Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 39

Chapter 39

Raina Kama Book 2 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

ruwa. Sauka nayi daga gadon dan zazzza6inna ya fara hucewa nima, freight na bud'e na d'akko masa ruwa, na had'o da Kofi, zama nayi kusa dashi a gefen gadon na tsiyaya ruwan a Kofi na mik'a masa. kar6a yayi ya shanye, ya mik'o min kofin, zan kar6a ya girgiza min kai tare da min nuni da in k'ara masa. Kuma tsiyaya masa nayi, yakai rabi ya d'aga min hannu alamar ya Isa, bayan yakuma shanyewa ya mik'a min kofin yana fad'in “Thanks”. Kar6ar kofin nayi, ba tareda na tashiba nace “Yalla6ai lafiya kuwa”.. “Mafarki”. ‘yafad'a yana komawa ya kwanta’. Idanu kawai Na zuba masa, kusan 4minutes ya juyo da kansa ya kalleni, “kizo ki kwanta mana”. K'aramar ajiyar zuciya kawai Na sauke Na mik'e, Na d'ora ruwan da Kofi a dirowan gefen gadon na koma inda nake na kwanta. Ganin ya sauya hannun da yay mafarkin kuma yana addu'a sai ban sake cewa komaiba, na kwanta shiru ina sak'e-sak'e a raina mafarkin mi yayi to? da har yasakashi firgita irin haka?. banida mai bani amsa dan haka nayi shiru. Saiya zamto da asuba na rigashi tashi, harma saida nayi alwala sannan na tadashi, da k'yar ya iya tashi yana dafe kai, binsa nayi da kallo kawai harya shige toilet. Lokacin daya fito na fara salla, dan haka saiya fice kawai. A mamakinsa saiya iske Aiyaan da Aryaan sun tashi suna alwala, hakan ya Burgesa sosai. Sai kawai ya kama hannunsu suka tafi massalaci. Bayan an idar da salla bai yarda sun had'u da Sarki ba, ya gudo. Sai dai abinda bai saniba shi Sarki ya gansa, dan yau ya makara salla shima. Wajen Around 9am nagama gyaran d'aki nayi wanka, saina d'an fito falon domin duba dubawa, natarar sabbin kuyangina suma komai sun gyarashi k'al, harma da mana break fast, banyi yunk'urin bud'ewa ba ma balle tunanin son ci, dukda kuwa natashi da yunwa, to amma Momma ta gargad'eni sosai akan cin abinci wani a masarautar, dan haka na fito daga kitchen d'in kawai. Tunkan na shigo nake jiyo maganarsu Aryaan, zaune na iske Galadima su Aiyaan na kusa dashi suna bashi labari, anmusu wanka tsaf, sunsha sabbin kaya iri d'aya. Har yanzu Galadima bayada walwala, na zauna ina gaisheshi, batareda yabar latsa wayarba ya amsa min, su Aiyaan suka dawo kusa dani suna gaisheni, kumatunsu naja ina murmushi, “oh my guys kunsha k'yau, waya muku wanka haka?”.. Atare suka amsa min da fad'in “Uncle ne, kuma ya saka mana tirare yanda kuke mana”. Murmushi nayi, na saci kallon Galadima da yay biris damu kamar baya d'akin, alhalin sanda na shigo na iske suna hira shidasu 'yan 2. Sallamar da wata baiwa keta kwad'awa na amsa, sannan na mik'e na fita dannaji minene? A k'ofar falona na isketa, nace, “miya farune?”. Duk'ewa tayi ta gaisheni, sannan ta mik'omin ledojin hannunta tana sanarmin Sarkin motane yace “na kawo wannan ranki ya dad'e”. Kar6a nayi, na koma ciki. Ajiye ledojin nayi a gabansa, “gashi wai inji sarkin mota”. Idanunsa ya d'ago ya kalleni, yace, “breakfast d'inku ne”. Tashi yay ya fita yana fad'in na shirya zaije ya dawo mu shiga cikin gida gaida mutane. Na amsa masa da to. ___________________ Tun a daren jiya wasu bayi sukaga Muftahu, dan haka suka shiga ihu, dandanan sauran bayin dake kusa da wajan suka firfito, manyan bayin cikinsu ne suka kai maganar cikin gida, shine akasakasu d'aukar Muftahu su shiga dashi. Lamarin yabama kowa mamaki, babu wani mummunan rauni a jikinsa, inbanda d'an jini dake gefen bakinsa, saidai sun sami kwanciyar hankali ganin yana numfashi. Maganar dawowar Muftahu bata baje masarautar ba sai washe gari. Bayan Galadima ya fito daga sashensa zaije fada yaji anata k'ananun magana akan dawowar Muftahu, saidai kuma miskilancinsa bai barsa ya tambayi kowaba ya nufi Fada. Ya isa mai martaba baikai ga isowa ba, dan haka suka gaisa da 'yan majilissar Sarki dake fadar, sannan ya nemi mazauninsa dake gefen Sarki Na dama ya zauna. Zamansa baifi da mintuna 10 ba Mai martaba ya iso, gaba d'aya suka mik'e tsaye, dogaran Sarki sunata kirari da fad'in gyara kintsi da k'yau, duksun baza riguna ba'a gani mai martaba, basu bar kowa ya gansa ba har saida ya zauna a kujerarsa. Baya suka mammatsa mai martaba ya bayyana, atare su Galadima suka rissinar dakai alamun girmamawa, sannan kowa yafito tsakkiyar fada ya mik'a gaisuwarsa ga Sarki, yayinda fadawa ke faman amsawa, tsakanin Sarki dasu kuwa shine d'aga hannu. Mai martaba yayi mamakin ganin Galadima yau azaman fada, bawai baya zaman bane, sai dai yakan dad'e bai zaunaba, an masa uzurine kasancewar ansan ba zaune yake dindin dinba, kuma idan yazo akwai harkokinsa Na kasuwanci da yakeyi, sai dai dolene yakan shigo yayi gaisuwa. Bayan fada ta nutsu aka fara fadanci. K'a idane fadar gagara badau takanyi fadancine a sati sau hud'u kawai, litinin ba'a zaman fada, domin ranace da ake tunawa da abinda ya faru ga tsohon Sarki mahaifin Galadima, talata, laraba, alhamis, asabar, sune ranakun da ake fadanci, ranar juma'a ma ba'ayi saboda muhimmancin ranar ga al'ummar musulmi. A wad'annan ranakun akanyi zamanne daga 10am zuwa 12:30pm, da an tafi sallar zuhur ba'a dawowa, idan kaga anwuce wannan time d'in a fada to tabbas akwai abinda ya farune. A wannan zaman fadancine maganar dawowar Muftahu ta fito, sun tattauna akai harda shirin kuma d'aukar matakai Na tsaro a masarautar. Bayan anyi sallar zuhur ne Sarki ya shige gida, sauran fadawa ma kowa ya kama gabansa, Galadima bai shiga gidaba saiya nufi sashen su Muftahu domin dubashi. Bayan an masa iso ya shiga, ya iske mahaifiyar Muftahu da 'yan uwansa zagaye dashi, har yanzu kuma yana cikin yanayin barci. Ya jajanta musu, Yakuma kwantarma da mamansu Muftahu hankali, kusan mintunsa talatin ya fito ya koma sashensa. Ya iske su Aiyaan kawai a falon Munaya suna kallo, suka taso da gudunsu suka rungumesa, fuskarsa cikeda fara'a ya tarbesu, ya tambayesu ina Auntynsu?. A tare suka bashi amsa, “Uncle tana d'aki ta kwanta kuma tace karmu tadata, inba hakaba jiki magayi”. Murmushi yayi yaja kumatunsu, “kuce zatayi zana kenan idan aka tada ita?”. Nanma atare suka amsa da “eh Uncle, kasanfa Aunty Munaya tacika fad'a, gidanmu tsoron masifarta akeyi, amma ita Aunty Munubiya babu ruwanta”. Galadima yace, “da gaske?”. “ALLAH kuwa Uncle, idanfa mukayi rashinji ita ke zanemu ba innarmu ba, kuma dukanta da zafi, gashi taita hararmu da katun-k'atun idanunta nan”. Sosai abin yabama galadima dariya, dan haka ya dara sosai abinsa yana fad'in, “kubari tajiku to, idan ta zaneku babu ruwana nidai, kunga bara naje naga kota tashi, karfa Ku shigo, dan zata iya zaneku”. Sukace “ai bazamu shigoba Uncle”. Yace, “good boys”. Da sallama ya shigo, amma saiya isketa baje a gado tana shak'ar barcinta, yad'an murmusa kafin ya k'arasa ya zauna a bakin gadon saitin fuskarta, yatsunsa biyu yasaka a gefen wuyanta dan yasan da wahala wannan barcin ya kasance na lafiya, aikam jikinta ringim yake da zazza6i, tausayinta ya kamashi, lallai uwa dabance acikin al'umma, Ashe haka sukeshan wala, tundaga d'aukar cikinma zuwa rainonsa, akoma rainon yaro, daganan tarbiyarsa, lallai masu raina mata ko kallonsu masu k'arancin tunani sune masu k'arancin tunanin ai, ya d'an lumshe idanunsa yana cije lips, ganin ta dunk'ule a waje d'aya saiya ja bargo

Table of Contents

Chapters

92 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});