Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 101

Chapter 101

Gidan Uncle Return Complete Hausa Novel 1,206 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ina roqonka kamar baka amsawa Allah banaso ka kamani dason matar wani kafi kowa sanin banida qarfin raba zuciyata da ita a jinina take yawo" bude qofar motar da akayi ne yasashi dagowa da idanunsa da har sun dafe saboda kunan zucci ya zubasu akan Yusuf yayi murmushi don yasan kukan me yake Hameed bashi da damuwar data wucce Umaimah a rayuwarsa gashi Umaimah tayi masa nisa. Dafashi yayi yace “mutumin ya kamata ka cire bloody dinnan taka aranka ka nemi wata yar baby ks aura ka qarasa rayuwarka da ita" wani kallo ya watsa masa wanda ya tilasta masa rufe bakinsa jikinsa har tsuma yake saboda bala'i yace “waikai anyama kuwa kasan meye so a rayuwarka Yusuf to bari kaji idan baka sani ba ka sani inasonta kuma ina fatan na mutu da soyayyarta wlh nayiwa zuciyata alqawarin bazan sabawa farin cikinta ina sani ba Umaimah tana sona jiya nagano soyayya ta da tausayina har yanzu a cikin idonta Maliha ta fadamin tun jiya take tambayarta Ina Ina me nakeyi har turowa tayi tazo taga lfyta Umaimah tana kishin ganin nayi tarayyah da wata mace saboda haka bazanyi ba har abada zan hqr na rinqa azumi har zuwa lkcn da Allah zai yankemin ya kawomin mafita amma bata hanyar aure ba na hqr da aure har abada indai bada bloody bane kuma koda banda rabon sake aurenta inason na mutu da soyayyarta saboda itama nasan da tawa zata mutu wlh Yusuf na tsani mutumin nan da yake ganin kansa wai mijinta kayyy! kayyy!! kayyy!!! badai miji ba dan riqon qwarya wai harma ciki yayi mata kuma ma harta kusa haihuwa" Ya mgnr yana dafe kansa yana jan zuciya yace “babu komai qaddara ce da kuma rabo wannan kadai ya isheni ishara" ajiyar zuciya Yusuf yayi cikin tausayin abokin nasa yace “kayita addu'a Allah yana sane dakai zai kawo maka mafita yawwa kaji kuwa cewa matarka tana gdan mahaukata?" Dagowa yayi da sauri yace “wa kenan?" Murmushi yayi yace “matarka data rabaka da kowa kaqiji kaqi gani matarka data rabaka da farin cikinka jiya nake samun lbrn ta haukace sai tonawa kanta asiri take har tana fadin yanda tayi ta rabaka da Umaimah da bayan ka daketa ka saketa komawar da tayi akan a haukata Umaimah yanda bakai ba wani ma bazaiyi sha'awar rayuwa da ita ba taje ta hado abinta tazo tayi ita kuma Umaimah tayi aure wannan dalilin da kuma addu'a sune suka mayar Mata da abinta kanta" qwafa yayi yace “narasa me muka tsarewa mutane kowa yake nufin mu da sharri Allah shine muka dogara dashi kuma shine abin dogaron bloody" yana mgnr yana dafe qirjinsa yace “bani maganina nasha qirjina ciwo yakeyi" Haka sukayi sallama Yusuf ya tafi kwanaki biyar tsakani ya gama dukkan shirye²nsa ranar daya cika sati da dawowa daga India ya shirya sai birnin California na qasar amurka inda suka bashi katafaran gdan zama da zundumemiyar mota da matsayin me girma a world Bank. ******* Sati hudu da rasuwar su Shurafah Umaimah ta haifo yaranta biyu mace da namiji kyawawan gaske farare tas masu kama da ubansu fari irin na fulanin Yola wai zokuga murna gurin D.S anyi yaya shine yayi musu huduba da Zulaiha da Kabir aka mayarwa da Hajiya chibinar ta sannan yasa wa namijin sunan mahaifinsa aikuwa yaran sunga gata amma shi yayi musu inkiya da Nawwas da Nawwarah ranar suna tazo akasha bidiri abu gwanin sha'awa har kuka Umaimah tayi saboda gatan data samu gurin danginta da dangin mijinta goga Hameed ma da Daddy ya tura masa hoton yaran yayi murna sosai yaji qaunarsu har cikin jininsa ya rinqajin dama shi ta haifawa yaran bayan taro ya watse da kwanaki uku suna kwance da Sulaiman aka kirashi a waya ake fada masa anyi musu rasuwa a Adamawa qanin mahaifinsu ya rasu yaji mutuwar sosai don zaune ya tashi ya hada kai da gwiwa daqyar ta lallabashi suka kwanta da asuba ya tashi ya shirya lkcn har qaninsa Nura yazo daukarsa zasuyi sammako itadai Umaimah hakanan tarinqa jin gabanta na faduwa daqyar ta bari yayi kissing yaran ya rungumeta a jikinsa ya fita har ya fita ya dawo ya kirata ya janyota jikinsa yace “amana nabar miki yarana ki rayu dasu cikin aminci inasonki Umaimatu"......... *UMMUH HAIRAN CE...✍🏻* [2/3, 8:45 AM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *_GU_* Duk da faduwar da gabanta yakeyi hakanan ta qwaqulo murmushin qarfafa gwiwa tace dashi “zaka dawo ka samemu cikin amincin Allah" yayi murmushi tare da kissing din bakinta ya fita da sauri suka dauki hanyar Adamawa. Ta jima a tsaye a gurin daya tafi ya barta tana jera masa addu'ar dawowa lfy kafin ta koma cikin gdan lkcn twins dinta sun tashi dake tanada meyi mata raino ta basu sukasha ta miqa Mata su ita kuma ta kwanta har yanzu ciwon jikin haihuwar bai saketa ba sannan D.S ya kuma tara mata gajiya da D.S da Hameed batasan waye yafi wani jaraba ba sauqinta daya shi baya dadewa kuma penis dinsa batada girman ta Hameed amma jiya ta fada duk da bai shigeta ba saida yasan yanda yayi ya samu gamsuwa da ita sosai. Wajen qarfe daya taji wayarta tana ring ta shiga dakin da sauri ta daga ta kara a kunnenta tace “Allah ya taimaki mijina badai har kunje Yola ba naga tfyr da nisa sosai” ajiyar zuciya taji anyi gabanta ya yanke ya sake faduwa kafin tayi mgn aka katseta da cewa “matarsa ce ke?" Cikin in...Ina da tashin hankali tace “a...eh ni... Ina matarsa ce" me mgnr ya kuma cewa “sun samu hatsari ne a hanyarsu ta zuwa Adamawa amma yanzu haka suna asibitin qashi na dala shine yace a kiraki a fada miki” wani salati ta saki tace “way... wayyoh Allah... Ni Umaimatu amma dai bai mutu ba ko?" Bata iya jiran amsar dazai bataba ta kashe wayar cikin tashin hankali ta durqushe a gurin qirjinta yana tsananta bugu jikinta yana wata irin rawa daqyar ta iya sake daukar wayarta ta kira Daddy tana kuka tana cewa “Daddy Abu Nawwas Daddy karya mutu don Allah ya barni ka hanashi mutuwa Daddy..." Saurin katseta yayi da cewa “ya salam waye ya fada miki Umaimatu bafa shi bane qaninsa ne" Allah sarki baiwar Allah sai kuwa ta sauke ajiyar zuciya tace “Allah na gde maka daba mijina bane" hawaye Daddy ya share cikin rawar murya yace “ki... Kiyi hqr haka Allah ya tsara miki ga Hajiya nan zuwa da yayarku Zahrah zasu tayaki zama kafin yaji sauqi a dawo dashi kada kice zaki fita daga gdan nan" yana fadin haka ya kashe wayar bata samu damar yin tunanin komai ba taji shigowar motoci gdan aikuwa batasan sanda ta zabura ta miqe tayi waje a guje ba ambulance tagani da qananun motoci uku tayi wajen ta tsaya tana rarraba idanu kamar mahaukaciya zuciyarta takasa tuna komai Daddy da Abba mahaifin Sulaiman taga sun fito sai wata motar Dawood ne yayan Sulaiman da Nazir qaninsa dayar kuma Hajiya Sa'adatu ce da qannansa mata biyu sai ma'aikatan asibitin da suka fito suka bude ambulance din suka janyo wani dogon abu da mutum kwance akai jini sai diga yake ta qasan gadon daukar gawar. Daddy yana qoqarin riqeta amma ina da tayi wata alkafura ta dira gabansu

Table of Contents

Chapters

111 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
  93. 93 Chapter 93
  94. 94 Chapter 94
  95. 95 Chapter 95
  96. 96 Chapter 96
  97. 97 Chapter 97
  98. 98 Chapter 98
  99. 99 Chapter 99
  100. 100 Chapter 100
  101. 101 Chapter 101
  102. 102 Chapter 102
  103. 103 Chapter 103
  104. 104 Chapter 104
  105. 105 Chapter 105
  106. 106 Chapter 106
  107. 107 Chapter 107
  108. 108 Chapter 108
  109. 109 Chapter 109
  110. 110 Chapter 110
  111. 111 Chapter 111
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});