Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 49

Chapter 49

Gidan Uncle Return Complete Hausa Novel 1,212 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Batayi mgn ba har Hajiya ta gaba fadanta ta tashi ta nufi kitchen miqewa tayi a sanyaye tabita suka gama aikin suna gamawa suka dawo parlourn lkcn Hajiya ta shiga dakinta zama tayi a dinning din ta dora kanta a hannuta zuciyarta nayi mata wani irin ciwo bataso kuma bata qaunar taji Hajiya na fadin mugayen kalamai akan Hameed. Jitayi an rufe mata ido qamshin turarensa ne yasata sauke ajiyar zuciya hakanan taji wani sanyi da farin ciki yana ziyartar zuciyarta janye hanunsa tayi tayi kissing din tafin hanunsa tare da daga kanta suka hada ido ya lumshe idonsa tare da sakin mata kyakkyawan smile dinsa dake qara narkar da zuciyarta sunkuyawa yayi ya dora bakinsa saman nata ya hadesu yana yawo da harshensa cikin bakinta yana sakin ajiyar zuciya. Hannunta ta dora saman kansa ta janye bakinta a nutse tanajin wata ninki qaunarsa na zagaya jikinta duk abinda ke faruwa tsakaninta dashi bata tabajin haushinsa ba saima tarin tausayinsa daya samu guri ya zauna a zuciyarta yasani mijinta dabanne bashi da wani aibi bayan matsalarsa wadda ta riga ta yarda kuma ta karbeta amatsayin kaddararsu tasani rabata dashi kamar rabata da rayuwarta ne. Duk tayi wannan tunanin ne cikin abinda bai wucce minti daya ba “banda kamarki Umaimah dake kadai nake kambunki na riqe babu ranar dazan sake Umaimah keta dabance dake kadai nake burin gama rayuwata Umaimah duk inda nake tunanin samun sauqi na kasa samu hatta kaka da nake tunanin zata fahimceni jiya na kirata taqi daga wayata wlh banida burin cutar dake Umaimah ke tawace ni nakine ko babu aure tsakaninmu ni nakine kada ki barni na zama maraya Umaimah na qaddara banida kowa a duniya bayan ke saboda ke kadaice kike tausayina kece kika zabi farin cikina fiye da naki na rantse miki da ubangijin da yake busamin numfashi da ace zaa dawomin da littafin qaddarata saina soke wannan saboda ba kyakkyawar qaddara bace bansan sanda nake yi miki irin wannan cin ba Umaimah nafi kowa son naga rayuwarki ta inganta saboda nafi kowa sonki Umaimah kada ki daina tausayina don Allah kada ki amince a rabamu.......” Rufe masa baki tayi da sauri tana hawaye sosai kalamansa suka kashe mata jiki fadawa tayi jikinsa tanajin ninkin tausayinsa da qaunarsa tace “ya isa nace ya isa Abdulhameed na yarda kai nawa ne ni takace bazan taba gudunka ba kuma bazan taba daina tausayinka ba inasonka fiye da son da nakewa cikinnan dake jikina nafi buqatarka fiye da kowa da komai a duniya amma hakan bazai hana muyima iyayenmu biyayya ba kayi hqr duk inda zani a duniya bani da gwanin daya fika kaine gwarzona kuma kaine jarumi na dole ko anaso ko baasa abarni dakai saboda sun sani bazan taba iya rayuwa da wani bakai......” Marin da taji ne ya sanyata saurin janye jikinta Hajiya ta gani tsaye a kansu shikuma yana dafe da kuncinsa hawayen dake bin fuskarsa sun nunku bakinsa yana rawa itama nata yana rawa tace “Hajiya kika mareshi....” bata ida rufe bakinta ba itama takai mata marin yayi saurin janyeta ta sake samunsa ya miqe jikinsa na bari ya figi hanunta amma Hajiyan tayi saurin riqeta tace “indai nonona kasha ka girma har ka kawo yanzu to Ina baka umarnin ka saki Umaimah a yanzun nan ba tare daka qara daga qafarka ba idan ba haka ba kuma na debe maka albarkar da kake taqama da ita”...... *UMMUH HAIRAN CE...✍🏻* [1/15, 9:05 AM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: https://www.facebook.com/Zauren-Brilliant-Writers-Pans-111419110389493/ *🅱RILLIANT WRITERS* *ASSOCIATION* 🖊 ( _Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers)_ *GIDAN UNCLE* ( _Love and romantic story_) *SHORT AND TRUE LIFE STORY* *MALLAKAR* 👇🏻 *FAUZIYYA TASI'U UMAR* *®FAUZAH* www.fauzahtasiu41@gmail.com Ki biya kafin ki karanta ta GTbank akan wannan account number: 0255526235; sai kiyi screenshot ki tura wannan number: 09013718241; Ko katin waya MTN or Airtel ta wannan number:09031307566: *PAGE TWENTY-FIVE* Juyowa sukayi a tare cikin mamaki dukkansu suke kallon Hajiyan da tayi kicin² ta riqe Umaimah gam tare da qara daka masa tsawa tace “ka saketa nace Hameed wlh kaji na rantse gdannan yau dagani sai ku Daddynku baya qasar nan saboda haka dole ka saki Umaimah bazaka kashe marainiyar Allah ba Hameed tsine maka zanyi idan kaqi yimin biyayya" Cikin tsananin tashin hankali ya zube a gurin muryarsa na wata irin karkarwa yace “na roqeki Hajiya kiyimin rai ki ceci rayuwata wlh inason matata ita kadai ta saura me tausayina a duniya Hajiya kada ki rabamu wlh nayi miki alqawarin bazan qara kusantar Umaimah ba har abada amma ki barmu tare Hajiya tana sona inasonta....” daukeshi da mari Hajiya tayi tace “bawai tausayinka ne banaji ba amma kaima kasan zamanka da Umaimah cutawa ne a gareka da ita kanta saboda haka dole anan ka saketa” miqewa yayi yana layi kamar dan giya ya nufi qofa zai fice Umaimah tayi saurin riqoshi cikin kuka me ban tausayi tace. “Kada ka fita cikin tsinuwar mahaifiyarka Uncle bawai saboda wannan dalilin ne kawai Hajiya takeson rabamu ba tanason rabamu ne saboda banida kowa banida gata don girman Allah Hameed kada ka sabawa umarnin Hajiya ka sakeni Hameed ka sakeni nace...” rufe mata baki yayi yana girgiza Mata kai Amma ya kasa cewa komai sai rawa da jikinsa yakeyi ya janyo Umaiman ya hadata da qirjinsa “Allah ya tsine....” da sauri Umaimah ta janye jikinta daga nasa ta cukumi wuyansa tace “wlh bazaka taba kasancewa cikin tsinuwar mahaifiyarka akaina ba dole ka sakeni Hameed” qara rufe mata baki yayi da sauri yana girgiza mata kai yana hawayen tausayin kansa cikin tashin hankali yace “Haj....” katseshi ta kuma yi tace “wlh saika saketa Hameed” Cikin fitar hayyaci yace “shis.. shikenan na...na sakeki saki day....” bai ida qarasawa ba wani mugun jiri ya debeshi yayi baya kansa ya hadu da glass din qofar ya fadi tim tare da ballewar jini a kansa. Nufarsa tayi da gudu tana sakin wata qarar tashin hankali tana cewa “shikenan kin kasheshi Hajiya mun shiga ukun mu...” riqo hanunta Hajiyan tayi cikin tashin hankali tace “kada ki tabashi babu aure tsakaninku" zubewa tayi a gurin tayi zaman tan bori kanta da kwakwalwar ta na juyawa jin abin take kamar a mafarki “Hameed ya sakeni" ta fada a fili tare da miqewa tana dafa bango ta nufi dakinta tana shiga ta zube a qasa sai yanzu kukanta ya dawo sabo zuciyarta nayi mata suya kanta na juyawa “ Innanillahi wa innah ilaihir raji'un Allahummah ajjirni fi musibati wa'akalifni khairin minha” Su taketa maimaitawa batare da tunanin mafita tafi awa daya a zaune a gurin batasan lkc ya tafi ba saida wayarta tayi qara sannan ta iya rarrafawa ta daukota sunan Sa'ud tagani ta daga ta kara a kunnenta tare da fashewa da kuka tace “Sa'ud Hajiya ta rabani da farin cikina na shiga ukuna Sa'ud zuciyata zata fashe Ina tunanin mutawa tace ta iskeni a wannan lkcn” salati Sa'ud ta dauka tace “ta rabaku Umaimah yanzu Ina Hameed din?” bata iya bata amsa ba saboda wata hardewa da numfashinta yakeyi saurin kashe wayar tayi inda Sa'ud ta miqe cikin fitar hayyaci ta dauki motarta ta nufi gdan Umaiman amma tana zuwa get man din ya sanar da ita kusan sati batanan da mugun gudu ta juya ta nufi Sokoto road tana zuwa ta

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});