Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 22

Chapter 22

Abdulmalik Bobo Book 1 Complete Hausa Novel 1,198 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ta jinjina kai kamar wata k'adan garuwa. Shikam yajuya yafice da Nawal ahannu. Itama fitowa tayi tahad'ama kowa abinci agabansa, hankalinsa kwance yakecin abinci shida d'iyarsa, amma Rahma duk atakure take, haka kullum take cin abin ci atakure, bakuma danwai bata saba da ahakan bane, saidai kawai nauyinsa datakeji, tunda agidansu gaba d'aya suke had'uwa suci abinci tuntana yarinya. Tananan tana juya cokali haryagama shida Nawal, yad'auketa suka koma falo suna jiranta. Ganin yatashi yasata sakin jiki taci abincinta sannan takwashe kayan taje ta d'auraye. d'aki takoma tacanja shigarta cikin wani had'ad'd'en doguwar rigar shadda pink colour, kayan sunmata k'yau sosai, tasaka k'aton farin hijjabinta sannan tafito, babu kowa afalon, danhaka takashe komai na kayan wuta, gamawata keda wahala yafito shida Nawal daga d'akinsa, hannunsa rik'eda jakar aikinsa. Kallo d'aya yaymata yad'aukekai, saidai har azuciyarsa yaji dad'in hijjabin data saka, yanason kamilar mace arayuwarsa, gaba yay suka bishi abaya. Tashaya kulle k'ofar falon shikuma sukai gaba cikin mota shida Nawal. Ganin Nawal abaya itama tabud'e bayan zata shiga, ahankali yay maganar tamkar mai ciwon baki. "Halan ni direban kine?." Cak tatsaya tafasa bud'ewa, kuma tak'i dawowa gaban. Yakuma cewa kina 6atamin lokacifa, kuma wajen aiki zanje, jiki a sanyaye tabud'e gaban tashiga, shima baisake cewa komaiba yatada motar suka fice bayan sun gaisa da baba mai gadi. Karatun Alkur'ani yasaka musu, cikin k'ira'ar shiek Abdurraham sudes, ahankali Rahma kebin karatun, yana kallonta ta gefen idonsa, jiyay tak'ara girma a idonsa. Har sukaje gidan Appa babu Wanda yay magana, garama Nawal takanyi jefi2. Saida yatsaya suka gaisa da baba mai gadi, yaymasa alkairi kamar yanda ya saba sannan yashige ciki. Yana faka motar Nawal tafice da gudu zuwa cikin gidan, sukuma suka fito cikin nutsuwa, da gudu khairiyya da khursiyya suka fito, rungume Rahma sukayi suna farin cikin ganinta. Ta ce, "aini nayi fushi, daga zuwa d'aya baku sakeba. Kiyi hak'uri auntyn mu, Ammi ce ta ce, " mubari sai nan gaba. Bobo yak'araso yana harararsu to maganannu ai kwabari kushiga gida dai ko?, yay gaba abinsa. Khursiyya ta ta6e Baki, aifa yau munga banu jarabatu yazo, ALLAH yasa aiki zai wuce cewar Khairiyya. Rahma najinsu dai tayi murmushi kawai. Cikin gidan suka shiga, hakan tayi daidai da sakkowar Ammi daga saman Appa, Dan Nawal nazuwa canta haura. Ta rungume Rahma tanamai jin dad'in ganinta, cike da kunya Rahma ta rissina ta gaida Ammi, ta amsa cikeda fara'a, da tambayarta ya zaman babudai wata Marsala ko?. Kan Rahma ak'asa ta ce, "Ammi babu matsalar komai, to Alhmdllh d'iyata haka nakeson ji. A'a mukarram d'ina lfy dai ko?, Ammi tafad'a tana kallon bobo dayay tsaye yana kallonsu tun d'azun. yaturo baki gaba kamar wani yaro, yo Ammi sai yanzu kika san dani?. Ammi taje takama hannunsa, o ni na isa namanta da babana, kawai ina murnar ganin d'iyatane. Yakuma turo Baki, Toni bari nakoma tunda bak'ya murnar ganina, yanda yay maganar ashagwa6e yasa su khairiyya kwashewa da dariya. Harara ya watsa musu suka bar wajen, itadai Rahma murmushi takeyi da mamakin Bobo, irin wannan shagwa6a haka kamar wani d'an shekara 5, anace mata tanada shagwa6a toga Wanda yatakata iyawa. Ammi ta lallashesa suka haye sama domin gaida Appa. Appa yaji dad'in ganinsu sosai, Dan haka yaymusu nasiha sosai sannan bobo yamik'e yaymusu sallama Dan wucewa aiki, saikuma antaso. Yakalli Rahma k'asa k'asa ya ce, "saina dawo. Kanta ak'asa ta ce, " ALLAH yatsare yabada sa'a. Yaji dad'in addu'arta Dan dama ita yake son ji. Ammi taji dad'in addu'ar da Rahma taima bobo, hakama Appa, suma sukai masa yatafi. Zuwa 10:30 gidan yagama cika, aunty Rasheeda da 'yayanta, aunty Sameera ma da NATA, aunty ummy ma haka, mazan kuma suna ajiyesu suka wuce wajen aikinsu. Dan danan gidan ya haukace da hayaniya, yaran duk suna falon sama wajen Appa, sukuma iyayen suna falon k'asa sunashan hira kamar wasu k'awaye, babu wannan shegiyar ak'idar ta kishin Sauri, hirarsu suke sosai, Dan danan Rahma tasaki jikinta dansu, su aunty Rasheeda akwai saurin shiga rai, gasu khursiyya iyayen shafta............ *_luv u oll my fan's_* *_(((S))).........2017_* [11/12, 2:25 PM] mrs bilkisu: 👩🏻‍💻typing........ ❣ *_ABDUL-MALEEK_*❣ _•{BoBo}•_ *_NA_* _*Bilyn Abdul*_ _sadaukarwa_ *_Abba Gana_* *_Batul mamman_* *_Billy giro_* *_wannan shafin nakune sister's, Raheenat Mamoudou, billy ladan, Asmy b Aliyu, Aysha Umar Abubakar, Alkairin ALLAH yakai muku aduk inda kuke, ALLAH yabarmana zuminci._* Luv u dayawa dayawa❤⛹🏻‍♀😂. 3⃣7⃣=3⃣8⃣ Safna da k'awayenta ne tafe, daka gansu kasan agajiye suke, fitowarsu kenan daga lectures. Zeenat tasauke numfashi tana fad'in wayyoni ALLAH na yaukam munji jiki wlhy, hummm kema kike fad'a wani naji, cewar Baseera. Safna dai batace komaiba, saima tsirama wani guri ido datayi, baseera ta zungureta Safna yadai?, mikike kallo hakane?. Ajiyar zuciya ta sauke tareda kallon Zeenat, Zee Dan ALLAH kalli Sir Hamza sosai, baya miki kama da Bobo?. Zeenat takalli ya Hamza dake k'ok'arin bud'e motarsa da takardu ahannunsa, Zeenat ta ce, "wlhy safna saifa yau nakula sosai, towaima miyasa bakita6a tambayarsaba?, tunda naga awajensa muka fara ganin Bobo. Baseera ta ce, " kumafa hakane, ALLAH baita6a kawo mana wannan tunaninba. Kunga dawannan surutun kumuje gunsa karya tafi to, cewar Safna. Assalamu alaikum. Wa'alaikummussalam, ya Hamza dake k'ok'arin shiga mota ya amsa tareda juyowa. Gaidashi sukayi, ya amsa yana nazarinsu suduka. Baseera mai ido atsakar ka ta ce, "sir Dan ALLAH munzo tambayar wanine agurinka?. Tofa ALLAH yasa nasani. Insha ALLAHU kasani, Dan ALLAH sir waye Bobo?. Wani d'an murmushi ya Hamza yayi, ya ce, " miyasa kuke son sanin waye shi?. Zeenat ta ce, "wlhy sir babu komai sai alkairi. Motarsa yabud'e yashige, azatonsuma bazasu sami amsaba, amma bayan yazauna saiya kallesu, ya ce, " Bobo kanina ne uwa d'aya uba d'aya. Wata sassanyar ajiyar zuciya Safna tasauke, jitake tamkar ansakata a aljanna, muryarta na Rawa ta ce, "sir Dan ALLAH kataimakamin da number sa mana. Yay d'an Jimm sannan ya ce, " tom kid'anban zuwa Monday zan nemi izininsa tukunna, idan ya amince saina baki. Dukda ba haka tasoba amma taji dad'i sosai, ta ce, "ngd sir ALLAH yakaimu lafiya. Amin yafad'a yana rufe motarsa, sallama yamusu yabar wajen. Safna ta ce, " guys insha ALLAH matsalata takusa k'arewa. ALLAH yasa cewar Baseera da Zeenat. .*.*.*.*.*.*.*.*.*.*. Fitowarsa kenan daga wata shari'a, hannunsa d'auke da takardu da hularsa, sai kuma d'ayan hannun ya sak'alo k'atuwar rigarsu ta lauyoyi, ya k'arasa Inda Br Nazeefi yake sukayi musabaha, dashi suka kara yau, shi yana kare mai k'ara, Bobo kuma mai laifi, yanda suka gaisa cikin girmama juna da sakin fuska bazakace sune yanzu suka d'auki zafiba akotu ba. Wayar bobo tafara ruri, hannu yasa cikin aljihun wandon jins d'insa ya d'aukko, Br Nazeefi yaymasa sallama, shikuma yafar'a k'ok'arin kiran Ammar Dan wayar ta katse. Bayan sun gaisa dad'an tsokanar junansu, Ammar ya ce, "nakirakane na gumtsa maka labari, tund'azun nake Neman wayarka akashe. Eh wlhy muna shari'ane, wane labari kasamo mana my Guy?, nasanka baka labarin banza. Ammar yay dariya, mutuminkane yazo wajena d'azu a haukace. Mutumina kuma wakenan?. Alh Sunusi dala mana, ahargitse yazomin yanason Sanin Inda d'ansa yake, nikam namasa kwatance, bayan kamar awa d'aya saigashi yadawomin da kud'i wainasa asakar NASA d'ansa, Dan yasan kud'i nake buk'ata. Na ce, " masa karya damu zuwa Monday zamukaisa kotu. Hankali tashe ya ce, "wai akan mima aka kama masa d'a?.

Table of Contents

Chapters

83 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});