Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 71

Chapter 71

Gidan Uncle Return Complete Hausa Novel 1,203 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

mata ya shafa mata powder tare da taje mata sumarta baqa sidik mai yawa da tsayi yayi kissing lips dinta ya dauketa yace “ehhhh beautiful daughter kinfi kowacce ya kyau a duniya" Suna fitowa Daddy yana nocking door din qarasawa yayi ya bude Daddy ya shigo ya dubi Shurafah da taketa hanqoron zuwa gurinsa yayi murmushi tare da daukanta ya cillata sama ya cafe yace “kin tashi lfy ayar Allah" kallonshi dukkansu sukayi yayi murmushi irin nasu na manya yace “sunanta kenan iznah ce Zulaiha" share zancen yayi da cewa. Naso na bari sai nan da kwanaki shidda mu tafi so amma wani uzuri ya tasomin na gaggawa saboda haka yau da yamma nakesa ran zan tafi..." da sauri Umaimah ta tari numfashin sa da cewa “yawwa Daddy dama inason ce maka nima zan bika mu tafi saboda saura kwanaki uku hutunmu ya qare” wani malolon kishine ya tasowa Hameed yayi saurin kallon Daddy yace “hutun me Daddy?" Murmushi Daddy yayi yace “hutun makaranta ta fara degree dinta a Skyline University har sunyi semester guda” Daure fuska yayi ya zabga mata wata uwar harara ya juyo ya kalli Daddy yace “kayi tafiyarka kawai Daddy idan na qarajin qwarin jikina zamu taho" dagowa tayi cikin tsoro saboda ita tunda taganshi jiya yayi Mata wani kwarjini sannan tsawar daya daka mata jiyan tasata jin wani mugun tsoronsa ya darsu a zuciyarta tace “amma don Allah Uncl...." hanunsa ya dora a lips dinsa alamun tayi masa shiru yace “ba dake nake mgn ba malama banason rashin kunya" Kallonsa Daddy yayi da mamaki yaga yanda ya wani tsare gda shi a dole me iko yasan tabbas idan ya barta bazaa shuka abin arziqi ba ya miqe yace “debo kayanki kizo mu tafi Jidda mu jira lkc mu tafi" miqewa tayi zuciyarta fari tas ta shiga dakin ta fara hada shirginta saboda Allah ma ya sani bazata iya zama inuwa daya da wannan sabon Hameed din mara mutunci ba. Baiyi mata mgn ba har saida ta gama hada kan kayanta ta goya yarta tabi bayan Daddy har Daddy yakai bakin qofa ya zai fita suka tsinkayo muryar Hameed yana cewa “nine mijinki ba Daddy ba idan kika taka qafar wajen dakin nan a bakin igiyoyin aurenki"........ *UMMUH HAIRAN CE...✍🏻* [1/24, 9:32 AM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *G.U* Ki biya kafin ki karanta idan kinaso ki kira number nan; 09031307566: Tsayawa sukayi cak daga ita har Daddy saboda girma da mamakin da furucin nasa ya basu amma shi ko a jikinsa miqewa ma yayi ya shige bedroom ya rufo qofar. Hawayene suka fara bin kuncinta tace “muje Daddy” girgiza mata kai yayi da sauri yace “bazaayi haka ba Umaimah ya kamata mu daina yanke hukunci cikin fushi saboda munyi a baya bamuga ribarsa ba qarshe ma sai tarin nadama da fargar jaji da ya sanyamu kiyi hqr kibi umarnin mijinki yafi komai muhimmanci kinsan har yanzu ba daidai yake ba sai kinyi hqr da yanayinsa kafin ya koma normal” Sanya hununsa yayi a aljihunsa ya dauko kudi Riyadh da batasan adadinsu ba ya miqa mata yace “ki kasance me hqr aduk inda kika samu kanki Umaimah komai yayi farko yanada qarshe" komawa tayi ta zauna saman kujera tayi watsi da kayan hanunta tare da kwance Shurafah ta rungumeta a qirjinta tasaki kuka me ciwo tana jinjina yanda zaman nasu zai kasance miqewa tayi ta shiga dakin yana kwance saman bed din yana sauraron qira'ar Shaikh Sulaiman yanabi a hankali ta zauna gefen gadon tare sanya hanunta ta dan daki cinyarsa kadan. Wata zabura yayi ya miqe zaune tare da watsa mata wani mugun kallo yace “meye kuma na zuwa ki dameni wato bakiji abinda na fada miki ba ko?" Share hawayenta tayi tace “Don Allah kayi hqr kabarni nabi Daddy banajin dadin rayuwar qasar nan ni kadai" murmushi yayi na isa yace “bakyajin dadin rayuwar qasar nan ke kadai ko? Hmn tashi ki bani guri" Kallonsa tayi da manyan sexy eyes dinta da suke cike da qwallah ta bude baki zatayi mgn yayi saurin daga mata hanu yace “silent pls nayi waya da reception kije ki karbi key din dakin kusa da wannan banason takura" miqewa tayi ta koma parlourn ta hade kanta da gwiwa taci gaba da rera kukanta cikin tausayin kanta wai yau ita Hameed yake kora daga sashin sa ta fada tare da miqewa ta nufi reception din suka bata key din tare dayi mata jagora har dakin shima suit ne kamar wanda Hameed din yake ciki larabawa akwai tsafta dakin sai zuba qamshi yakeyi tayi ajiyar zuciya ta haye gadon ta kwanta. Yinin ranar gaba daya bataga Shurafah ba itama bata nemeta ba tunda tasan idan taje ma rashin mutunci zata jawowa kanta haka tayita harkokinta ita daya saidai tayi waya a kawo mata abinci idan taci ta sake waya azo a dauka haka har dare yayi ta miqe ta shiga bathroom tayi wanka ta dauro alwala tayi sallar isha sannan ta tashi ta murzawa jikinta mai ta fesa turarenta ta zura rigar baccinta ta haye gadon taja blanket tayi kwanciyarta. Cikin bacci taji ana danna Bel din qofar ta miqe tare da tambayar “waye?" Cikin muryarsa mai kama data wanda yakejin bacci yace “waye kike tunanin zaizo gurinki a daren nan?" Ajiyar zuciya tayi ta bude dakin ya shigo tare da qarewa dakin kallo har ya sauke idanunsa akanta qirjinsa ya buga da qarfi ganin yar yaloluwar rigar baccin dake jikinta itamma kallonsa takeyi ganin yanda ta kafeshi da idone yasashi saurin dauke nasa idon cikin son nuna baiji komai ba a yanayin daya ganta yace. “Na lura baki damu da yarinyar nan ba tun safe rabon daki sanyata a idonki amma tunanin qaramar qwalwarki bai baki cewa kije ki duba lfyrta ba" kawar dakai tayi ta fara takawa cikin takunta na isa da ko in kula komai na jikinta yana girgiza ta haye gadon taja bargonta ta rufa batare da tace masa komai ba saboda ta lura da take²nsa idan ta gaba da nuna masa damuwarta akan abinda yakeyi mata to ya samu qofar wulaqantata kenan ita kuma ko kadan bata dauki wulaqanci ba toma banda tsabar rainin wayo irin nasa meye yake sabo a gurinta game dashi da har zaiyi tunanin zata jure wulaqancinsa saboda shi. Matsawa yayi jikin gadon ya janye bargon data rufa dashi ya kwantar da Shurafah a gefenta yace “ki tashi ki bata tasha banason ake barmin yarinya da yunwa" kuda bakwa gurin idan kun samu arziqin motsawa to itama ta motsa wani takaici ne ya tokare masa maqoshi ya haye gadon a fusace ta miqe da sauri zata sauka ya cafkota da sauri ya hadata da jikinsa suka kama kokawa ta tureshi ta miqe da sauri ta nufi parlourn da sauri ya sake cafkota yace “wlh idan kika fusatani zakiji a jikinki” buge hanunsa tayi tace “ka ficemin daga daki banason ganinka dacan kaine kake sani nake bata nonon ko kuwa biyana kake da zaka titsiyeni saina bata” Sakinta yayi da mamakin irin rainin dake tsakaninsa da Umaimah juyawa yayi ya fice saboda yanda zuciya ke fuzgarsa ya afka mata amma bayaso so yake ya nuna mata ko babu ita zai iya rayuwa so yake ta gane kuskurenta na banzatar da rayuwarsa ta watsar da

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});