Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 107

Chapter 107

Gidan Uncle Return Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Daddy fitowa da sauri daidai lkcn da Nawwas ya fito yanz rarrafe ya shige jikinsa qanqame yaron yayi yanabin iyayen nasa da kallo zuciyarsa na ciwo yace. “Fisabilillahi Daddy adalci kenan kubar Umaimah ta rinqa kwashe² kowanne kare doki yanzu wannan kuma me yazoyi gdan nan?" Hajiya ce ta tafa hanu tace “Heee Allah na dawo inji dan cirani yanzu Hameed sanyata zamuyi a gaba mu kwadata muci ko kuwa hanata zabin ranta zamuyi shita kawo tace tanaso mgn har tayi nisa ma aure saura sati daya kayi hqr ka rungumi sorry Umaimah ta daina yayinka...." Daga mata hanu yayi a fusace ya miqe kamar mahaukaci yace “ya isa Hajiya basai kin kasheni ba naji naji abinda kikeso kice amma wlh tallahi bai isa ya auri matata ba nagaji da binku din da nakeyi kuna neman turani kabari nine na farko kuma nine na qarshe ko Sulaiman don babu yanda zanyi ne na barshi yayi shuka a gonata amma wannan kodadden balaraben bai isaba wlh saidai muyi mutuwar kasko zan saceta nabar qasar da ita idan yaso kowa ya huta kuma wlh Idan na dauketa guba zan dura mata sannan nima nasha tunda naga Allan ma bazai kasheni na huta ba gara na kashe kaina da kallon wannan ta'addancin da akeyimin ni banida gata banida masu sona bani da wanda zai tausaya min bayan kunsan komai...." Katse mgnr yayi saboda numfashinsa da yake sama da sauri ya dafe qirjinsa yayi waje a guje da sauri Daddy yabi bayansa ya riqo hanunsa ya juyo da sauri zuciyarsa na tafasa idanunsa na fitar da hawaye yace “ka qyaleni Daddy wlh kasheta zanyi na kashe kaina kowa ya huta na gaji Daddy na gaji wanne irin rarrashi ne banyi yarinyar nan ba wanne irin qasqantar dakai ne banyi mata ba koda ace a cikin hayyacina nayi mata laifin da take iqirarin nayi mata indai tanada imani ya kamata ta tausayamin....” Daidai lkcn sukayi sallama Prof Khair ya shiga motarsa ya tafi ita kuma ta tako cikin takunta na isa ta raba ta gefensu zata gifta ya cafko hanunta da qarfi ya finciko ta ta fada jikinsa babu kunya yasa hanu ya matseta yace “wlh tallahi billahillazi La'ilaha illah huwa babu wanda ya isa ya rabani dake don kece rayuwata Umaimah ko zaa kasheni kuma ko zan rasa komai nawa a yau sai an dauramin aure dake idan kuwa akaqi wannan karon zan saceki sacewar da babu wanda zai sake ganinki har abada" yana fadin haka ya fizge hanunsa daga na Daddy Hajiya tayi saurin riqeshi tace “Alh kayi wani abu kace wani abu wlh Hameed ya haukace baa cikin hayyacinsa yake ba zai iyayin komai Alh yaronnan mukaishi asibitin mahaukata a duba kwalwarsa" daga mata hanu yayi yace. “Babana shiga gda zaayi yanda kakeso a yau da wani bacin ran gara wani Umaimah zo inason ganinki" sakinta yayi ya zube a gurin yana kuka me gigita tunanin kowa da ban tausayi yace “babu inda zani Daddy ni zakayi wa wayo wlh yau saina kwana da Umaimatu kota halin qaqa nasani tana sona toshewar qwalwarta yasa ta kasa fahimtar hakan waye zai aureta ya riqe mana yayanmu idan bani ba so take dole saita tozarta amanar Allah so take dole sai twince sun tashi sun fuskancin cewa su marayune meyasa zata bijirewa saqon zuciyarta bayan nasan babu son kowa a cikinta sai nawa meyasa bazaku kalli idonta ba kalli Daddy Hajiya kalli idonta wlh sona kawai nake hangowa a ciki so take ta kasheni ta kashe kanta bayan tasan ba cikkakiyar lfy ce dani ba itama kuma nasani zuciyarta ta kamu da irin ciwon da yake damun tawa zuciyar" Daqyar Daddy da Hajiya suka bambareta daga jikinsa suka jata suka shiga da ita gdan suka kulle parlourn ya miqe yana buga qofar da qarfi yana cewa “ku bude bude Daddy zan balle qofarnan wlh saika bani matata ai donni kadai aka halicceta bazan yarda ku rabani da matata ba....." Surutai dai rututu na rashin kan gado haka Hameed yakeyi kamar zautacce yana dukan qofar kamar zai balleta saida ya gaji ya hqr ya fita ya shiga motarsa ya nufi gdansa ya bude dake an gama aikinsa tsaf har ya zuba komai na amfani ya fada daya cikin dakunan ko qofar bai rufeba jikinsa yana bari zuciyarsa na tafasa yana dafe qirjinsa da qarfi yana nishi da kakarin aman wahala. Shi kuwa Daddy yana shiga da ita ya zube akan gwiwarsa ya ruqo hanunta yace “badon ni ba badon na isa dake ba don girman Allah Umaimatu ki duba maraicin twince da wasiyyar mijinki Sulaiman ki bani dama ta qarshe na daura auranki da Hameed yaron nan ya garu sosai sonki zai kasheshi Umaimatu ya zakiyi da haqqin ran dan'uwanki idan ya mutu saboda ke bayan kinada yanda zakiyi ki taimakesa...." zubewa tayi ta rungume Daddy tana kuka me ban tausayi tace “kada ka qara roqona akan wannan Daddy zan iya bada rayuwata na fanshi taka balle wannan wlh indai hakan zai zama farin ciki a gareka na amince da auren Abdulhameed indai hakan zai zama farin cikinka na amince wlh na amince Daddy" tana fadin haka ta miqe da sauri ta fada daki saman gado ta fashe da wani kuka me ciwo tana cewa “Allah ka yafemin laifin da nayi maka ka sake jarabta ta da auren Abdulhameed Allah ka dubeni ka kawomin dauki cikin buwayarka Allah na roqeka kabani ikon yima mahaifina biyayya" A wannan daren Daddy bai zauna ba yana fita ya kira Yusuf da mijin Aunty Zarah a masallaci bayan sallar magaruba ya fadawa limamin cewa yanada daurin auren yayansa biyu yabada komai aka daura auran akan sadaki dubu dari biyu suna shiga gdan ya fadawa Hajiya takuwa rangada guda ta daga hanu sama tace “Allah na gde maka daka sake gwadamin wannan rana Umaimatu na matar Hameedu na wayyoh dadi kasheni na huta" tasowa tayi zata fito taji mgnr Hajiyan ta koma da sauri ta zauna tana fadin “Hasbunallahu wa ni'imal wakil Innanillahi wa innah ilaihirraji'un Allahummah ajjirni fi musibati wa'akalifni khairin minha yanzu nice matar Hameed mutuwa ta tazo ya zanyi da jarabar Hameed" shigowar Hajiya ne yasata dagowa ta dubeta hawaye nabin kuncinta tace “Hajiya yanzu shikenan an daura aurena da Hameed Hajiya kwanana ya qare nama sani bazan iya dauke lalurarsa ba kamar yanda na dauka a baya Hajiya ki taimakeni...." Rufe mata baki tayi da hanunta tana girgiza mata kai tace “kiyi hqr Umaimah Hameed zai canza baza kiyi irin zaman da kukayi a baya ba wlh ni kaina da farko banyi farin ciki ba amma yanzu ina farin ciki sosai saboda na yarda kuma na gasqata Hameed sonki yakeyi da gaske baso irin na sha'awa ba" da wadannan kalaman tayita rarrashin ta har ta samu ta saurara da kukan dama ta fara shiryata da magungunan su kasancewar saura sati daya aurenta da prof Khair saboda haka ta dora daga inda ta tsaya tunda tariga tasan halin dannata ba sauqi gareshi ba. Yusuf ne ya nufi gdan Hameed din da nufin yi masa kyakkyawan albishir get man din ya tambaya ko megidan yana ciki yace masa eh yayi parking ya shiga yanata kiransa yana cewa “dallah malam ka fito haukanka yayi rana Allah dai ya yarda

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});