Chapter 92
Chapter 92
masa wata damuwa ba yace “Eh Allah ya sauketa lfy Hameed bata mutu ba Allah bai cika maka burinka na kasheta da kayi niyyar yi ba banda abinka Hameed ai ko baka batta cikin halin ciwo ba takardar sakin daka batama shaida ce ta baka buqatar zama da ita to yau dai qurunqus dan kan barya Hameed aure babu tsakaninka da Umaimah kuma aure indai irin nakane to Umaimah ta barshi har abada wlh indai irin zaman da tayi a gdanka ne gara nasata a gaba nayita kallonta" duk cikin kalaman na Daddy babu abinda ya fahimta ya dago zaiyi mgn Hajiya dake fitowa ta daki bakinsa har saida ya fashe tace “sannu da zuwa tatacce dan'uwan koko ubanme kazo fada mana kazo ka jaddada mana ka saki Umaimah saki biyu ne ka cike mata ya zama uku?" Murmushi tayi me ciwo tace. “Ai dama kayi zamanka gurin matarka abar qaunarka basai kazo ba saboda zuwan naka bashida wani amfani" dagowa yayi cikin tashin hankali da kidima yace “na roqeku badon halina ba ku taimakeni ku warwaremin qullin nan wlh fahimci me kukeso kuce ba" kallonsa Daddy yayi kallon tsaf yace “waye Abdulhameed Adam Hameed Shuwa ne?" Dagowa yayi yace “nine Daddy" ya kuma cewa “wace Umaimah ne?" Sake dagowa yayi yace “qanwata ce kuma matata ce Umaimah" murmushi Daddy yayi me ciwo yace “to tunda hakane karanta wannan takardar rubutun waye a jiki?" Miqa hanunsa yayi jikinsa na rawa ya karbi takardar daya rubuta da manyan kalmomi _“NI ABDULHAMEED ADAM HAMEED SHUWA NA SAKI MATATA UMAIMAH SAKI BIYU BATARE DA WANI DALILI BA_ Tashin hankali wanda baasa masa rana wata uwar zabura da yayi yayi cilli da takardar yana ja da baya yana girgiza kai yanason bude bakinsa amma ya kasa wani mugun jiri yakejin yana fuzgarsa kuma ya kasa tsayawa da tafiyar da yakeyi da baya da baya Daddy ne ya miqawa Hajiya Shuraif dake hanunsa ya tafi da gudu ya ruqoshi yana dafe da kansa dake sara masa yace “rur.. rubuta nane Daddy amma yaushe na saki matata ni da kaina na saketa Daddy aa wlh bani bane"........ _Kuyi hqr da wannan banida charge kuma inason muyi fira_ *UMMUH HAIRAN CE...✍🏻* [1/31, 8:55 AM] UMMUH HAIRAN CE...✍🏻: *GU* Yana fadin haka yayi baya luuuuuu cikin fitar hayyaci ya dafe saitin zuciyarsa data daukar masa wani mugun zafi yaci gaba da cewa “ya yama zaayi kuce na saki matata me tayimin dazan saketa bayan itace rayuwata Daddy koda Umaimah yankar jikina takeyi tanaci wlh bazan iya rabuwa da ita ba Daddy ku duba lamarin nan kuyimin rai wlh Allah Daddy bansan sanda na rubuta mata takardar nan ba bansan meye ya faru dani daran jiya ba a dakin Bloody na kwanta amma dana tashi da safe saina ganni a dakin Salma wlh Daddy bansan komai akan takardar nan ba ku dabeni kuji qaina ku tausayamin kada ku rabani da matata” Yana mgn muryarsa na kakkatsewa saboda tashin hankali kamashi Daddy yayi ya zaunar dashi a kujera ya dora masa Shuraif a cinyarsa yace “abinda ya faru ya riga ya faru ka saki Umaimah a daren jiya ta haihu a daren jiya ta tsarkaka daga iddarka ga danka nan kasa masa albarka dama rabonsa ne yasa ta koma gdanka nayi maka shisshigi nayi masa huduba da sunan marigayi babanku da fatan banyi laifi ba don kai yanzu hukuma ne sai lallashi” Shigewa Daddy yayi daki ita kuma Hajiya taja qofar dakin da Umaimah take ciki ta datse da mukulli ta nufi kitchen tafi awa daya a kitchen din ta fito ta tarar dashi a zaune tayi mamakin ganin yanda ya rungume Ahmad Shuraif a qirjinsa numfashin sa yana sarqewa bata kobi takansu ba ta shige dakin hakan ya bashi damar miqewa yana hada hanya ya nufi cikin dakin ya tsaya a bakin qofar ya zubawa Umaimah manyan idanunsa da suka kada sukayi jawur tana kwance nannade da blanket amma yana jiyo shassheqar kukanta daqyar ya iya jan qafarsa ya matsa ya zauna a gefen gadon yana jiyo sautin muryarta tana maimata kalmar innanillahi wa Innah ilaihir raji'un hanu yasa ya janye bargon data rufa dashi ta dago da sauri suka hada ido tayi saurin kawar da nata yakai hanunsa zai ruqo nata tayi saurin make hanunsa tace “kada ka tabani Hameed na haramta gareka har abada insha Allahu sai Allah ya sakamin wannan baqin cikin daka qunsamin Hameed nayi danasanin saninka a rayuwata bantabajin tsanarka da tsanar zuri'ar dake tsakanina dakai ba sai dama ashe haka so yake meyasa ka cusamin sonka da tausayinka bayan kasan bazaka rayu dani ba Allah ya isa tsakanina dakai Hameed kuma wlh azeem idan baka daina bibiyar rayuwata ba zan gudu ku nemeni ku rasa kowa ma ya huta” Fitowar Hajiya ne yasata tayi shiru da kukan da takeyi ganin a zaune yayi mugun qonawa Hajiya rai ta nunashi da hannu tace “tashi ka fita daga dakinnan” dagowa yayi yace “amma Hajiya ya kamata ku tsaya ku fahimceni waini meyasa kullum ni me laifine bakwa yimin uzuri Hajiya kada idonki ya rufe kema kamar yanda na bloody ya rufe take caccakamin maganganu masu ciwo son ranta kuyimin adalci kafin yanke hukunci naji ni me laifine amma ku tsaya kuyi tunani da hankalina zan saki Umaimah har saki biyu wlh Hajiya ko maqiyina yasan inayiwa bloody son da bazan taba yiwa wata mace ba a duniya bazan iya rabuwa da itaba itace rayuwata Hajiya itace farin cikina” Wani murmushi Hajiya tayi me ciwo itafa ta fara tantamar hankalin dan nata saboda kalaman gaba daya babu hankali a cikinsu dauke yaron tayi daga jikinsa ta kama hanunsa tace “miqe ka tafi gdanka safiya ce yanzu matarka tanacan tana jiranka ka cika mata burinta tayi nasara ta rabaka da matarka me qaunarka domin Allah ga gidannan ku zauna ku kadai" tana fadin haka ta turashi waje ta rufe qofar. Durqushewa yayi jikin qofar yana kiran sunan Umaimah sai yanzu yaji wasu zafafan hawaye sun zubo masa ya dade a gurin ganin babu wanda zai fito daga dakin yasashi miqewa jiri na dibansa ya fita ya fada motarsa yaci gaba da kukansa yana buga kansa da sitiyarin motar jin abin yake kamar almara wai shine ya saki Umaimah saki har biyu to me tayi masa meye ya hadasu yaushe ma yayi sakin kuma yaushe ya rubutashi kai ina bazai taba yarda ba wannan gonarsa akeson shiga ayi masa barna. Daqyar ya iyajan motar ya nufi gdan abokinsa Yusuf dake asabar ce yana zuwa ya tarar dashi tsaye tare da megadi mamakine ya cika Yusuf saboda rabonsa da Hameed tun lkcn daya fada masa zai auri Salmah ya fito ya nuna masa bai amince ba so ko waya basayi kamar aikin asiri ya daina kulasa ko wayarsa ya daina dagawa. Takawa Yusuf yayi har motar ya bude ya shiga yace “yadai mutumin yau amintakar ce ta motsa asirin ya sakeka kenan...”hadiye mgnr yayi ganin yanda jikinsa yake bari haqoransa suna haduwa ya damqi hanun Yusuf yace “Yusuf wai su Daddy ne sukace wai nine na saki Umaimah da hanuna jiya da daddare har saki biyu yanzu shikanan bloodyna ta haramta gareni...." A tsorace Yusuf ya dago yace “kamar ya wai akwai wanda ya isa yace ka saki matarka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92
- 93 Chapter 93
- 94 Chapter 94
- 95 Chapter 95
- 96 Chapter 96
- 97 Chapter 97
- 98 Chapter 98
- 99 Chapter 99
- 100 Chapter 100
- 101 Chapter 101
- 102 Chapter 102
- 103 Chapter 103
- 104 Chapter 104
- 105 Chapter 105
- 106 Chapter 106
- 107 Chapter 107
- 108 Chapter 108
- 109 Chapter 109
- 110 Chapter 110
- 111 Chapter 111