Chapter 67
Chapter 67
mata ba itama Hajiyan murmushin yaqe tayi mata ta koma ta zauna tana kallonta yanda idonta yake juyawa akan yarinyar duk da babu bakin mgn amma da ganin kallon da takewa yarinyar kasan nasone da farin ciki hadi kuma da tarin tausayi na da da mahaifi lumshe idonta tayi tare da daukan hanunta ta tallafo bayan yarinyar ta hadata da qirjinta wani bacci ya dauketa itama yarinyar numfashinta saida ya canza saboda jin dumin uwarta data yini tana kukan nema ko madara taqisha saidai zamzam da ake bata. Alhmdllh jikin Umaimah yana sauqi sosai amma fah shi Hameed abun baa cewa komai saboda ko motsa hanunsa baya iyawa komai saidai ayi masa da na'ura ga wani qarin tashin hankali penis dinsa data miqe tun ranar da abin ya faru bata kwanta ba tun Daddy yana ganin kamar sauqi zaizo har ya sallamawa ubangiji komai saboda baya hangen wani sauqi a ciwon Hameed. Kwanaki bakwai din a asibiti sukayita saboda dinkin Umaimah daya rikice sosai saida aka tsaya a kanta kana aka samu ya koma normal suka koma gda ranar da suka koma akayima yarinyar hakika raguna uku Daddy ya yanka mawa amaryarsa Shurafah da Sa yasa akayi sadaka duka a maqota ana fada musu haihuwar babu wanda yasan abinda ake ciki aikuwa a ranar akayita tururuwar zuwa tayasu murna saboda kowa sanin da yayi Umaimah matar Hameed ce saboda haka babu wanda yasan matsayin yarinya Shurafah sai su isu. Kayan da Daddy yayima Umaimah da Shurafah ya bawa kowa mamaki saboda babu wanda yayi tunanin yanda ya dauki zafin nan zai siyawa maijego da jaririyar ko pant, sai dare da mutane suka lafa Daddy yasa aka kira masa Umaimah gata ga Hajiya ga Aunty Zarah ga Aunty Jameelah ga Kaka duk a gurin Shurafah tana tsakaninsu sai yawo take tsakanin dangin uwa da uba Allah Sarki shima shege me asali dan gata ne gadone kawai bashi dashi yanda ake lelen yarinyar har kuka yakesa Umaimah tana nadama da danasanin abinda suka aikata da Uncle din nata musamman idan ta tuna halin da yanzu haka Hameed din yake ciki na rayuwa ko mutuwa. Daddy ne ya katse shirun ta hanyar bude taro da addu'a ya dubi Umaimah yace “Baby ba komai yasa na taraku ba sai akanki kinga dai abinda ya faru tsakaninki da dan'uwanki kuma kinga irin matsalolin da suka rinqa fullowa qarshe dai ga ribar abinda kuka aikata nan kun samarwa zuri'ar Alh Abdulhameed Yauri Shuwa babu yanda zamuyi daku a dan qaramin family dinnan namu tunda daga ke harshi babu wanda zamu kora amma dai kun sani bakuyiwa zuri'arku da yarku adalci ba musamman keda kike mace yakamata ki nuna kedin mace ce wacce take fatan samun zuri'ar da zatayi alfahari da ita amma qarshe sai kika bige kika lalace wajen biyewa namiji da son zuciyarki saboda rashin tunanin me gaba zata haifar todai yanzu ga abinda gari ya waya yanan Allah ya sani munyi iyakar qoqarinmu na ganin kun kasance iyaye ababan koyi ga yayanku amma hakan yaci tura Umaimah dagake har Hameed nawane babu wanda zanyiwa baki saboda haka nidai na yafe muku batamin din da kukayi bada haqqina ba" Dakatawa yayi yaja fasali kana ya dora da cewa “inayi muku fatan alkhairi a rayuwarku ta gaba sai Abu na biyu kamar yanda al'adata take kuma nayima yan uwanki Zarah da Jameelah lkcn da sukayi haihuwar fari to kema ga mukullin motar ki sannan ki zabi duk qasar da kikeso a duniya zan biya miki keda yarki kuje ku huta" Tunda ya fara mgnr take wani irin kuka me ban tausayi kukan nata ba qaramin tasiri yayi a zuciyar duk wani wanda yake zaune a gurin ba har saida Jameelah da Zarah suka tayata, Tsawa ya daka musu yace “banason shirme tanayi kunayi memakon ku rarrasheta sai ku qara turata ke mgn nakeyi miki ki fadamin qasar da kikeson zuwa nayi miki visa da passport zuwanan da sati biyu saboda saura 5 weeks hutu ya qare ki fara attend lectures" Cikin kuka da rawar murya tace “Saudia Daddy" dagowa dukkansu sukayi suka kalleta saboda basu taba tunanin wannan zabin ba sunyi tunanin zata zabi Turkey ne saboda duk wanda ya kwana ya tashi a zuri'ar yasan burin Umaimah bai wucce taje Istanbul ba amma sai gashi lkcn da damar tazo Mata ta zabi wata qasar daban. Kafin kowa yayi mgn Daddy yace “meyasa kika zabi Saudi Arabia Umaimah?" Cikin kuka ta bude baki tace. “Saboda na kusanci ubangiji na na ziyarci kabarin annabi na roqeshi ya roqamin gafarar ubangiji ya yafemin wannan kayan dana daukarwa kaina nasani Daddy na take sani na aikata zunubi mafi girma wanda laifi biyune a duniya yafishi nauyi a mizani shirka da giba Daddy hukuncin kisane akaina ta hanyar jefewa meyasa bazaka kaini a yankemin hukuncin ba nasan zanfi samun sauqi idan na mutu ta wannan hanyar Daddy wanne jin dadi ne ya ragewa rayuwata Daddy da nasan wannan qaddarar tana cikin abinda zai faru dani ta haihuwa ba aure wlh dana roqi Allah na mutu na huta Daddy meyasa Mama batayi barin cikina ba? Daddy me zancewa Shurafah ranar data girma ta tsinci wannan mugun tabon da rudin zuciya yasamu mukayiwa rayuwarta....." Rufe mata baki Jameelah tayi ta rungume yar uwar tata a jikinta tana kuka tana cewa “kidaina fadar haka Umaimah ki daina roqon ki mutu ke bamu da yawa a zuri'ar mu kuma tun ran gini tun ran zane Umaimah waman qaddarallahu haqqan qadarihi haka wannan mgnr take babu wanda ya isa ya canzata naku dakyau ma tunda kinsan uban yarki kuma ya karbi abarsa kuma yanasonta kuma yar dangi ce qarshen dai abin ace idan mgnr aure ta taso tunda mace ce to koda mutane a duniya ko babu indai muna raye kuma muna haihuwa Shurafah zata auru ko a tsakanin yayanmu....” Sake rungume Aunty Jameelah tayi tana wani kuka mecin zuciyar me imani itama Zarah kwantowa tayi a jikinta itama kukan takeyi tace “mu rufe mgnr nan tsakanin mu kada ta fita waje Umaimah don Allah koba Hameed ne uban Shurafah ba a qaramin family dinmu zamu karbeta mu riqeta saboda bamu da yawa muna buqatar yawaita a duniya abu daya ya rage Daddy kayi ka mayarwa da Umaimah da Hameed aurensu su riqe yarsu cikin aminci da kulawa" Saurin dagowa tayi ta kalli Aunty Zarah ta girgiza kai tace “na roqeku kubar mgnr nan koda son Uncle Hameed zai kasheni na hqr da aurensa har abada kada kayimin dole Daddy hakan zaisa na rinqa kallon kaina a matsayin marainiya mara gata kuma bazan taba farin ciki a rayuwata ba Daddy bazan boye maka ba na tsani Uncle Hameed...." Ba qaramin girgiza kowa kalmarta ta qarshe tayi ba amma babu wanda yayi qoqarin sake maimata mgnr saboda suna ganin kamar ciwon abinda ya farune yasata furta haka. Murmushi Daddy yayi yace “Shikenan Uwar masu gda tunda bakya raayin zama dashi babu meyi miki dole amma kinsan aure dolene akanki bada jimawa ba saboda haka zan baki shekara guda ki shayar da amaryarta ki fitar da miji kiyi aure sannan kamar yanda kika zaba zamu tafi Saudi dani dake da Hajiya sai Hameed da zamukai a dubashi acan saboda ciwonsa yafi qarfin asibitocinmu na nan sai kuma
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111