Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 40

Chapter 40

Raina Kama Book 2 Complete Hausa Novel 1,204 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ya lullu6a mata, harya mik'e ya koma ya zauna, risinowa yay kanta a hankali ya mannama goshinta kiss, sannan yamik'e ya fice. Koda ya dawo saiya wuce d'akinsa, yabar su Aiyaan suna kallonsu. Kayan jikinsa ya cire ya kwanta shima, dan yana buk'atar hutawa kona 2hours ne, kwanciyarsa kuwa babu dad'ewa barci ya saceshi. Kiran sallar la'asarne ya tashesu kusan lokaci d'aya, Galadima yatashi da k'yar, a mamakinsa sai yaga Aiyaan da Aryaan kwance a gefensa suma suna barci, murmushi kawai yayi yasako, saida ya watsa ruwa sannan yay shirin tafiya massalaci cikin k'ananun kaya. Harzai fita saiya dawo yashiga wajen Munaya. tana tsaye gaban wardrobe tana neman kaya, da alama wanka tayi, dan daga ita sai towel. Banji sallamarsa ba, saboda shi idan zaiyi magana bayason bud'e baki, ganin batajishiba saiyayi gyaran murya, a tsorace na waigoshi, ganin shine nai saurin saka kayan dana d'akko ina kare k'irjinna da tura baki, bakinsa ya d'an ta6e, sai kuma ya shiga takowa inda nake, duk takun da yayi sai gabanna ya fad'i, na waiga kozan samu nabar wajen ko abinda zan suturta jikinta sosai, amma sainaga babu a kusa, kuma ina jikin wardrobe d'inne sosai ai. ban gama yanke shawara ba ya k'araso daf da ni, kuma matsawa nayi na matse jikinna sosai a drowa d'in, shikuma yawani had'e gabas da yamma, wannan ne yakuma sakamin tsoronsa a raina, na zata kowata tsiyarce ta kawoshi. Hannu yasaka ya d'ago da ha6arta muka kalli juna, ya tsareni da idanu yanda nakasa janye nawa cikin nashin, munkai kusan 2minutes a haka, kafin yakumamatsoni sosai, ya kai fuskarsa gab da tawa tamkar zai had'e bakinmu, dan haka saina lumshe idanu, murmushi yayi ya hura mata iska akan idanun, ta rumtse idon sosai, ya d'an ja baya yana ta6e baki, kafin yasaka hannu ya cire nata dataketa faman kare k'irji da kayanta, still ya kuma matsawar saitin kunnenta yana fad'in “wane darene jemage bai ganiba yalla6iya”. ‘ya k'are maganar da shafa kirjina ya fice abinsa. Kad'an yarage namasa ihu wlhy, aiko yana fita na durk'ushe a wajen ina sauke numfashi, sometimes nakan rasa yazan fassara Galadima da ayyukansa. Da k'yar Na iya tashi nayi sallar nakoma kan gado Na kwanta. Galadima kam daya fita dariya ce taita cinsa, ya kula Munaya akwai tsoro, kuma haryanzu a tsorace take dashi, cikinnan ne kawai kanci galaba akanta yake samunta cikin sauk'i, ya girgiza kansa kawai yana murmushi. Bayan ya dawo massalaci d'akin nata ya dawo, dan yanason suje su gaida jama'ar gidan, maybe gobe suje masarautar papi ma. A kwance ya iskeni, nak'i kallonsa, jingina yay da mirror yana fad'in “yaya jikin naki?”. Ban kalleshinba nace, “da sauk'i”. “ALLAH ya k'ara sauki, idan zaki iya tashi ki shirya muje cikin gida, kafin waccan tsohuwar tafarama mutane surutu”. “to” nafad'a ina mik'ewa, Na sakko a gadon, harna nufi wardrobe zan d'auki alk'yabba saina tsaya, batareda Na kalleshi ba nace, “toka fita Na shirya”. Hard'e hannayensa yayi a k'irji yana fad'in “ashe bazaki shirya d'inba, dan bazanje ko inaba”. “karkaje d'in, ai akwai bayi” nayi maganar a zuciyata. Kayan Na d'auka na shiga toilet, shikuma ya ta6e baki. Babu dad'ewa na fito tsaf, nayi k'yau, nazo ta gefensa na d'auki turare nasaka kad'an sannan na kallesa nace, “na shirya”. Baice komaiba ya nunamin hanya, gaba nayi yana bina a baya muka fice. Kasancewar tazarar dake d'an tsakaninmu da sassan nasu muka shiga mota, dan banajin dad'in jikinna, bama zan iya tafiyarba. 6angaren Abba hayatudden muka fara zuwa, daga nan sai sashen matan mai martaba, soyayyar da uwargidansa ke nunamin yasani k'ara k'aunarta, sai addu'a take zabgamin akan ALLAH ya saukeni lafiya. Galadima kad'ai ke amsawa, amma ni saidai a zuciya kawai. daga nan muka d'an shishshiga wasu sassa, 6angaren mama fulani shine k'arshen zuwanmu. Kunsan dai mutuniyar taku akan mulki, tana kishingid'e kuyanginta nata bauta, mai matsa kafa daban mai firfita daban, ga masu bata labarai, tufa takeci cikeda k'asaita da izza. Amintacciyar baiwarta data mana iso tana gaba muna biye, mama Fulani ta d'agama kuyanginta hannu alamar subata waje. Rige-rigen ficewa suka, yayinda mukuma muka k'arasa gareta, idonta a kammu ko k'yaftawa batayi, nidai tsarin ALLAH na nema daga sharrinta, ina dalili wannan kallon k'urilla haka?. Galadima yace, “barka da yammaci”. nima saurin fad'a nayi. A yatsine ta amsa mana, ta d'ora da fad'in “Saraki kayi wuyar gani?”. Galadima ya murmusa yana kallona, “Ranki ya dad'e kinsan mai amarya ai yafi dubu wahalar gani dama”. “Humm” kawai tace batareda ta amsaba. Sai zuwa can tace “nafa manta, ina tayaku murnar samun k'aruwa”. “mun gode ranki ya dad'e, amma taki murnar itace tazo a latti, gashi kuma idonkine yafara hango abin cikin kwan tun a india”. Mama Fulani ta tsatstsare Galadima da idanu, shikuma yay salute nata yana murmushi. Jitai kamar zata makesa dan haushi. Ya lura da haushin da taji, dan haka ya kama hannuna muka mik'e tsaye yana fad'in, “bara mukoma inda muka fito ranki ya dad'e, a huta lafiya”. Bai jira amsartaba mukayi fitowarmu. Da kallo kawai ta bimu, takasa koda motsawa, tarasa miyyasa yau Galadima da matarsa suka mata wani mugun kwarjini? batada mai bata amsar tambayar tata... Yini guda yau Galadima a gida yayishi, baije ko inaba, sai da daddare Nuren yazo sukayi magana, daga nan yace ya nema mana tickets d'in zuwa masarautarsu. Washe gari muka tashi da shirin tafiya masarautar su papi, mukad'ai muka tafi, babu kuyangi babu dogarai, dagani sai shi dasu Aiyaan, sai Nuren..................✍🏼 *_ALLAH ka gafartama mahaifanmu_*😭🙏🏻 [7/3, 9:59 AM] Aysha Galadima: *_typing📲_* 💡 *_HASKE WRITERS. ASSO....._* *_♦RAINA KAMA.....!!♦_* _(Kaga gayya)_ *_Bilyn Abdull ce🤙🏻_* ~Book 2~ 👉🏻1⃣5⃣ ...................Abin yabani mamaki ganin yanda akazo tarbarmu, yo saikace wani Sarki, hakan yakuma tabbatarmin da Galadima d'an gatane a wannan masarautar. A masarautar ma gungun mutane muka iske wai masu tarbarmu, ni dukma sai kunya ta kamani wlhy, musamman da Mom ta rungumeni tana fad'in “ga maman twins d'inmu ga Maman twins d'inmu”. Galadima dai murmushi yayi, Nuren kam dariya ya kemin. Lallai naga tsantsar soyayya a wannan masarauta, sai nan nan ake dani kamar wata sarauniya, duk wani Motsina Inno tace minakeso? hakama mom. Aiyaan da Aryaan kam ai suna tare da Galadima, duk inda yasaka k'afa suna biye. Nikam dai a kwana biyun da mukayi babu abinda zance da wad'annan bayin ALLAH sai godiya, naga karamci naga hallaci sosai, hakama k'annena. Sosai Galadima yasamu tattaunawa da papi a tsakaninnan, sunyi maganganu masu muhimmancin gaske. Musamman akan ciwon Abie da cikin jikin Munaya, harma da Abbanta. sosai kuma Galadima yakuma samun haske akan lamuran. Kwannamu biyu muka dawo cikeda kewarsu, tare da tarin alkairi ga wad'annan mutane masu tsayawa a rai. Mun dawo da kwana 1 yaran gidanmu na ma'auri suka kawomin ziyara. Aunty khaleesa, aunty Hauwa'u, aunty Ramlah, aunty Raheenat, matansu ya hameed, Fiddausi, Siyama, Zarah, Safara'u, Fauziyya, Haleematu,Munubiya, Ayusher, Feena. Wayyo dad'i wlhy saika d'auka biki akeyi, rasa inda zansaka kaina nayi saboda dad'i, shi kansa Galadima ya fahimci ina tare da tsantsar farinciki, nima dagewa nayi namusu hidima iya hidima, dan hardani aka shiga kitchen. Sukam duksun rikice da mamaki, dama haka gidan sarautar yake, dan saidama Galadima yaje da kansa ya shigo dasu. Su Aiyaan anata murna anga 'yan gida. Ranar dai anan suka yini zir, dazasu

Table of Contents

Chapters

92 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});