Chapter 102
Chapter 102
kafin su ankara ta janye yadin da aka lullubeshi ta matsa ta qara kallon fuskarsa da gaske ba gizo ba Sulaiman ne kwance babu numfashi a jikinsa fuskarsa wasai da murmushin sa na rahama ta dafe qirjinta tare da furta Innanillahi wa innah ilaihirraji'un tayi baya luuuuuu ta zube a qasa itama qanwar gawa da sauri Daddy da Hajiya sukayo kanta aka dauketa itama aka shiga da ita ciki aka kwantar da ita a gado babu irin ruwan da basu yayyafa Mata ba amma taqi dawowa hayyacinta hakanan aka kimtsa Sulaiman aka daukeshi aka kaishi gdansa na gsky zuciyoyi na kukan rashin managarcin mutum salihin bawa wanda bashi da tamka Hajiya Sa'adatu fadi takeyi. “Wlh babana da nasan mutuwa zakayi da bazan takura maka kaje gaisuwar nan ba saida ka nunamin bakason tfyr na takura maka dake kaidin dane me biyayya haka ka tafi yanzu ka mutu babana ka mutu kabar matarka abar qaunarka ka mutu kabar yayanka masu kwanaki goma sha daya a duniya ka mutu ka barni kabar yan'uwanka kabar abokanka kabar kowa babana wayyoni kaina wayyoh Umaimatu dole ki suma kinyi rashi Umaimatu wannan mutuwa takice ke akayiwa mutuwa kin rasa miji me sonki da qaunarki kin rasa miji me tausayinki dason farin cikinki Umaimatu Allah ya mayar miki da alkhairi Umaimatu na rasaki yanzu kenan na rasa sukura ta qwarai wadda ta ginamin dana da tsarkakkakiyar soyayyah Allah na gde maka da baka dauki rayuwar Sulaiman ba saida ka cika masa burinsa na ganin yayansa" Bayan ankai Sulaiman makwancinsa aka dauki Umaimah aka tafi da ita asibiti tashin hankalin dasu Daddy basu taba shiga wannan karon shi suka shiga ba akan Umaimah yau shi suka shiga Umaimah ma da ciwon zuciya wannan wacce irin jarabta ce suke fuskanta ne. Bata samu kanta ba saida tayi kwanaki bakwai saboda kumburar da zuciyarta tayi twins kuwa sai madara ake basu bayan ta dawo hayyacinta mutuwar mijin nata ta dawo mata sabuwa tayi kuka kamar ranta zai fita tanajin dama ita ta mutu ta huta daqyar Hajiya ta shawo kanta da dadadan kalamai da misalai kwatankwacin nata da kuma irin nasarorin da zata iya riska a rayuwarta da wadannan kalaman Hajiya da Daddy sukayita kwantar mata da hankali amma duk sanda ta kalli Nawwas da Nawwarah sai tayi kuka saboda tunawa da kalmarsa ta qarshe yayana amanane a gareki inasonki Umaimah” wannan dalilin taci alwashin zata tsaya ta riqe masa amanar yayansa koda kuwa zata mutu babu aure ita aurenma ya fita a ranta tama hqr dashi gara ta zauna tayi rayuwarta ita kadai tunda bai karbeta ba. Haka su Hajiya suka tafi da ita gda aka gyara mata dakinta aka zuba mata komai sabo duk wani abu da zai cire mata kewa saida suka sanya mata ga mai rainon twins dinta ita dakinta guda sannan ga Maliha da Shuraif da suke dauke mata kewa lkcn Allah yasa cikin hutu suke koda aka koma mkrntar ita bata komaba saboda abin na gdane ita daluba ce shi kuma marigayi D.S malami ne da sukeji dashi a Skyline University sunji mutuwarsa sosai hukumar makarantar tayi rawar gani sosai wajen ganin sun yiwa iyalan D.S wani abu aikuwa sunji dadi koda akazo rabon gado da Abba da Hajiya Sa'adatu cewa sukayi sun yafewa Umaimah da yayanta komai. Rayuwar haka taci gaba da tafiya bason raiba sai bayan wata uku da rasuwar D.S sannan Daddy ya sanar da Hameed ya tausayawa twins tare da jin ninkin qaunarsu a zuciyarsa yasan rabonsu shine ya rabashi da mahaifiyarsu sannan rabonsa dabai qare a jikinta ba shine ya kashe mahaifinsu" da wannan tunanin ya biyo jirgi ya dira a 9ja batare daya fadawa kowa ba suna zaune a parlour da hijjab dinta na masu takaba ya shigo da sallamarsa Maliha da Shuraif sukayi tsalle suka rungumeshi Twince kuwa da suke koyon zama sai bangale masa baki sukeyi murmushi yayi me hade da kwallah yana tuna irin wulaqancin daya rinqa yiwa mahaifinsu lkcn da yana neman auren Umaimah ya sunkuya ya daukesu ya rungumesu a jikinsa wani kuka me qarfi ya kwace masa yayi saurin tashi daga gurin ya shige dakinsa da yaran ko gaisawa da Hajiya bai iya yi ba balle Umaimah tasaran zaiyi mata ta'aziyyar mijinta, itama batasan sanda mikin mutuwar D.S ya dawo Mata sabo....... *UMMUH HAIRAN CE...✍🏻* [2/3, 11:53 AM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *_GU_* Miqewa tayi ta shige dakinta ta kwanta tanajin haushi da tsanar duk wanda ya kasa yi mata gaisuwar rashin mijinta da takejin bazata mayar da kamarsa ba a duniya. Shima ya jima yana kallon Nawwas da Nawwarah yana kuka yaran sai wasa sukeyi da gashin qirjinsa sunayi masa dariya kamar Nawwas da mahaifinsa har tayi yawa kamar dai shida Shuraif abubuwan da yayiwa D.S suna sake bijiro masa musamman haduwarsu ta qarshe lkcn mutuwar Nihal da Shurafah da yazo daukarta yana ganinsa yana miqa masa hanu ya bige hanunsa ya wucce hakan baisa yaji haushi ba washe gari ma daya dawo karba mawa Umaimah yajin daddawa lkcn da cikin yaran saida ya sake miqa masa hanu da yaqi bashi nasa kawai sai yaga ya share qwallah ya rungumeshi yace. “Kada ka qullaceni a zuciyarka Yaya banine na rabaka da Umaimah ba qaddara ce kuma nima itace ta hadani da ita wlh da inada ikon halatta maka Umaimah tun kafin muyi aure zan halatta maka ita saboda nasani kaine Umaimah takeso kaima kuma ita kakeso amma Ina banida damar hakan abu dayane zai hanani dawo maka da Umaimah saboda ina burin rayuwarta ta samu farin ciki Hameed ka qaddara idan Umaimah rabonka ce zata dawo gareka amma bayan qasa ta rufe idona saboda a tsarin rayuwata mace ko cutar dani take indai bazata cutar da Umaimah ba zan rayu da ita balle Umaimah da kullum burinta farin cikina Hameed idan na mutu bana fatan kabar Umaimah ta auri wani bakai ba saboda Ina kishinta kuma nasan zaka riqemin dana saboda kanada imani kuma kanason uwarsu" Yana fadin haka ya sakeshi ya shiga motarsa yaja yana daga masa hannu yanayi masa murmushinsa me tsayawa s zuciya “kyakkyawan namiji me kyakkyawan hali da sanyin zuciya ya mutu" ya fada yana rungume yaran a jikinsa yace “dole Umaimah tayi kuka saboda tayi rashin miji na qwarai amma nasani bazai fini sonta ba kuma zanyi iyakar qoqarina naga na bata farin ciki fiye da wanda yake burin bata zan riqe maka yayanka kamar nawa har qarshan numfashina Sulaiman Allah ya gafarts maka" Yana mgnr yana kuka da shishi kamar qaramin yaro tunda yake baitabajin mutuwar data girgiza shi kamar ta Sulaiman ba ko mutuwar yayanss biyu batayi masa dukan mutuwar Sulaiman ba musamman idan ya kalli yaran sai yace “yanzu fah yanason rayuwa dasu Allah ya karbi rayuwarsa ko? Meyesa a duniya mutanen kirki basa dadewa?" Ya tambayi kansa tare da kwantar da yaran da sukayi bacci a gefensa ya ja blanket ya rufesu ya tashi ya dauro alwala yayi sallar Isha yayi shafa'i da wuturi yaci gaba da addu'a rabin addu'ar tasa ga Sulaiman ne yana kuka yana roqon Allah ya bashi hqr da kyawawan halaye da kyakkyawar mu'amala irinta Sulaiman. Bayan ya gama ya fita ya nufi kitchen domin dauko fresh milk sukayi clear da ido ido cikin ido amma sai ta
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111