Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 68

Chapter 68

Gidan Uncle Return Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Yayarki Jameelah da idan kun gama umararku zaku wucce Turkey ki cika burinki na zuwa Istanbul kafin ki mutu" Dariya tayi me hade da kuka ta miqe cikin tafiyarta da bata koma Normal ba ta matsa kusa da Daddy tayi kissing hanunsa ta rungumeshi ta kuma fashewa da kuka tana jera masa dubun gdy murmushi yayi yace komai nayima uwata ba faduwa bane fatana dai karta qara irin kuskuren da tayi a baya" jinjina masa kai tayi ya rungumeta yace Allah yayi miki albarka yabaki miji na gari wanda zai riqemin ke amana" Amsawa kowa yayi da amin Daddy ya sake rufe taron da addu'a tare da yima yarinya Shurafah addu'ar shiriya da kariyar ubangiji kowa ya tashi ya nemi gurin kwanciya inda Daddy ya fice ya koma asibiti gurin Hameed. Koda suka koma daki Aunty Jameelah ce ta hauta da fada wai bata kyauta ba da tace ta tsani Hameed tanajinta tayi mata shiru taci gaba da feeding din yarta har saida taga ta qoshi ta canza mata Pampers ta kwantar da ita tare da kissing din jajayen lips dinta tace “sleep well my lovely daughter kiyi dreaming dina kinji” abin dariya yabawa Jameelah sosai tace “oh ni Jameelatu Umaimah da ya hauka ya qaru wannan ya zakiga hauka gurin uwarki" dariya tayi tace “Allah Aunty bansan haka iyaye sukeji ba sai ranar da Hameed ya tafi da yarinyar nan wlh hankalina gushewa yayi ban iya sanin komai da nayi ba saida aka bani labari Aunty wai dama haka kukeji akan yayanku tab aini wlh babu mai dukar min Shurafah gara ka bugeni daka bugarmin ita dan zan iya rufe idona na ci mutuncin uban kowa" Dariya sosai Aunty Jameelah da Aunty Zarah sukeyi Aunty Zarah tace “harda ubana ko?" Kunyace ta kamata don tama manta da Aunty Zarah a gurin ta kwanta tace “Allah aunty dan bakisan abinda nakeji bane" murmushi tayi tace “kafin kiji na rigaki ji Umaimah" da haka sukayi bacci. *UMMUH HAIRAN CE...✍🏻* [1/22, 4:45 PM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *GIDAN UNCLE* Ki biya kafin ki karanta idan kinaso ki kira number nan; 09031307566: *PAGE FOURTY ONE* Kwanaki bakwai tsakani Umaimah tayi shar da ita baby Shurafah tayi wayonta tayi qiba kalar fatarta kalar fatar iyayenta kamarta da mahaifinta ta fito sosai Daddy ya gama musu komai na tafiya qasar Saudia duk tsayin lkcn nan Umaimah bata taba zuwa ta duba Hameed ba kuma ko a baki bata taba tambayar ya jikinsa ba. Kwana biyu tsakani jirginsu ya daga qasar Saudi tun ranar da Daddy yace Hameed ya tafi da Shurafah rabon da ta sanyashi a idonta sai yau data hangeshi a zaune saman welchair kansa yayi gefe sai gyara masa kan yakeyi gefe ta koma ta zauna har lkcn tashinsu yayi suka shiga jirgin suka daga zuwa qasa me tsarki itadai bata cewa kowa komai game da Hameed din ba kowa yana jajanta jikin nasa amma banda ita da tayi qasa da kanta ta zubawa yarinyar ido wasu hawaye masu zafi sunabin kuncinta. Koda suka sauka a filin jirgin saman Saudi Arabia motar asibitin da akayima Hameed boorking ce tazo Daddy da Yusuf suka shiga Umaimah da Hajiya da Aunty Jameelah suka shiga ta masaukinsu suka tafi. Wani babban hotel ne kusa da harami anan suka sauka Hajiya dakinta daban Umaimah da Aunty Jameelah suna shiga dakin ta kwantar da Shurafah ta shige bathroom ta fara kukan da taketa qoqarin hadiyewa tunda suka taho koda wasa bata taba tunanin jikin Hameed din yayi zafi haka ba tausayinsa ya kara darsuwa a zuciyarta mutum lafiyayye me tashe quruciya da qarfi da mazantaka wai yau shine a kwance haka kamar gawa saidai a kwantar dashi a tayar. Lallai Allah ya cika me ikon yin komai a lkcn da yaso a hankali cikin kuka ta zube ta dora goshinta saman tiles din toilet din tace “Allah kaji qaina kabawa dan'uwana lfy Allah ka yafe masa zunubansa Allah kada ka kashe Uncle ka mayar min da Shurafah marainiya kamar ni Allah ka tausayawa bawanka me qoqarin tsayawa akan dokokin ka Allah na sani qaddara ce da sharrin shaidan tasa Hameed watsi da umarninka wannan jarabta tayi masa yawa da wanne zaiji" Ta jima a bathroom din sannan ta fito ta zauna kusa da Shurafah ta daukota ta sanya mata nono ta kuma fashewa da kuka Aunty Jameelah ta dubeta da sauri tace “mene kuma na kuka Baby?" Dagowa tayi tace “Aunty kinga Hameed fah yanda ya koma aunty anya Hameed zai koma normal kamar da?" Harara ta zabga mata tace “to meye damuwarki da komawarsa kamar da Umaimah na dauka ko babu komai tsakaninki da Hameed yafi qarfin wannan wulaqancin daga gareki Umaimah me Hameed yayi miki da zafi haka da zaki kwana ki tashi ki kasa tambayar iyayensa jikinsa kina ganin hakan daidaine a gurinki Umaimah kina tunanin Daddy da Hajiya basajin zafi da ciwon ko in kula din da kike nunawa dansu gudan jininsu akan laifin daba tursasa ki yayi ba kece kikaba da qofar da hakan ta faru Umaimah ko kina tunanin Daddy da Hajiya zasu soki fiye da son da sukewa dansu na cikinsu? Amsar itace aa Umaimah qaramin misali yanzu ki duba ki gani shekara nawa kikayi kina wahala da Nihal da Maliha kwana nawa kikayi da haihuwar Shurafah amma soyayyar Shurafah ta disashe hasken soyayyar da kika dauki shekaru kina nunawa Nihal da Maliha saboda itadin jininki ce da wani bangare na jikinki aka halicceta balle su da suka dauki shekara sama da talatin da biyar da dansu wacce soyayya zasu nuna miki data dara ta dansu? Ki fadamin ita Umaimah" Ta qarashe mgnr tana matsawa kusa da yar uwar tata ta kamo hanunta tace “amma saboda tsabar rashin kunya da tsageranci da cin fuska kika iya duban tsabar idonsu kika iya furta musu bazaki qara zaman aure da dansu ba kuma kin tsaneshi hmn yarinya kiyi gaggawar sake tunaninki wlh mutanen nan basu cancanci wannan sakayyar daga gareki ba Umaimah kinsani Hameed yana sonki bazai iya rayuwa babu keba kamar yanda yasha fadamin, ko kinsan yasha zuwa ya fadamin irin wulaqancin da kikeyi masa da tsanar da kike nuna masa Umaimah Hameed yasha zuwa har Damaturu yasani a gaba ya rinqa yimin kuka yana fadamin zuciyarsa zafi take masa a duk lkcn da yaso ganinki ko yaso jin muryarki yazo gdan kikaqi yarda ku hadu ko ya kiraki a waya kikaqi amsawa Umaimah ko kinsan Hameed yasha fadamin sonki shine zai kasheshi ko kinsan a ranar da abin ya faru yana fitowa daga gdan Daddy ya daga waya ya kirani yake fadamin zuciyarsa fashewa zatayi Ina bashi hqr naji ya saki wata qara tare da kiran sunanki shikenan har yau tsayin sati biyu da kwanaki uku baisan kansa ba".... Ajiyar zuciya ta kumayi kana ta dora da cewa “bakiyi kuka ba Umaimah sai ranar da kika daura aure da wani ba Hameed ba aka kaiki gdansa dare yayi ya shigo yayi mu'amalar aure dake minti biyu ya sauka ya bingire ya fara bacci bai farka ya sake nemanki ba saida safe ki nemeshi yace kin cika karuwanci da takura shi ya gaji to a sannan ne zaki fara kukan nadamar gujewa namiji daya tamkar da dubu namijin da mace da yawa take

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});