Chapter 79
Chapter 79
zuciya ba zai iya bashi taimakon gaggawa, shikuma Dr jalal ya fara kar6ar Abdurraheem dake hannun inno, yan d'ube-dube, yayi Na tsawon lokaci kafin ya ajiyeshi ya kar6i Na hannun mai Martaban, shima yagama duk abinda ya dace ya kar6i Amaturrahman a hannun papi, ajiyar zuciya ya sauke yana fad'in “Alhmdllh duk basu mutuba, allurar barci mai k'arfi sosai suka musu, shiyyasa numfashinsu yay nisa sosai, danta musu k'arfi da yawa, amma idan kuka saka kunne nawasu mintuna saitin jikin zuciyoyinsu zakuji suna motsawa kad'an-kad'an, sai dai ta wannan tafi yin k'asa sosai gaskiya”. Ya nuna Abdurraheem dake hannun inno. Su mai Martaban suka sauke ajiyar zuciya suna hamdala ga ubangiji. A cikima Akash nata iya bakin k'ok'arinsa ganin Galadima ya farfad'o, Ahaka su mai Martaban suka k'araso cikin d'akin d'auke da yaran a hannun, Munaya Na gefen Galadima an lullu6a mata bargo batasan wainar da ake toyawa ba, dan barcin nata shine mafita fiye da zama ido biyu. A gadon suma yaran duk aka shimfid'esu, Dr jalal yad'an musu dabarun likitoci sauran kuma aka barma ubangiji ikonsa Na jiran farkawarsu. Hankali kuma duk saiya koma ga Galadima da aketa fama. Har aka kirayi sallar Asubahi babu amo babu labari akan farfad'owar tasa. daga k'arshe dai Akash saida ya kira likitan Galadima na zuciya. Shiya dunga fad'ama Akash d'in yanda yadace yayi, lokacin shiga salla ya saka su mai Martaban fita masallaci dole, sukabar Akash da Dr jalal dake taimaka masa suna aikinsu, saisu Aunty Mimi da suka kasa matsawa ko nan da can, Sauban ma da k'yar su papi suka lalla6asa yabisu salla. Har gari ya waye sashen Galadima ya cika da manyan masarautar irinsu mama Fulani matan Sarki da sauransu Galadima babu wani bayani, zuwa yanzu ma wasu sun fara tunanin kodai yama mutu ana 6oyewane kawai. Wajen 8:00am Dr Yaseen Ali Modibbo babban likitan zuciya da akeji dashi ya iso, bisa kiran da Dr jalal ya masa yafad'a masa, dan abubuwan da sukaima Galadima bai farfad'oba Akash yakuma sanarma likitansa, shine yace tofa gaskiya Kodai asamo ainahin likitan zuciya ko kuma su taho dashi kafin cikar awanni 12, idan ba haka ba komai zai iya faruwa. A k'iyasin da sukayi cikin awanni 12 bazasu Isa india ba, tunda duk tsiya sai an samu jirgi mai tafiya, sannan ma kafin komai ya biyo baya. Hakkane yasaka Dr jalal kiran Dr Yaseen Ali Modibbo d'in, cikin amincin ALLAH kuma ya amsa zaizo d'in, saikuwa gashi ya iso. Canjama Galadima d'aki akayi, dukkan kayan aikin da Dr Yaseen yazo dasu aka shigo dasu, rufe d'akin sukayi suka duk'ufa su uku kansa suna taimakon Dr Yaseen d'in. Sun jigata kwarai da gaske kafin zuciyar Galadima tafara bugawa k'asa-k'asa, sai numfashinsa yafara fisga yana k'ok'arin fita. Duk ajiyar zuciya suka sauke. Suka cigaba da aikinsu, ana sakama Galadima wani abu a k'irji kamar dutsin guga, saiya girgiza sannan a cire, akuma maidawa. Basu barsa ba saida yasaki wata ajiyar zuciya mai matuk'ar sauti, harsu mai Martaban dake falo saida suka jiyosa kuwa. Wannan ne yasaka zukatan doctors d'in uku sanyaya, Dr Yaseen da Dr jalal suka had'a baki wajen fad'in “Alhamdulillah!”. Numfashin Galadima ya dawo dai-dai, amma sun masa allurar barci danya samu nutsuwa. Yaranma an kawosu ne Dr Yaseen ya kuma bincikawa, shima dai yace suna da ransu, amma Abdurraheem yanada ciwon zuciya shima, shiyyasa yafi sauran y'an uwansa jigata, ALLAH nema dai yay rabon yanada sauran numgashi, amma allurar tamasa k'arfin da zata iya dakatar da bugun zuciyarsa. Suma dai sun kuma samun taimako, musamman ma dai Abdurraheem da tausayinsa ya kama mutane da yawa a wajen. *_2:00pm_* Zuwa wannan lokacin Munubiya da mama Rabi'a da Ayusher Feena duk sunzo masarautar, Hakama baba k'arami da daddy, dan an sanar musu samo yaran da halin da galadima yake ciki. Amma saboda kara irinta Abba da innarsu Munaya sai suka bar su Baba k'arami da maman Fauziyya da mamansu yaa Hameed, maman Safara'u suka taho, sai innaro da gwaggo Safiyya. Ba'a barin wani bak'on fuska shigowa masarautar a yau, amma su sai mai Martaban yasa aka shigo dasu, basu samu ganin ko d'aya a cikin su Munaya ba, saidai Munubiya da aka shigar d'akin galadima inda Munaya ke kwance, Sauran kuma sun shiga ayarin y'an zaman jigum-jigum da jiran tsammani. Har zuwa wannan lokacin Galadima da Munaya babu Wanda ya farka, Amaturrahman da Abdurrahman dai sun farfad'o, sai dai suna kuka ko fita bayayi. Wanka laraba ta musu aka gasa musu jikinsu sosai, yau dai dole aka nemo madarar da Galadima bayason susha d'in, ita aka dama aka basu sukasha, aiko sun shata sosai dan yunwa sukeji, bayin ALLAH, rabonsu da abinci tun jiya da rana kusan I war haka d'in. Tausayinsu ya kama Munubiya dake basu madarar, tana yi tana sharar hawaye, da da farko nono inno tace ta basu, sai papi yace, “a'a kar ayi wannan gangancin, dan ba'asan abinda ALLAH zaiyiba wataran, ko akwai k'addarar aure a tsakanin yaransu, kar azo ayi Dana sani a watarar da baza'a iya maido wannan ranarba balle a gogo 6arnar da akayi”. Kowa ya gamsu da wannan magana, dan haka Muftahu yafita suka nemo madara shi da Saleem. Shine aka basu. Baiwar da aka kami da mutumin kuma suna hannun police, kuma kowa yaji cewar tana cikin bayin gidan wad'an da aka aminta dasuma sosai, saidai ba'asan ta wane sashe bace. Wannan Abu ya tsurar da zukatan Sauran bayin, dan dolene ya shafesu. Hankalin Uwargidan Sarki Sarauniya Zulfah (mahaifiyar su matawalle) a tashe yake, amma dayake ta iya takunta bazaka ta6a fahimtar haka ba, saima nuna tsantsar damuwarta akan lamarin da tayi fiye da sauran matan Sarki. dama kuma tafi nuna kulawarta ga Galadima kowa yasan wannan, shiyyasa babu Wanda yakawo wani Abu game da ita, saima wasu daban ake zargin. Munaya da Galadima sun farfad'o ne kusan time d'aya, amma Galadima ya riga Munaya, dama allurar awanni 4 kacal aka masa, da Sunan ALLAH a bakinsa ya farka, sannan yafara kiran yaransa d'aya bayan d'aya yana fad'in karsu tafi su barsa.. Rik'eshi Dr Yaseen yayi yana fad'in “ka kwantar da hankalinka ranka ya dad'e, dan zuciyarka tana cikin yanayin jiran k'iris ne, inamaka albishir da cewar yaranka suna raye, yanzu nan zakagansu insha ALLAH”.. Galadima ya sauke nannauyar ajiyar zuciya yana kallon Dr Yaseen, ya lumshe idonsa a hankali sannan ya bud'e, hanunsa ya d'ora akan saitin zuciyarsa saboda wajen yamasa matuk'ar nauyi. Ana haka Dr jalal ya shigo d'auke da yaran biyu, dan Abdurraheem shi yanan a d'akin kusa dashi bai farfad'o ba. Tunda Galadima yaga yaran sa suna a raye saiya kuma rungumesu a k'irjinsa da Dr jalal ya d'ora masa, wasu hawaye masu zafi suka gangara gefen kunnensa. Dr Yaseen yaji dad'in kukan da Galadima d'in yakeyi, dan zai rage masa rad'ad'in da yakeji da nauyin zuciyar, hakan ya nuna aikinsu zaiyi k'yau insha ALLAH. Galadima ya dad'e rungume da yaran, saidaga baya ya farga babu guda d'aya. A hankali ya bud'e baki yana fad'in, “ina d'ayan?”. Murmushi Dr Yaseen yayi, yace, “gashi a gefenka yana barci shima”. Juyawa Galadima yay ya kallesa, ganin d'an cikin yaron Na motsi alamar fitar numfaahi sai dad'i ya kuma ratsashi, ya lumshe idonsa yana yun k'urawa zai tashi zaune, taimaka masa. Dr
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83
- 84 Chapter 84
- 85 Chapter 85
- 86 Chapter 86
- 87 Chapter 87
- 88 Chapter 88
- 89 Chapter 89
- 90 Chapter 90
- 91 Chapter 91
- 92 Chapter 92