Chapter 96
Chapter 96
da Sa'ud akan su taimaka su rakata ta dubo jikin bloody dinta da farko qi sukayi Saida sukaga yanda hankalinta ya tashi sannan suka yarda sunayin parking ta bude murfin ta nufi dakin da yake da sauri cikin saa kuwa babu kowa ta tsaya ta zuba masa ido yanda duk aka daure masa qirjinsa da na'urori shine yafi komai daga mata hankali gashi kwance kamar gawa sai idanunsa da suke motsi kawai yana ganinta ya fara qoqarin miqewa tayi saurin matsawa jikinsa ta dora kanta a saitin fuskarsa ta qanqameshi ta saki kuka a haka su Sa'ud suka shigo suka tarar dasu tana kuka shi kuwa bama zai iya kukan ba sai zafin zuciya kawai daqyar ya motsa bakinsa yace. “Shi..shikenan na rasaki Umaimah na roqeki kada ki manta dani a addu'ar ki idan bazan taba yafewa duk wanda ya rabani dakeba Umaimah nasani kema saboda babu yanda zakiyi ne zaki auri wani amma ki riqe kuma kisa a ranki watarana zaki dawo gareni Umaimah don Allah idan kinje kada ki bari ya tabamin ke idan na tuna abinnan zuciyata neman tarwatsewa take bansan meyasa naqi mutuwa ba....” Rufe masa baki tayi tana girgiza masa kai tace “bazaka mutu ba Hameed zaka miqe kaci gaba da rayuwa kayi hqr haka Allah ya tsara mana...” ji tayi an janyeta tana juyowa taga Sulaiman ne suka shigo da mahaifinsa da Daddy kuka ta saka me sauti ta fada jikinsa ta qanqameshi tana kuka tace “kayi hqr dani a yanda nake D.S wlh inason sabawa zuciyata dakai amma na kas..." Rufe mata baki yayi yayi murmushi me ciwo yace “kiyi hqr ki daina kukannan banaso inasonki zanyi hqr dake a duk yanda kika zomin kuma zan riqeki amana da zuciya daya nayi alqawarin saina goge miki duk wani namiji dake zuciyarki nazama nikadai ne nake mulkinta" Yana fadin haka yaja hanunta suka fice ya sata a motarsa Saudat Alfah da Sa'ud suka biyosu ya zage sai goge mata hawaye yakeyi duk da yanda yakejin kishinta a ransa amma ya kasa nuna Mata saboda yasan nunawar qarin shigarta damuwa ne Sa'ud ce ta leqo tace “ango kabamu aron amaryar taka yamma tayi kwalliya zamu" kallonta yayi yace “kuyi gaba zamu biyoku" hakan kuwa akayi shine yakaita har gurin kwalliyar Saida ya shigar da ita har ciki ya sumbaci hanunta yace “ki kulamin da kanki iya yau na baki amanar kanki daga gobene" Qasa tayi da kanta tana murmushi yayi murmushi yace “yanzu hankalina ya kwanta matata tayimin murmushinta me tsada" juyawa yayi ya fita yana daga Mata hannu ta bishi da kallo tana masa murmushi shima yanayi mata kiss ya jefo mata ta kumayin dariya har haqoranta suka bayyana. Hakanan akayi musu kwalliyar suka fito suka tafi gda suna zuwa gda motocin daukar amare sukazo 6:30pm suka isa gurin dinner ba tare suka taho ba amma tare suka shiga anatayi musu tafi da ihu suka isa gurin da aka tanada dominsu suka zauna daqyar yasata ta tashi suka shiga filin rawar lkcn da M.C din ya kirasu suka dan taka kadan kai ranar Umaimah taga rashin kunya a gure D.S ko kunyar mahaifiyarsa bayaji da Hajiya da suke gurin kamota yakeyi tako ina suna hotuna itadai hawaye kawai takeyi da ta rasa na meye farin ciki ko baqin ciki basu tashi ba sai sha biyu suna zuwa gda wanka kawai tayi ta kwanta tana kwanciya D.S ya kirata yana fada mata wai yau bazai iya bacci ba duk ta tayar masa da hankali ji yake kamar ya janyo gobe itadai murmushi kawai tayi masa sukaci gaba da hirarsu waishi ya matsu yaji abinda akeji. Washe gari qarfe goma daidai na safe aka daura auran Dr Sulaiman kabir Yola da Umaimah Ahmad Hameed Shuwa farin ciki gurin Sulaiman baa cewa komai ita kuwa da aka sanar da ita an daura auran kamar yanda Hameed ya suma haka itama ta yanke jiki ta fadi hankalin gdan biki ba qaramin tashi yayi ba shidai Daddy baa gama bikin dashi ba ya dauki dansa suka wucce India ita kuwa amarya Umaimah lbr yana zuwarwa Sulaiman babu kunya ya shigo cikin gdan har dakinta ya shiga ya kuwa yi saa babu kowa ya mayar da qofar ya kulle ta bude idonta a hankali da suka kumbura saboda kuka zama yayi a kusa da ita ya dagota jikinsa yace “ni bantaba ganin aure irin namu ba sweet Ina cikin farin ciki ke kina baqin ciki yakamata ki yarda da qaddara ba duka abinda zuciya takeso take samu ba ki qaddara dama Hameed ba shine mijin da zaki qarasa rayuwa dashi ba wlh Umaimah inasonki kuma zanyi miki komai donki yarda da hakan babu saki a tsarin aurena dake aurene na mutu ka raba” *UMMUH HAIRAN CE...* ✍🏻 [2/1, 1:44 PM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *_GU_* Kuka takeyi sosai tana shigewa jikinsa shima yana qara matseta yanajin ninkin sonta da tausayinta ya yarda so halitta ne duk kyansa da kwarjininsa amma Umaimah kuka takeyi saboda an daura aurenta dashi wasu hawaye masu zaffi suka zubo masa suka diga a dokin wuyanta yace “kiyi hqr Sweet da zan iya halatta miki Hameed dana halatta miki shi saboda nasani shine burinki" saurin dago da kanta tayi tace “wlh ba hakanne yake sani kuka ba tunanin halin da yake ciki shine yafi dagamin hankali D.S aman jini fah yakeyi..." Rufe mata baki yayi da nasa ya lumshe idonsa a hankali yanajin wani farin ciki na mamayar zuciyarsa yau da Umaimansa zai kwana a hankali ya janye bakinsa daga nata yace “zamu hadu anjima kiyi hqr ki cire komai a ranki ki barwa Allah ikonsa zan tayaki da addu'a Allah ya sassauta miki son mijin daba naki ba kiso mijinki me qaunarki” murmushi yayi mata ya daga Mata hannu yace “mu hadu a matakin qarshe" ya juya ya fice da sauri batasan sanda tayi murmushi ba sanyi Halin Sulaiman yana burgeta a hankali ta daga hanunta tace “Allah ka cusamin son mijina Allah kabani ikon yimasa biyayya Allah kada ka jarabceni da jarabta irin ta gdan Uncle Hameed" Haka ta yini a kwance tana juyi Saudat Alfah da Sa'ud da Sarah sune suka zama amarorin bikin suna tausayin Umaimah suna tausayawa Sulaiman da irin rawar qafar da yakeyi akan Umaimah dashi aka zage akayi aikin shirya gdan bai iya barin masu decorations din su kadai ba abokansa sai tsiya sukeyi masa wai ba sabon ba wasu suna cewa dashi wai Allah yasa ba auran kisan wuta tayi dashi ba da haka har magrib tayi aunty Jameela Zarah da Hajiya da Hajiya Kaka sune suka sanyata a gaba suna yi mata nasiha akan ta riqe mijinta amana kada ta cutar dashi domin shi da zuciya daya yake sonta kuma ya yarda zai rayu da ita duk da kasancewarsa saurayi sannan yan'uwansa basu nuna mata wani hali na tur ba mahaifiyar mijinta kamar ta goyata tanata godewa Allah daya nuna mata lkcn auran dan nata sama da shekara talatin da uku amma ko zancen budurwa akayi masa sai ya kama fushi da mutane yau gashi shima yayi mata saidai fatan zaman lfy. Sosai Hajiya tayi mata nasiha me shiga jiki tare da fitowa ta fada mata bazata taba yafe mataba idan tayi qoqarin kashe aurenta saboda Hameed ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111