baza ido domin hango Nusfulhayat d'insa, rabonsa da ganinta tun jiya bayan sun dawo daga faty. Ganin duk d'unbin taron Matan falon bai Gantaba har sama dasuka haura aka gaisa dasu ammi nanma bata nan baimaga Matan yayyensaba ko d'aya. Sakkowa yayi yabarosu a can, wayarsa yaciro a aljihu yafara kiran number ta amma bata d'aukaba, yana nan tsaye yanad'an waige waige saiga Nasiba zata shige

Table of Contents

Chapters

83 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});