Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 2

Chapter 2

Abdulmalik Bobo Book 1 Complete Hausa Novel 1,192 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

zuwa cikin gida, kansa yagirgiza yana fad'in ALLAH ya shiryeki baby. (nace amin). Bayan yakashe motar yakwashi wayoyinsa shima yay ciki. Ammi dake zaune Nawal nakusada ita ta kwa6e fuska zatayi kuka, ta amsama bobo sallamarsa. Yak'araso cikin falon yana kallon Nawal, kekuma lfy daga dawowarmu?. Ammi tasauke ajiyar zuciya ta ce, " maganar kullumce dai takawo rigimar. Shiru yayi baice komaiba. Ammi takalli Nawal dahar tafara hawaye ta ce, "haba tagidan Appa kiyi hak'uri insha ALLAHU kinkusa ganin momynki kinji. Da sauri bobo yad'ago yana kallon ammi, k'irjinsa sai harbawa yake da k'arfi, yakasa cewa komai. Ammi takauda kai, ranta a6ace ta ce, " nagaji da ganin kukan yarinyarnan wlhy, amma babu komai bari Appanku yadawo, zand'auki mataki. Hannun Nawal takama suka haura sama. Bobo tamkar zai fasa ihu haka yakeji, yarintse idanu zuciyarsa na zafi, afili ya ce, "baby miyasa kikeson sakani a matsalane?. Ganin babu maibashi amsa yamik'e yanufi d'akinsa. *_Wanene Bobo_* Abdulmalik d'ane ga Alh Aliyu Abdulmalik Hamshak'i. d'an siyasa sananne wad'anda suke gwagwar Maya da ilimi dakuma nemawa talakawa 'yancinsu, matarsa d'aya Haj. Zahura (Ammi). Yaransu shidda maza hud'u mata biyu. Is'haq shine babba, yanada mata d'aya da yara hud'u, sai Sulaiman, shima yaransa uku da mata d'aya, sai Hamza matarsa d'aya shima da yara biyu, sai Abdulmalik (matarsa ta rasu) yarinyarsa d'aya, sai 'yan biyu duk mata basuyi aureba. ALLAH ya azurta Alh Aliyu Hamshak'i da yara maza masu kwazo da himma, yaa is'haq ma'aikacine na banki, yaa Sulaiman kuwa likitane, sai yaa hamza lecture, sai Abdulmalik (bobo) cikakken lauya mai zaman kansa. Kansu ahad'e yake, idan kagansu saika d'auka abokaine musamman ma yaa hamza da Abdulmalik, komai zasuyi saida shawarar junansu. *_Abdulmalik_* Mutumne mai zafi da sauk'i, gaba d'aya 'yan uwansa yafisu fad'a, saidai zasuzo daidai da ya is'haq (Dan shima mafad'acine). Abdulmalik mutumne dabayason raini ko kad'an, baya wasa da mutane, baizama dolema kuzauna har kurabu kaga dariyarsaba, kullum cikin d'aurewa yake, amma yanada son jama'a sosai. Abdulmalik bobo, yasamo sunan bobone tun yana k'arami, kasancewarsa mayen shan Bobo sai 'yan uwansa suke kiransa da bobo, ahankali sunan yay tasiri kowa Yakoma cemasa bobo, bayan ya girma saiya zama bobo na gsky saboda gayunsa ga k'yau ga kud'i ga ilimi, komaidai zam zam. Bayan ya kammala karatunsa yafara aiki iyayesu sukace saura aure. Yay tsalle yadire bashida budurwa, wannan yasa Appa yanema masa auren d'iyar k'anwar Ammi mai suna Ni'ima. Da farko baya sonta ko kad'an, amma k'yawawan hali irin na Ni'ima yajanye hankalinsa harya tsunduma a k'aunarta. Shekararsu biyu da aure ta haihu mace, wadda taci sunan Ammi, suna kiranta Nawal, shekarar Nawal d'aya Ni'ima takuma samun ciki, amma wajen haihuwa ALLAH yay mata rasuwa itada abinda ke cikinta. Bobo yashiga rud'ani Dan saida aka had'a da addu'a sannan yadawo daidai. Tundaga nan baisake kallon wata mace da sunan so ba, damashi matan bawani damunsa sukaiba. Bobo yanada k'yau daidai gwargwado, gashi d'an gayu, akwai tsafta da iya d'aukar wanka, dolene mace mai lfy taga bobo ta k'yasa, kullum cikin k'amshi yake. Shiyyasa Madeena ta k'yasa. (To aunty bily dai ta ce, "ki kama kanki Dan bama kulaki zaiyiba, danshi aharkar mata ba gwani bane😜). Shekarar Ni'ima 5 kenan da rasuwa amma bobo yak'i k'ara aure, iyayen sunata fama dashi amma yak'i sunata fama saidai yace zaiyi amma yak'iyi. Kullum zancen Nawal akaita gurin momynta, haka take damunsu Ammi da Appa hardashi dadyn Nata, itadai tanaso taga momynta, kullum zancen kenan. Abin yana damun yayyensa da iyayensa, shikam ko'a kwalar rigarsa, harkar gabansa kawai yakeyi. Wannan kenan. *_Mundawo labari_*......... *_{Aunty bilyn Abdul na gaisheku masoya😘😍.}_* [11/12, 2:10 PM] mrs bilkisu: πŸ‘©πŸ»β€πŸ’» ❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣ _{Bobo}_ _Story & editin_ *_Aunty Bilyn Abdul_* ✍🏿 _Written_ *_Marak'isiyya_* _hak'in mallaka_ *_Aunty Bilyn Abdul_* _sadaukarwa_ *_Abba Gana_* *_Batul mamman_* *_Bily giro_* 5⃣&6⃣ ........Safna tadanna hon afusace, da sauri maigadinsu yazo yabud'e mata get, ta danna hancin motarta cikin gidan, tana kashe motar tasuri jakarta da wayoyinta zuwa cikin gida. Wani wawan tsaki tasaki Dan ganin Rahma k'anwarsu kwance akan cinyar ummi. Daga Ummi har Rahma baki suka saki suna kallonta. Ummi ta ce, "kekuma lfy daga shigiwa zakiyi mana tsaki?, wai Safna ban hanaki halinnanba ne?. Baki ta turo gaba tana Harar Rahma, haba Ummi ALLAH wannan abun kunyane, wannan k'atuwar yarinyar shrkara 17 haryanzu bataida halin yaraba, aiiko jafar d'in ya Shaheed baya wannan ta6arar. Rahma ta girgiza kai danjin akanta yayar tata take tada jijiyar wuya, tarasa miyasa basa shan inuwa d'aya da 'Yar uwarta, (ita aganinta abin yafara wuce fad'an sako da sako), afili kuma sai ta ce, " aunty Safna miyayi zafi shiba wutaba, zauna ki huta Dan ALLAH....... Duka takaima Rahma ummi ta kare, Safna kishiga hankalinki danifa, uwarmi tamiki daga shigowa?. Cikin huci ta ce, "ummi kinajinfa maganar datake fad'amin, ALLAH yarinyarnan ta rainani, zan koya miki hankali kwanannan wlhy. Ummi ta tamke fuska tana nunama safna hanya, kinga tashimin anan. Ran safna a6ace tabar wajen tanufi d'akinsu tana mita. Rahma kam ta sauke ajiyar zuciya tana k'ara gyara kwanciyarta. Ummi ma kai ta girgiza ALLAH ya shiryaki Safna tafad'a tana shafa kan Rahma. Safna tacire kayanta tanata masifa harta shiga wanka, (nikam mamaki take bani, Dan banga abin fad'aba anan). Rahma tanason shiga d'akinsu tayi wanka tana tsoron masifar Safna, Dan tasan wlhy bata bartaba, k'ilama yau kwana zatayi bala inta da mitar tsiyarta. d'akin umminsu tanufa dantayi wankanta kawai, yafi sauk'i. +++++++++++++++ Bobo yana kwance ad'akinsa sai juye2 yakeyi, barci yakesonyi amma yak'i d'aukarsa, maganar Ammi ce kemasa yawo akwakwalwa. Yasan Ammi sairai babu sauk'ice, indai Abu ya6ata mata rai saita d'auki mataki, shikam yana tsoron zancennan yaje kunnen Appansu, yad'an cije le6e yana sauke numfashi, tund'azu soyake yafita amma yana shakkar had'uwa da Appa. Yasan fita tazame masa tilas Dan dole zasu had'u wajen cin abinci....... Bai rufe bakiba aka buga k'ofar, batarda ya d'agoba ya ce, "ashigo. Khairiyyace k'anwarsa, cikeda da tsoro ta ce, " yaya kazo wai aci abinci. Hannu yad'aga mata kawai, bata gane nufinsaba Dan haka ta ce, "ka k'oshi kuma yaa Bobo!?. Harara ya watso mata sannan yamik'e, da sauri tayi waje, shikuma yad'auki doguwar riga fara yazura yafito. Kowa ya hallara shikad'ai ake jira, rissinawa yayi yagaida Appa da Ammi sannan yazauna. Khursiyya ta ce, " yaya ina yini, harara ya watsa mata, ya ce, "k d'azu dasafe miya hanaki wankemin bayi?. Kanta ak'asa ta ce, " wlhy yaya ina uzirin makarantane, dakuma nadawo na manta. Tsaki yaja kawai baisake cewa komaiva. Ammi tazubama Appa abinci, tasakama kanta, kairiyya kuma tasakama bobo shima, suma suka zuba. Nawal tana kusada Appa. Suna cikin cin abinci kamar antsikari Nawal ta ce, "aunty khursiyya. Na'am Nawal miya faru?, khursiyya ta fad'a. Cike da murna ta ce, " Ammi tace nima ankusa kawomin momyna. Ayya my dear natayaki murna. Ran bobo yak'ara 6aci, fuska ad'aure ya gallama Nawal harara, Appa da Ammi suna kallonsa, amma basuce komaiba. Itama Nawal saitayi shiru kafin ya bibbigeta, Dan dukda yana wasa da ita hakan bai hana yaci k'aniyartaba idan ta k'uleshi. Harsuka kammala cin abinci babu Wanda yakuma cewa komai, bayan sun kammala kowa yakama gabansa. Bobo yaji dad'i Affa baimasa maganaba har dare. Da daddare yana zaune a babban falo daga can gefe, wasu buks yake dubawa, khairiyya

Table of Contents

Chapters

83 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});