Chapter 87
Chapter 87
fifita farin cikinka fiye da nawa" Tana gama fadin haka ta miqe zatabar gurin yayi saurin riqeta yace “nifa bance miki aa ba bloody kawai dai na fada miki raayi nane bazan yarda na batawa farin cikina rai ba amma da sharadin zaki rinqa sa babban hijjab har qasa sannan zakisa safa da niqaf sannan kisa glass a idonki idan kin yarda to nima na yarda" shiru tayi tana nazarin kalamansa Allah ya sani bawai hijjab ne bataso ba amma tanajin sanya niqaf dinnan garama glass din dama ko gari banza tana sawa" Bai jira abinda zatace ba ya miqe ya nufi sama bai jima ba ya fito ya miqa mata hijjab dinta yace “ tashi muje ki rakani unguwa karba tayi ta sanya ta nufi dakin qasan ta dauki takalminta dana Shurafah tasa mata shikuma ya dauke suka fito “A'uzullahi minasshedanur rajim" taji ya furta ya dauke kansa tayi saurin kallon gurin idonta yakai kan Salma dake nufosu da sauri ta zuba mata ido gabanta na faduwa a zuciyarta tana furta “ La'ilaha illah anta subhanaka inni kuntu minazzalumin" qarasowa tayi gabanta tana wani cin magani ta tsaya tare da riqe qugu saurin sakin fuska Umaimah tayi tace “yi hqr amarya banzo mun gaisa ba ko koda yake kece ya kamata kizo ki kwashi gaisuwa na qara miki haske akan mijin namu...." Dora hanunsa yayi a bakin Umaimah yajata da sauri yasata a mota ya kama hanun Shurafah ya sata a baya ya juyo zai shiga tayi saurin cewa “ba gurin kucakar matarka nazo ba gurinka nazo ka fadamin matsayina a gdanka ka tashi ka fice tun asuba naga dawowarka tun shidda saura amma baka waiwayeni ba saboda wulaqanci kaje kuna ha'inta ta da wannan makirar matar...." Saurin dafe kuncinta tayi saboda jin saukar mari ta dago ta dubeshi ya nunata da yatsa yace “kiyi da Abdulhameed amma kada ki sake ki taba darajar iyalina don irinki dari kuzame bazasu iya yin daidai da ita daya ba saboda haka ki dawo hayyacinki baa bariki kike ba kuma dole kiyi biyayya ga shugabancinta saboda nima da kika liqemin na daukoki na kawoki gdana kike sani amai da tashin zuciya a qarqashin masarautarta nake rayuwa itace ni itace rayuwata karki qara" Ya fada yana kada mata yatsa ya bude motar ya shiga ya barta da dafe kunci tana zubar da wani hawaye me ciwo yaja motar da gudu ya nufi get megadi ya bude masa ya fice da gudu ya lula hanya yana huci kamar kububuwa itadai Umaimah bata kulashi ba saboda batama lura da abinda ya faru tsakaninsa da Salma ba kai tsaye wani babban shopping plaza suka shiga a zoo road ya rinqa jidar mata dogayan riguna da hijjabai da takalma sai ita da yarta saida suka koma daya gefen ita kuma ta fara zabarwa Nihal da Maliha suma sukaje yayi total din kudin ya biya suka fita mota suka shiga yaja suka nufi hanyar gda tace “don Allah ka kaini muyi sallama da Aunty Jameelah gobe zata tafi" kada mata kai yayi yace “kya kirata a waya amma bazakije gda ba kadan Hajiya take jira ta rabamu" Bata kuma ce masa komai ba suka nufi wani gurin shaqatawa suka yini suna hutawarsu a gurin sai gaf da magrib sannan suka nufo gdan suna shiga sukaga motoci a gdan har biyu yayi parking da sauri ya tambayi me gadi yace “Ibrahim su waye sukazo gdannan?" Shafa kansa yayi yace “ranka ya dade Hajiya qarama ce tayi baqi tun rana" bai jira ya sake cewa komai ba yaja suka qarasa parking ya budewa Umaimah ta fito ya fara lodar kayan yana shiga dasu ciki ita kuma ta zube a kujera yace “ina zuwa" ya fice part din Salma ya nufa ya bude qofar ya shiga a fusace ya fara kallon mutanen dake parlourn mazane biyu sai mata biyu ita ta uku duk sunci uban attach sai zuqar shisher sukeyi kallonsu yayi daya bayan daya koshi da yake Shuwa baisan dadin shisher ba saboda baiga anasha a gdansu ba ya hadiye wani takaici yace “ke mahaukaciya uban waye ya baki damar shigomin da qartin banza gdana?" Kallonsa tayi a cikin maye tace “au saina fada maka idan zanyi baqi nida gdan mijina?" Daga mata hannu yayi yace “waye mijin naki Allah ya kiyaye am ba wannan ne ya kawoni ba ki sallami baqinki su tafi kuma daga rana irin ta yau kada ki qara shigomin da wani qaton banza gdana saboda ba gdan tsoho bane matata bata taba shigomin da mutum gdana ba saida izini na kuma ita batada wani ma namiji da zata shigo dashi saboda nine dan'uwanta dazan kai Mata ziyarar kuma nine mijinta wlh idan kika kuskura kika takamin doka to zakisha mamaki don saikin koma gda kinci gaba da zawarci saboda shine ya karbeki" Shigewa yayi cikin dakin daya kwana ya dauki abinda zai dauka ya fito lkcn baqin duk sun miqe yace “saida safe bazan iya kwana a cikin qazanta ba" ficewa yayi bai jira amsarta ba ya nufi bangaren Umaimah a parlour ya tarar da ita ya zube takardunsa yace “waccan tunkiyar naje na tarar ta shigomin da qarata gda saboda nonon akuya tasha to wlh idan ta qara a bakin aurenta danni ba ayimin hakika da bunsuru ba da zata mayarmin da gda tasha idan ta saba ni ban sababa zuri'ar mu ma bamuda yawa balle ayimin hauka a gda" Yana gama sababinsa ya haye sama ya cire kayansa ya shiga wanka ya fito ya shafa mai da turarukansa ya sanya gajeran wando ya sauko qasan har lkcn tana kwance a inda ya barta ya matsa ya zauna kusa da ita yace kinyi sallah kuwa miqewa tayi tace “aa yanzu dai zanyi" daukar Shurafah yayi ya kwanta a inda ta tashi ya dora yarinyar a qafarsa yanayi mata macilili tanata dariya abinta ita kuma ta haura sama tayi sallah ta kwanta saboda bacci takeji sosai. Gajiya yayi da jiran fitowarta ya miqe suka haura saman ya taddata kwance tana bacci ya kwantar da Shurafah a gadonta ya haura gadon ya kashe fitilar tayi saurin miqewa tace “aa wlh haram bloody bazai yuwu ba tashi maza ka tafi gurin matarka ni na yafe kayi mata komai ma amma bazaayi wannan zunubin dani ba" miqewa yayi ya nufota ta kauce yace “ke matsala ta dake rashin uzuri wlh idan naci gaba da zama da matar cen zan iya sabauta ta dan idan tace zatayimin rashin kunya dukan tsiya zan yiwa shegiya ta barni naji da famin ciwon zuciyata da qaddararren aurenta yayi mini ma mana" Toshe kunnenta tayi tace “ nikuma wlh saika tafi gurinta bazan taba yarda da wadannan kalaman ba sati guda na baku ku raba raini sosai kowa yasan kowa" wani kallo yake Mata na kin rainamin hankali ma yace “dawa zanyi sati gudan kuma dawa zan raba rainin?" Bata damu da kallon da yake Mata ba tace “da matarka daka auro mana meye amfaninta idan baka barje guminka ba million daya da rabi fa ka bata banda kyautar qauna da tasha a gurinka" daukan wayarsa yayi a fusace ya shiga dannan wasu numbobi can taji alert a wayarta yace “wlh bantaba bawa Salma ko ficika ta ba da sunan kyauta hasalima sau
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111