Chapter 22
Chapter 22
suna fita basu karya ba kawai saboda sakacin uwarsu kama hanun yaran yayi yace “kuyi hqr Auntynku batada lfy tana asibiti kuzo muje kuganta sai kuci abinci acan" murna suka hauyi da tsalle da kansa ya cire musu kayansu yasa musu wasu ya jasu suka fice daga gdan suna zuwa asibitin ya nuna musu dakin suka shiga da gudu lkcn an cirewa Umaimah roba ta biyu ta jinin tana zaune ta jingina da pillow da gudu suka nufeta suna murna suna tsalle itama taji dadin ganin yaran saboda ta saba dasu koya ta yini bata gansu ba sai taji babu dadi haurawa sukayi saman gadon suka rungumeta Maliha tasa kuka tace “Aunty shine jiya Uncle ya daukeki kika tafi kika barmu kikaqi dawowa kiyi mana break yau sai haka muka tafi bamu karya ba nayita kuka a makaranta inajin yunwa” Nihal ce me wayo tace “Aunty kin rame kinyi fark meye yake damunki aka kawoki asibiti?” murmushi tayi vta shafa kansu tace “banida lfy ne amma naji sauqi da ganinku kunajin yunwa ko?" Daga Mata kai sukayi tace “no wonder indai yarana sunajin yunwa Ina ganewa Hajiya dake zaune tana kallonsu tana murmushi tace “kaji yan jakar uba ina iyayen naku da suka barku da yunwa” kawar dakai Umaimah tayi tace “mudai ki bamu abinci yarana suci Hajiya idan sunci sayi miki bayani” Nihal ce tace “mu Mom dinmu bata sonmu yau ma duka tayi mana saboda mun tambayi ina Aunty” Daidai lkcn ya turo qofar ya shigo tare da sallama dago kanta tayi da sauri idonsu ya sarqe guri guda yanayi mata kallonsa me narkar da zuciya murmushi yayi mata tare da ajiye kayan daya dauko mata da shopping din da yayo yace “Hajiya sannu da qoqari yame jikin?" Ko kallonsa batayi ba bare yasa ran zata amsa masa abincin ta zubo jallop din shinkafa ce data wadatu da alayyahu da kifi banda sai qamshi takeyi ta miqawa Umaimah ta karba tare da zaunar da Maliha ta fara basu abincin a baki sunata zuba mata santi itadai batace musu komai ba saboda yanda takejin qwayar idonsa na yawo a jikinta muryar Hajiya ce ta katseta tace “idan kaga dama kaje Daddyn ku yana nemanka yanzun nan ya fita zashi gdanka” amsawa yayi da “to” ya miqe yace bari naje na biyasu kudinsu na dawo dakatar dashi Hajiya tayi tace “aa aikai ka gama aikinka saura namu ubanka ya biya komai" dagowa yayi da sauri ya kalleta yace “amma Hajiya..." Dakatar dashi tayi da cewa “karkace min komai Hameed wlh da zaka yarda ma daka daina zuwa inda nake saboda idan na ganka jinake kamar na kasheka” *UMMUH HAIRAN CE...✍🏻* *🅱RILLIANT WRITERS* *ASSOCIATION* 🖊 ( _Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers)_ *GIDAN UNCLE* ( _Love and romantic story_) *SHORT AND TRUE LIFE STORY* *MALLAKAR* 👇🏻 *FAUZIYYA TASI'U UMAR* *®FAUZAH* Wattpad👉🏻 realfauzah www.fauzahtasiu41@gmail.com Alhmdllh a madadina da iyalaina munayiwa daukacin al'ummar duniya barka da shiga sabuwar shekarar gogerioun calendar duk da dai mu munci wata hudu a tamu ta musulumci Allah ya hadamu da alkhairan cikinta sharrikan dake tattare da ita Allah ya kade manasu yanda muka shigeta lfy Allah yasa muga qarshenta lfy idan kuma bamu da rabon gani to Allah ya karbi ranmu muna cikin musulumci muna masu aikata ayyukan alkhairi sannan yasamu a ceton Muhammadur rasulullahi (S.A.W). *PAGE ELEVEN* A salube yake kallon Hajiya lallai ta dauki lamarin nan da zafi saboda tunda yake da ita ko baqar mgn bazai iya tuna ranar data fada masa ba amma yau gashi tana neman tsine masa, cikin rashin qarfin gwiwa ya matsa jikin gadon na Umaimah yace “sannu Babyn Uncle ya jikin yanzu inane yake miki ciwo?” ya fada yana dora hanunsa a saman kanta ajiyar zuciya sukayi a tare cikin sanyi muryarta tace “da sauqi” murmushi yayi yace “ok kuzo mu tafi kada ku dame Aunty kunga batada lfy ko?” Nihal ce tace “Mudai anan zamu zauna gurin Aunty da safe ta dafa mana tea tayi mana wanka" Maliha kam kuka tasa wai a dole bazata koma gurin uwarta ba. Daqyar ya shawo kan yaran suna kuka suna komai yajasu suka fice daga dakin itama Umaimah gawayen ta share batason ko kadan taji yaran suna kuka jinshi take har cikin lakarta, Hajiya kam haushine yakusa kasheta ita a tunaninta mgnr data fadawa Hameed dince tasa Umaimah kuka. Kwanansu daya a asibitin yazo da safe dazai tafi aiki ya dubata ya jima sannan ya tafi office a CBN Kano yake aiki, bayan tafiyarsa babu jimawa Dr Saleem ya basu sallama suka tafi gda yayar Hameed Aunty Zarah tazo gdan saboda Hajiya ta kirata ta zayyane mata komai suka hadu a parlour sukayita Allah wadarai da abinda Hameed yayima Umaimah abin takaicin harda Daddy shima ya biye musu yace “wlh badon Hameed dana bane babu yanda zanyi dashi dasai nayi qararsa an fiddawa marainiyar Allah haqqinta jiya fah tsabar ya rainamin hankali na kirashi inayi masa fadan kuskuren da yayi sai cemin yayi shifa baiyi wani laifi ba Umaimah matarsa ce laifinsa daya daya boye mana gsky danaji rainin hankalin nasa yayi yawa sai nace ya tashi ya bani guri kawai saiya fashemin da kuka waishi ba mazinaci bane idan bamu yarda da abinda ya fada mana ba mubashi dama ya gabatar da wasu daga cikin shaidun da suka shaida daurin auransa da Umaimah fada na haushi dashi kamar zan cinyeshi amma bai fasa fadamin ba shifa matarsa yayi mu'amala da ita ba wata ba har yana neman yimin rashin kunya wai gobema idan yana buqatarta zai nemeta yayi duk abinda yaga dama da ita tunda shi yasan ba zina yakeyi ba saboda haka Hajiya sai kinsa tsaro sosai akan yaronnan saboda idan kikayi sake zaa samu matsala tabbas shima mgnrsa abar dubawa ce saboda haka zanyi binkice sosai kuma nace ya gabatar min da shaidunsa nanda kwanaki uku idan ba hakaba zan sauki matakin shari'a akansa” Yana fadin haka ya tashi ya nufi samansa itama Umaimah miqewa tayi daga jikin Hajiya ta shige dakin da idan tazo take zama a ciki ta kwanta itadai zuciyarta babu dadi kwata² batajin dadin yanda suke aibata Uncle din nata saboda koba komai yayi mata abubuwa da yawa da bazata iya mantawa dashi ba, tana wannan tunanin wayarta tayi qara ta dauka da sauri taga qawarta ce Sa'ud da sauri ta kara a kunnenta tace “Hello Sa'ud kizo gdan Hajiyata don Allah yanzu inason ganinki" tana fadin haka ta kashe wayar tananan kwance baafi 20 minutes ba taji muryar Sa'ud din suna gaisawa da Hajiya, Shigowa tayi tare da mayar da qofar ta rufe ta zubawa Umaimah ido tare da cewa “nashiga uku Umaimah meye ya sameki haka kika rame?" Lumshe idonta tayi tare da miqewa zaune tace “meyema bai sameni ba Sa'ud bari nayi na cikin Uncle” nan ta kwashe komai ta fada mata tace “Sa'ud nifa Ina tunanin abinda Uncle yake fada gsky ne saboda shekara daya baya munje Maiduguri lkcn dagani saishi sai yaran Aunty Sadiya qin zuwa tayi tace aiba taron family dunsu bane Ina kwance nayi matashin kai da cinyar kaka ya shigo parlourn tunda ya shigo naga yanamin kallon qurullah hankalinsa gaba daya yanakan qirjina saboda rigar jikina ba wata ta kirki bace kuma ko bra
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111