Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 81

Chapter 81

Gidan Uncle Return Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

miki" Kama hanunsa tayi ta miqe zaune ta dubi agogo cikin qarfin halinta tace “kwana biyu kenan da nake fama da zazzabin kawai daurewa nakeyi qarfe nawa ne daurin auran naka ne" tsuke fuska yayi yace mata “ba wannan ne a gabana ba so nake naji meye yake damunki" ajiyar zuciya tayi ta lumshe idonta yayi murmushi ya dauki wayarsa ya kira Dr Saleem yace “gamunan zuwa da Hearty zaka dubamin ita Ina zargin kamar nayi ajiya fah" bai jira abinda zaice ba ya kashe wayar ya dauki hijjab dinta yasa mata suka fito daqyar tasha tea saboda tashin zuciyar da takeji yana riqe da hanun Shurafah da take koyon tafiya suna fita sukaci karo da Aunty Zarah da Sa'ud da Sarah sukayi tsalle suka rungume juna su ukun Aunty Zarah kam wani mugun kallo take watsawa Hameed saboda tafi kowa sanin halin ballagazancin matar dazai auro tace. “Aa ango ya naganka a gida unguwa tanacan ta dauki harami zaa daura auran Salamatu da Sallau sallamamme asararre" sosa kansa yayi ya dauke wata siririyar qwalla a idonsa yace “wlh ni nama manta saida bloody ta tunamin kuma sai naji jikinta da zafi shine zamuje a dubamin ita" sakin Sa'ud da Sarah tayi tace “kuyi hqr Ina zuwa yanzu aunty ku shiga ganinan" juyawa tayi tabi bayansa ya bude mata motar ta shiga shima ya shiga yaja suka fita a bakin get taga motar qawarta ta makaranta Saudat Alfah takuwa riqeshi tana dariya tace “Abu Shurafah kaga Saudat Alfah ma da nake bakalbr jiya itama tazo" kallonta yayi da rinannun idanunsa ya kawar dakai yace “yanzu saboda zanyi aurene ake taruwa haka a gdana Umaimah wadannan duk nasan zugamin ke zasuyi don Allah kada ki biye musu duk abinda zasu fada miki qaryace nine kawai zan fada miki gsky" jikinta ne yayi sanyi ta dago ta dubeshi tace “wai da gaske yau zaa daura maka aure da Salma Abu Shurafah?" *UMMUH HAIRAN CE...✍🏻* [1/28, 8:44 AM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *G.U* Dagowa yayi da sauri ya kalleta hawayen da yake qoqarin hadiyewa suka zubo masa yace “nima jin abin nake kamar tatsunniyar tsoffi bloody waini Hameed Adam Hameed Shuwa zaa sake daurawa aure da wata watanma wai Salma Umaimah wannan abin da ciwo Allah Kaine ka halliceni ka halicci Salma Allah indai da nufin cutar dani da matata jinina takeson shigowa gdana Allah kayimin maganinta Allah kafimu sanin abinda ke boye game da wannan masifaffen auren Allah ka kawomin dauki Allah idan na tuna da yau zaa dauramin aure da wannan baiwa taka Allah zuciyata zafi takeyi bloody ciwon zuciyata neman tashi yakeyi" Cikin kuka da baqin kishi da tausayin kanta ta daure daqyar bisa taimakon addu'ar da takeyi a zuciyarta tace “kayi hqr" iyakar kalmar data iya furta masa kenan yayi parking a asibitin ya kashe motar ya ruqo hanunta qamqam a cikin nasa jikinsa na wata irin rawa yace “a... akwai matsala Umaimah dauki wayata ki bude ki kiramin Dr Saleem Umaimah yi sauri zuciyata zata tarwats....” Yana fadin haka yana qara qanqameta qirjinsa yana bugawa da qarfi, cikin Kaduwa da tashin hankali ta lalubo number Dr Saleem din ta kirashi bugu daya ya daga ta kara a kunnenta yace “hello ango mijin amarya amma Umaimah nake nufi..." Da sauri ta katseshi da cewa “na shiga ukuna Dr bloody mutuwa zaiyi zuciyarsa ke masa ciwo..." a firgice yace “what? Umaimah kuna Ina?" Cikin kuka tace “muna cikin asibitinku ya kawoni a dubani kuma shima yace zuciyarsa tarwatsewa zatayi jikinsa sai rawa yakeyi" da sauri ya kashe wayar ya fito kafin yazo tuni Hameed ya gama fita daga hayyacinsa amma duk da haka tana maqale a jikinsa yaqi sakinta sai kuka takeyi tana jijjigashi tana danna masa masa qirjinsa saboda tasani tun tana qarama idan ciwonsa ya tashi haka takeyi masa. Qarasowar Dr ne yasata ta zare jikinta daga nasa daqyar daidai lkcn kuma wayarsa ta shiga ring batabi takan wayar ba sai taimakawa Dr Saleem data shigayi suka fitar dashi aka dorashi a kujerar tura marasa lfy suka nufi heart attack word da gudu takebin masu turashi din saboda suma gudun sukeyi suna shiga suka nufi emergency din word din suka kwantar dashi suka fara bashi taimakon gaggawa daqyar Dr Saleem ya lallabata sukaje itama ya dubata ya tabbatar mata tana da shigar cikin sati biyu da kwana biyu tayi farin ciki amma damuwar da take ciki ta danne farin cikin ta fitowa tayi ta zauna a reception tayi tagumi daidai lkcn Daddy ya shigo asibitin lkcn 11:30am yayi parking ya shiga word din da sauri hango Umaiman ne yasashi nufarta da sauri yace “mamana meye ya kawo tashin ciwon nan wlh ina kwance a gda Alh Jamilu ya kirani yake fadamin an taru gurin daurin aure shida zai karbi abinsa baizo ba so shine naketa kiran wayarsa najita a kashe na fito na nufo gdan naku don nasani yanda yake dumin wannan qaddararren auren lfy bazata hanashi fitowa ba Ina zuwa Zarah take sanar dani kun tafi asibiti so shine na Kira Dr yake fadamin ke ya raqo a dubaki saboda yana zargin kinada shigar ciki kuma sai ciwonsa ya tashi meye yayi dalilin hakan?" Miqewa tayi ta shige jikinsa ya rungumeta sosai ta saki wani marayan kuka tace “Daddy na tabbatar da bloody bayason Salma Daddy bayason auran Salma kuyi masa sauqi wlh qaddararmu ce Salma ni dashi Daddy ya sanar dani komai ya fadamin yanajin tsanar Salma a cikin jininsa amma kuma yakasa bijiirewa auran ta baya tunata idan baya tare da ita sai ta kirashi kota nemeshi kuma idan ta kirashi baya iya bijirewa umarninta Daddy ba fushi zakuyi da Bloody ba addu'arku yake buqata wlh Daddy baya cikin hayyacinsa kagafa yanzu kawai mgnrta nayi masa ciwonsa ya tashi wannan wacce irin masifa ce Daddy me Salma take nufi damu? Meyasa ta nace sai ta shigo cikinmu ta rusa mana farin cikinmu?” Ajiyar Daddy yayi me qarfi ya sanya hanunsa ya dagota ya fara share Mata hawayenta yace “akwai manufar wannan shedaniyar yarinyar akansa koma dai menene yau dai an daura aure Umaimah tun lkcn da Hameed yayi min mgnr auran yarinyar nan na nuna rashin amincewata amma naga ya dage nasan tabbas akwai matsala so nayi qoqarin tursasashi amma yaqi Umaimah an tsaface mini da an sanya masa ya daina jin tsorona dagani har mahaifiyarku yama daina zuwa inda muke saboda zamu fada masa gsky Hajiya tace jiya ta kirashi tace ya sakeki saboda bazaki zauna da muguwar yarinyar nan ba da Sunanta yayi tambari ta fitar da mace a gdanta kota hanyar saki kota haukata kota kashe abune me sauqi a gurinta amma yaqi yace tayi masa uzuri ku hakan bazai faru daku ba saboda kun fahimci juna kuma kin bashi hadin kai shine ta kumayi masa rantsuwa akan saiya sauwaqe miki bazai kasheki da baqin cikinsa a banza ba Umaimah bayan qiyayyar Salma da ciwon auranta dakecin zuciyarsa harda wadannan kalaman na Hajiyanku addu'a kawai ya kamata muyiwa Hameed saboda kansa na cikin tukunya baya cikin hayyacinsa nasa ma da sauqi saboda qarfin kariyar farko da kuka samu daga kakanku musamman ke da kike mace da abin sai yaci uban haka ki qara hqr Umaimah mijinki yana sonki da izinin Allah komai zaizo

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});