Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 51

Chapter 51

Gidan Uncle Return Complete Hausa Novel 1,215 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ta dubi Hajiya tace “Hajiya wai meye yayi coorsing din matsalar nan ne Ina matansa da banga kowacce a gurinnan ba?” Gaban Hajiya ne ya fadi ta miqe da sauri tace “na shiga uku na Zarah amanar Allah wlh na manta da ita" tana fadin haka ta fita da sauri ta tari dan sahu ta nufi gdan tun daga parlourn ta fara ganin gdan a hargitse dakinta ta nufa tana qwala mata kira amma shiru tura kanta tayi a dakin ta fara dube² amma babu alamar mutum a gurin kunna light din dakin tayi idanunta ya sauka akan inda Umaiman ta zauna dazun taga yanda jini ya bushe a gurin da sauri ta shiga ta banka qofar bandakin amma babu wata alama ta an shiga toilet din sake fita tayi tana kalle² a parlourn sai yanzu idanunta ya kai kan Nihal da Maliha da suke kwance a qasa kan tiles suna bacci matsawa tayi da sauri gurinsu tana haskasu fuskarsu duk tayi jirwaye da alamun kuka sukaci har sukayi bacci hankalinta ya dada tashi ta nufi wajen gdan ta fara qwalawa me gadi kira ya iso da gudu ya rusuna tace “ina Umaimah?" Da sauri ya kalleta yace “banganta ba nidai bayan ansa yallabai a mota kun tafi naga wata motar tazo amma banga wanda ya ke ciki ba kuma bata dade ba ta fita...”bata tsaya bata lkcn sauraron shirme ba ta juya gdan tana safa da marwa itakam taga ta kanta da yaran daga nema musu sauqi ta jangwalo fitina yanzu ina Umaimah ta tafi wata sani a garin wa take dashi a garin bayan su da zata wajenshi ta zauna? Tambaya ce mara amsa Hajiya take yiwa kanta har tana runtuma tuntube saboda tashin hankali. Debe yaran tayi ta kaisu dakinsu ta kwantar dasu ta kuma shiga dakin Umaiman itace leqe har qarqashin gado miqewa ta kumayi tana rarraba idanu ya shege a rabon gado sai yanzu ta lura ma duk wani abu da yake mallakin Umaimah babushi a dakin zubewa tayi a qasa tana karanto Innanillahi wa innah ilaihir raji'un kanta yana wata muguwar sarawa a fili tace. “Na shiga uku ni Zulaiha yau naga bala'i me hakan yake nufi Baby ta gudu saboda na rabata da abinda zai cutar da ita? Allah ka sani bada wata muguwar manufa nayi hakan ba Allah naji tsoron kada yaron nan ya hallaka ta ne Allah ka fitar dani kunyar duniya ka jefa marainiyar ka hanu na qwarai” tana maganar tana kuka me ban tausayi wayewar garin yau tayi danasani tafi dari tilon danta yana kwance baisan inda kansa yake ba ga marainiyar Allah ta gudu “wallahi saboda ni bazaka rayu cikin tsinuwar mahaifiyar kaba Hameed ka sakeni saika sakeni Hameed ba wannan dalilin ne kadai yasa takeson ta rabamu ba akwai wani qulli a zuciyarta...” kalaman Umaiman ne suka rinqa dawo mata tare dana Hameed din lkcn da yake kuka yana cewa “ki barni na rayu da farin cikina Hajiya nayi miki alqawarin bazan qara kusantar Umaimah ba har abada Hajiya ita kadai ta ragemin wadda takejin tausayina Hajiya kada ki rabamu tana sona kuma kema shaida ce inasonta babu wanda ya isa ya raba tsakanin hanta da jini…..” A matuqar sanyaye ta miqe ta fita zuwa dakinta ta dauki wayarta ta fara kiran wayar Umaiman tun kiran farko aka fada Mata a kashe wayar take amma bata daina Kiran ba har saita charging wayar tata ya dauke ta koma ta kwanta zuciyarta tayi mata wani mugun nauyi daidai lkcn kiran Daddy ya shigo a tsorace Hajiya ta daga cikin rawar murya tace “hel...lo Daddy" bai iya amsawa ba yace “nakira wayar babana najita a kashe na kira ta Umaimatu itama a kashe nayi miki Miss call yafi ashirin baki daga ba Zarah ta kirani tacemin babana yana asibiti cikin mayuwacin halin da baisan wake a kansa ba meye yake faruwa ne"....... *UMMUH HAIRAN CE...✍🏻* [1/15, 8:46 PM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: https://www.facebook.com/Zauren-Brilliant-Writers-Pans-111419110389493/ *🅱RILLIANT WRITERS* *ASSOCIATION* 🖊 ( _Pens of freedom,home of exceptional and magnificent writers)_ *GIDAN UNCLE* ( _Love and romantic story_) *SHORT AND TRUE LIFE STORY* *MALLAKAR* 👇🏻 *FAUZIYYA TASI'U UMAR* *®FAUZAH* www.fauzahtasiu41@gmail.com Ki biya kafin ki karanta ta GTbank akan wannan account number: 0255526235; sai kiyi screenshot ki tura wannan number: 09013718241; Ko katin waya MTN or Airtel ta wannan number:09031307566: *PAGE TWENTY-SIX* Cikin in..Ina Hajiya tace “ba...babu komai Alh kawai dai dama bashi da lfy ne kawai ita kuma Umaimah batajin dadi don harma tayi bacci” haka kawai yaji bai gamsu da abinda take fada ba amma bayason musu da ita saboda haka ya ajiye wayar da qudurin gobe zaiyi asubanci ya diro Kano tunda dama ba nisa yayi ba South Africa yaje. ************************* Kwance take saman kujerar parlourn washegarin ranar da abin ya faru zuciyarta tana mata wani irin suya tanajin takaici da tsanar Hajiya data rabata da farin cikinta taji shigowar Sa'ud miqewa tayi da sauri tana kallon Sa'ud din dake sanye cikin rigar bacci ta zauna a kusa da ita tana miqa tace “jiya bamu samu zama ba na shiga naga kinyi bacci da wuri yanzun dai me zakici?" Idonta a lumshe yake amma hawaye take fitarwa tace “Abdulhameed” kallonta Sa'ud tayi tana mamakin kalmar bakinta tace “kinsan kuwa me kike cewa bloody" bude idanunta tayi tar akan Sa'ud tace “nasani Sa'ud shi kadai nakeson ci shi nakeson gani kuma shi nakeso naji a jikina jiya ban iya bacci ba Sa'ud saboda tunanin halin da mijina yake ciki yanzu shikenan na tabbata sakakkiya na tabbata ba matsayin matarsa ba wannan wacce irin rayuwa ce meyasa banida saa a rayuwata Sa'ud son Hameed shine zai kasheni a jinina yake ya zanyi na rayu babu Hameed Sa'ud na saba dashi.....” kukane yaci qarfinta Sa'ud ta kamota ta rungume ta tana sharar hawaye cikin kuka itama tace “yanzu Ina Uncle din yake" kuka takeyi sosai tace “yana asibiti bansan halin da yake ciki ba inajin tsoron kada na rasashi Sa'ud ruhi nane a jikinsa nasane a jikina Sa'ud farin cikin Hameed shine nawa bazan taba iya rayuwar da babushi a cikinta ba” Daqyar Sa'ud ta rarrasheta tayi shiru tare dayi mata alqawarin zasu tsayawa juna kaida fata wajan dawowar farin cikin rayuwarsu rungume juna sukayi suna kuka Sa'ud ce tace “Umaimah rayuwarmu tana fuskanta matsala sati uku kenan da su Hajiya suka koreni daga gdansu saboda nace bazan auri Yaya Auwal ba Umaimah banida da kowa a Kano bansan kowa ba saisu haka na dauki kayana na fito bansan inda zan dosa ba gashi babu waya a hanuna saboda tun kafin wannan lkcn aka karbe wayata aka iyakar layin ne a hanuna nayi tunanin zuwa gdanki sai naji tsoron kada naja miki matsala kema a wajan yan garuwar unguwar mu na ari waya nasa layina na Kira Anwar nake fada masa halin da nake ciki banyi tunanin samun taimako daga gurinsa ba saboda irin cin mutuncin da yan uwana sukayi masa shida mahaifinsa amma ga mamakina sai naji hankalinsa ya tashi yacemin na jirashi gashina baifi minti biyar ba ya iso ya daukeni ya mayar dani gda amma Hajiya da Abba suka rufe ido sukaci mutuncin mu qarshe suka koromu harda cemin ai dama karuwanci nakeyi abinda ya karbeni kenan saboda haka naje nayi abinda na

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});