Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 94

Chapter 94

Gidan Uncle Return Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

kuma yaje ya dawo da ita ko mutum yaje yasha giya ko wani abu me gusar da hankali yazo ya nadawa matarsa duka ya saketa idan ya dawo hayyacinsa ya koma ya dawo da ita wannan abu ya batawa Sayyadina Umar (R.A) rai zamanin khalifancinsa ya kira majalissar sahabbai aka sakewa dokar qwasqwarima saboda sauyawar zamani aka buga mata guduma akan cewa idan har mutum ya saki matarsa saki uku a kalma daya to ta saku sannan ko cikin gushewar tunani mutum yayi saki to matarsa ta saku sannan idan kayiwa mace saki daya sannan kazo zaka sake sakinta bayan kasan da daya a baya kuma ka furta mata biyu to ya zama uku saboda haka ta haramta gareka harsai tayi aure da tsarkakkakiyar niyyah ba niyar kisan wutaba kuma harsai mijin yayi mu'amalar aure da ita sannan tasu ta hadosu suka rabo to a lkcn ne ta halatta gareka sai ku sake daura aure fresh me igiya uku. Wannan kalma ta sai Umaimah ta auri wani har ya kwanta da ita sannan zata halatta gareshi tana mugun dukan zuciyarsa yakanji dama ya mutu ya huta da ganin wannan baqar rana dalilin yasashi dawowa gdan dalilin ya qudurce a ransa bazaiyi aure ba itama bazatayi ba saidai su qare rayuwarsu a haka. Abu daya da yake cin zuciyarsa yanda Umaiman tayi watsi da duk wani abu daya shafeshi so tari idan bashine yayi mata mgn a gdan ba itadai bai isa ta daga kai ta kalleshi ba yana yawan kiran wayarta amma bata dagawa har layi ya canza musamman saboda ita amma daya kirata tana dagawa taji muryarsa tace “hello bloody ya akayi Allah yasa dai lfy?" Ajiyar zuciya yaja yace “ki taimaka ki fito come pound din gdannan inason ganinki don Allah" murmushi kawai tayi ta kashe wayarta bata fito ba kuma bata sake daga wayar tasa ba ransa yayi matuqar baci amma bashi da yanda zaiyi saboda baya iya fushi da lamarinta wani azabbaben so yakeyi mata wanda yake neman turashi lahira bai shirya ba haka lkc yayita tafiya tafi² har watanni takwas suka shude kullum cikin dagewa a karatunta take inda shi kuma Hameed ya mayar da azumin nafila abokinsa saboda lalurarsa tafi qarfin yace zai rinqayin na litinin da alhamis Hajiya tanajin dadin yanda Umaiman take tsarewa Hameed gida saboda tasan yanda yake rawar qafa akan duk abinda ya shafeta idan ta bashi fuska taasa zasu tafka ta lura basu zama inuwa daya daya shigo parlourn ita kuma zata tashi tabarshi da yayansa hudu Nihal Maliha Shurafah da Shuraif Maliha itace me wayo tunda a qallah yanzu ta doshi shekara takwas itace take cewa uban nasu “Uncle naga Aunty tana fushi dakai kuma kun dawo gdannan dukkanku kuma jiya naga wani yazo gurin Aunty ta fita suna hira har suna dariya" tashin hankali wata uwar zabura da yayi ya fara qwalawa Hajiya kira Hajiya ta fito daga kitchen tana cewa “waikai wanne irin mutum ne kaine diba nan duk yayanka ne amma kaqi hankali ubanme zaka bani kake dokamin kira haka?" Duban Hajiya yayi da idonsa da suka canza kala saboda bala'in yace “wato Hajiya yarinyar nan har kin barta ta fara kawo mana qartin banza gdannan ko to wlh bazai yuwu ba karyata zanyi na balla banza kuma naci uban duk wanda ya qara zuwa gdannan da sunan yazo gurinta haba Hajiya wannan ai cin fuska ne da wulaqanci ansan dai ina gdannan koma meke faruwa zanji baba megadi yasha fadamin yaga wani ya tuqota ya kawota gda ko yacemin yaga wani yazo gurinta to nida kashedi ne nayi muku wlh Allah hauka zanyi a gdannan ga duk wanda ya qara zuwa yayimin sallama da mata shima megadin bari naje wlh ya qara barin wani dan iskan ya shigo gdannan a bakin aikin sa” Yana gama fadamin haka ya fice fuuuu kamar zai kifa riqe haba Hajiya tayi tace “wata sabuwa inji dan caca to uwarka zatayi maka a gdan da zakace baza azo gurinta ba zakuwa kaci kan uwarka wlh Hameed dani kake zance kama godewa Allah Umaimah najin kunyarka ni bantaba ganin yarinya me yakanar Umaimah ba ko baqo tayi da zarar taga yamma tayi zata sallameshi idan nace meyasa tace babu komai bayan nasan saboda Kaine" Yana fita kuwa yayi katari Dr Sulaiman ya kawota daga mkrnta malaminsu ne tunda ya qyalla yaganta ya dauki so da kulawar duniya ya dora mata da farko Shuraif yakeja a jikinsa saidaga baya daya bincika yaji sun rabu da mijinta sannan ya fara fito mata da ainihin buqatarsa gareta da farko taqi sai daga baya Saudat ta rinqa tausarta tana fada mata shima kyakkyawa ne gashi fari gashi da gani babu tambaya naira ta zauna masa to daqyar dai ya samu ta saki jiki dashi suka fara gudanar da soyayyarsu amma qasan zuciyarta danqare dason dan'uwanta wanda bazata iya gogeshi a mind dinta ba don tasha kiran Dr Sulaiman da Hameed saidai yayi murmushi kawai yace “ sweet Allah yasa kisoni koda rabin son da kike yiwa Hameed ne sweet wlh inasonki fiye da tunaninki na fada miki bantaba soyayya ba saboda tsoron mata nakeji sai a kanki" To yauma zancen da yake mata kenan tayi dariya ta lakace masa hanci tace “sai kuma ka fara da bazawara me yara biyu....” dora hanunsa yayi a saman lips dinta ya kashe mata ido yace “banason ji idan yayanki goma inasonki kuma zan rayu dake zan baki soyayya madara kuma nasani nima zaki soni irin son da kikeyiwa abu Shurafah koma fiy...." Aslm alaikum sukaji anyi musu sallama gabanta yayi mugun faduwa da sauri Sulaiman ya dubeshi yayi murmushi tare da shafa sumarsa ta fullanin asali yace “amin wslm" ya miqa masa hanu amma sai ya noqe ya kalleta da jajayen idanunsa ka cafketa da qarfi yace “dama abinda kikeyi a makarantar kenan idan kinje irin wadannan yan iskan kike kulawa to karatun ma kin daina" yana fadin haka ya figeta ya cillata parlour ya juyo shidai Sulaiman yana tsaye cike da mamaki “dama wannan shine yayannata da take cewa dashi tanajin tsoron yazo gda kada yagansa?" Ya tambayi kansa kafin ya samo amsa yaji muryarsa yana cewa “kada ka qara biyomin qanwa gda wlh zan daureka harsai igiya tayi rara" wuccewa yayi Sulaiman yayi saurin binsa yace “kayi hqr Yaya wlh bada wasa nake ba auran Umaimah zanyi....” *UMMUH HAIRAN CE...*✍🏻 [1/31, 5:48 PM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *GU* Wani abune yaji ya caki zuciyarsa ya juyo da sauri yace “aure kuma wa zaka aura habadai wlh tun lkc be qure maka ba ka kama gabanka Umaimah ba matarka bace nayi mata miji" tsayawa Sulaiman yayi sororo har Hameed ya shige parlourn yana zuwa ya fara dukan dakin na Umaimah yana cewa “aure fah yace Umaimah aure? Wlh qarya yakeyi ya aureki" Daddy dake zaune ya miqe ya haye sama. Ita kuwa tanajinsa taqi budewa muryar Hajiya taji tanayi masa mgnr ya juya ya fara sababi yana cewa ai duk ke kika daure mata gindin tacimin mutunci harni wani zai tara yacemin wai auren matata zaiyi wlh bazai yuwu ba kasheni kukeso kuyi" Hajiya ce ta haushi da bala'in da yafi nasa dole yayi qus sai zafin zuciya da sharar hawaye da yakeyi. Tana zaune a dakin

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});