Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 83

Chapter 83

Raina Kama Book 2 Complete Hausa Novel 1,200 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

damuwar rashin amsawar tasaba a fuskar Harun, dan yariga ya saba da halinsa. Saidai idonsa k'uri akan Abdurraheem dake cinyar Galadima d'in yana barci, mik'ewa yay yana fad'in, “my son zo mu gaisa ko?”. Ganin haka nima nayi azamar mik'ewa nakai ga Galadima kafin shi ya isa, na d'auke Abdurraheem d'in ina fad'in “ai barcima yake ranka ya dad'e”. Ba Harun ba hatta da Galadima saida yaymin kallon mamaki, nakoyi cid'in-cid'in da fuska yandama bazaice nabama Harun d'inba. Baki ya bud'e kamar zaice wani Abu saikuma yay shiru yana kauda kansa daga kallona, nima saina ta6e baki ina barin falon da harar Harun ta gefen ido. Gaban Harun ya fad'i, mi yarinyarnan take nufi?...... Kafin ya lalubo amsar ya tsinkayi maganar galadima yana cewa, “sorry Harun, kasan har yanzu a tsorace take, duk wani motsinsu akan idontane”. Murmushin basarwa harun yayi, yace, “ai dolene hakan ranka ya dad'e, abinne akwai tsoratarwa, wlhy jiya tashin hankalinnan ne yasaka azababben ciwon kai rufeni, shiyyasa ko ganina ba'ayiba, yanzu police d'in ina suka samosu?”. “humm” Galadima ya fad'a cikin tsananin taune lips da k'unar zuciya, ya bud'e baki a hankali zaiyi magana nida ke bayansu basu saniba nai saurin tareshi da fad'in “a hannun wasu munafukaine ranka ya dad'e, ai koni daza'a bani baiwar nan da aka kama da yaran wlhy saina tsoma kanta cikin drum d'in ruwa harsaita daina Numfashi zan barta, kafin sannan kuma nagamajin labarin Wanda ya sakata, amma shi my boss ai a station suka zauna har aka kawo yaran, badasu akaje farautarba”. Tsuramin ido Galadima yayi cikin tsagwaron mamaki, miyasa to zanzo na kasa na tsare dukkan wani motsin Harun d'in? ya kula satar yaran tana Neman ta6a tunaninta takasa banbance Wanda zata zarga, ai Harun yawuce ya 6oye masa wani sirri na sashen rayuwarsa, tun da babu abinda bai saniba na baya, saidai abinda ba'a rasaba kam, danne ransa yayi ya nuna hakane, yabari har Harun d'in ya tafi sannan yaji dalilinta. Ina kallon Sassanyar ajiyar zuciya da Harun ya sauke a 6oye, sannan yace, “ai police d'in sun cancanci Babar k'yauta, shiyyasama na shirya musu ita, sunyi aiki irinnan jaruman masu tsaro”. “hakane wlhy ranka ya dad'e ”. Na fad'a cikin murmushi. Dukfa yanda Harun yaso bugar cikin Galadima yaji yanda abun yake, na kafa na tsare, dayayi tambaya nike bashi amsa, saiya d'auka kodan Galadima bashida lafiyarne shiyyasa bai iya amsawa, tun da tunda ya shigo baice k'ala ba, kuma yasan yanayin ciwonsa, a baya ma shikan bashi taimako, baidai tsinci komai ba yay mana sallama ya fita, da k'udirin anjima ma zai dawo ne. A sace na raka bayansa da harara, sannan na kalli Galadima na basar, dukda kallon tuhuma dayake jifana dashi kuwa. Wani farfesun na sake zuba masa na mik'a masa. Batare da ya kar6aba cikin k'ank'ance idon bala'i yace, “mikikayi haka? kinsan waye Harun a wajena?”. Kaina na girgiza masa. Yaja tagwayen tsaki yana hararata, “halan satar yaranki yafara shafar tunaninki ne? kina tunanin akwai abinda Harun zai iya gazaji daga sirrina?”. Na d'an ta6e baki ina jawo teble d'in gabansa, na d'ora bowl d'in dana zuba farfesun, baki ya bud'e kamar zaiyi magana saikuma yay shiru. nima bance uffanba na ajiye masa sannan na koma k'asa Na zauna na zuba sabon kunu nahau sha. Kwafa yayi, yace, kinma maidani d'an iska ko?”. “Hummm” na fad'a kawai, naimasa kallo d'aya “yalla6ai wani karatun akan barsane a yanda yazo, sai idan lokacin fasaarashi yayi amasa fashin bak'i, nasan darajar alak'ata dakai batakai koda rabin tsakaninka da Harun ba, domin ni alak'ar wucin gadice ta had'amu, k'iris ma ya rage ta k'are, saidai inason nabama y'ay'ana kamar yanda ka fad'a kariya koda sau d'ayane a rayuwarsu kafin na barsu, dan haka maida wuk'arka a kube, lokacin zareta baiyiba, sometimes kalmar Mahangi da mai hange takanyi kamanceceniya, dan bakowa ke iya rarrabata wajen fasaara ba, amma kalmomine duka masu harshen damo, wani k'alubalen saida tunanin mai zurfi, wata k'oramar ruwan mutanen dake zagaye da ita sukanyi imani bazata balle harta cisu ba, saboda sun yarda sud'in masuntane da kullum suke rayuwa cikin wannan k'oramar, abin mamaki saikaga wataran an wayi gari da mutanen da muhalansu duk wannan ruwan ya had'iyesu, abinda basu ganeba bakowacce irin alak'a bace ake kulla amana da ita, wani farin idan yashiga cikin fari banbance k'arkonsa saidai ALLAH”. Tashi nayi nai shigewata bedroom d'insa. A fusace shima ya mik'e zai bini, kad'an yarage ya zubda farfesun dana ajiye masa, ALLAH dai ya kiyaye ya shallakesa ya wuce. Hucin mutum kawai naji a bayana, hakan yasani waigowa da sauri, hannu ya dunk'ule zai kaimin naushi, nai azamar fad'awa saman gadon ina zaro ido waje, a lallai Abu ya girmama, nikuma miye nawa da zai sauke fushinsa a kaina? nai maganar a zuciyata. Janye hannunsa yayi yana ciza lips d'in sa da k'arfi, idonsa dukya kuma rinewa, ya dunk'ule hannun ya daki d'ayan dashi, muryarsa har rawa take yace, “Miyasa zaki kuma hargitsan tunani ne? Minene laifin Harun shikuma? kuna nufin duk Wanda na yarda dashi shine mak'iyina? Kai impossible wlhy, Munaya wakikema aiki a kaina? ya rankwafo kaina, kaikace cinyeni d'anya zaiyi, saikace zaki yaga bandar nama, da k'arfi yace, “bazaki sanarmin ba saina k'arar da numfashinki ne waishin Ubanwa ke fad'a miki wad'annan maganganun da kike d'aureni dasu a ko yaushe?!!!”. Ya k'are maganar cikin tsananin tsawa da k'araji. Ba k'aramin firgita nayiba, badan karnayi k'arya ba danace har wutar bala'i Nagano a idonsa tana ci, wannan bawa akwai zuciyar tsiya, idan zai zama jami'in tsaro da k'asarmu ta amfanu da yawa......... Da k'arfi ya girgizani, saboda ganin saboda rainin wayo tunanima na tafi.......... A firgice nace “yi hak'uri zauna zan fad'a maka”. na fad'i hakanne dan kawai ina ganin itace mafitar dazan nema ya fasa had'iyeni. a mamakina kuwa saiya tashin ya zauna yana dafe k'irji hawaye nabin kumatunsa. Tsantsar tausayinsa ce ta kamani, na tashi na d'akko ruwa na dawo kusa dashi na zauna, addu'oi na shiga tofawa a ruwan, yana zaune dafe da kansa, da alama kuka ma yakeyi, dan ajiyar zuciyar da yakeyi ta yawaita. Saida na gama na dafa ka fad'arsa, tamkar bazai d'agoba saikuma ya kalleni, ruwan addu'ar na basa, babu musu ya kar6a ya shanye, duk da baima san mita bashiba, idanma poison ne dai gara ma yasha ya mutu ya huta. Mintunansa biyu zuwa uku dasha yafara sauke ajiyar zuciya mai k'arfin gaske, saiya zame kuma ya kwanta, kafin kacemi barci ya saceshi a haka. nima ajiyar zuciyar nayi ina girgiza kai da share hawayen dake silalomin, ina rok'on ALLAH ya kawoma wannan bawan nasa sauk'i da rangwame cikin gaggawa da warwarewar al'amura. Dagashi har yaran tausayi suke bani, nayi zurfi a tunani wayarsa tayi ring, kamar zan share saikuma Na tuna maybe Momma ce, tashi nayi zuwa inda wayar take, aikam dai itace, nayi picking jiki a sanyaye, dan tunanina kota gamajin komai, amma sainaji sa6anin haka, da y'ar raharta ma tace, “Muh'd duk hidimar sunance haka?”. “Uhm Momma bashi bane nice”. “a'a d'iyata kece?”. “eh Momma, kuna lafiya? ya jikin Abie?”. “Alhmdllh d'iyata, ya k'arfin jikinki kema? ina yaran?”. Gabana ya fad'i, Na had'iye wani yawu da k'yar, cikin in ina nace, “lafiyar kowa k'alau Momma, shima y... yana barcine”.

Table of Contents

Chapters

92 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});