Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 34

Chapter 34

Raina Kama Book 2 Complete Hausa Novel 1,199 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

komai tun d'azun ya tuntsure da dariya yana fad'in ALLAH ya k'ara, bana fad'a miki Shiba Na wasan yara bane ba, banda jaraba kinbi kin nanik'ema bawan ALLAH daga had'uwa a jirgi, kinbi kin addabi rayuwata saina nemo miki number sa, aini nama godema ALLAH da kuma sake had'uwa ya kuma nuna miki ainahin halinsa, saida Na fad'a miki baima dad'e dayin aureba, ke gadararriya kikace aurensa bai damekiba........ Yanda ta daka masa tsawa yasakashi firgita ya russuna yana Neman afuwarta. Cikeda masifa tace “tada mota mukoma gida”. “Amma ma'am kin manta jirginku yakusa tashi?”. A tsorace yayi maganar. Harara ta Dalla masa tace “Ubanka ne ya viyamin kud'in jirgin”. Wasu yawu masu rad'ad'i driver ya had'iye yana girgiza mata kai, ya bud'e motar ta Shiga sannan ya rufe shima ya zagaya mazauninsa suka koma Inda suka fito😜. Nasan dai kun fahimci yarinyarnan Ce da suka zauna waje d'aya a jirgi itada Galadima randa zaizo😆🥳. Ganin tabar wajen Galadima yay murmushi sannan yafara k'ok'arin d'agoni daga k'irjinsa, ban yarda mun had'a idoba na bar wajen. “Saikin dawo” ya fad'a a hankali. Kasa daurewa nayi saida Na waigo Dan tabbatar da shine yay maganar kokuwa dai wanine?. Ido muka had'a ya janye nasa cikeda basarwa yana la6e baki. Nima harara Na watsa masa ina barin wajen. Tunda Na taho Maman safara'u da mamansu Yaa hameed da Momy suka zubamin ido. Nikuma fahimtar kallon k'urillar da sukemin saina canja salon tafiya da kuma had'e fuska na nufi zuwa wajen gungun yaran gidanmu masu aure dasuke hira. Suma duk kallona sukayi, namusu murmushi ina fad'in “lallai munada cin ragunan suna kwannan nan ashe”. Dariya duk sukayi, Fiddausi tace “yariman namu shikuma da kwad'ayin naman suna yazo?”. Harara Na zuba mata ina kai mata bugu ta waske itama tana dariya, yayinda su Munubiya ke tayata. Mun gaggaisa tareda tambayar lafiyar juna, muka d'an ta6a hira kad'an da alk'awarin duk zanje mu gaisa, suma sukace zasuzo tunda ba yanzu zan koma ba. daga nan mukai shirin tafiya, Siyama da Zarah anata mana iyayi su masu motar hawa, (dayake kowacce a motarta tazo). Ni dai ni da Munubiya Yaa Marwan ya d'aukemu muka tafi. ____________________________ Tunda nabar wajen Nuren yazo ya tasa Galadima da tsiya, wai dama haka yake ashe?, rashin kunyar tasa har agaban surukai?. Banza Galadima yamasa yay shigewarsa mota yabarsa yana iskancinsa. Anan suka tafi suka barsa dayake da mota yazo shima. Galadima na barin airport gidanmu ya nufa shima. A lokacin 'yan gidanmu suma sun Isa gida, sunata k'ananun magana akan abinda Galadima da munaya sukayi, dan saida suka bama sauran labari, nanfa suka kacame da zancen harda k'arin k'arya akai wai ba kiss kawai sukaiba ('yan gidansu munaya annamimatu🙆🏻😂). Itadai Maman Fauziyya batace k'alaba, saima dariya da zancen ke bata, Dady kuma bai dawo gidanba, daga nan wajen aiki ya wuce, yaran gidan ma kowa gidanta ta koma basu biyo nanba. Innaro da gwaggo Safiyya kam gida suka shige ana saukesu, dan haka basuji komaiba. Galadima bai shiga gidan ba, saiya nemi iso gidan Innaro, Habiba ta fito tamasa jagora. Innaro na falo tana cika da batsewa gwaggo Safiyya na lalla6ata akan ta kwantar da hankalinta. Koda Galadima ya shigo innaro sai antaya masa harara takeyi, yana kula da ita ta gefen ido, ya murmusa yana zama saman kujera, cikeda tsokana yace “Sweet Granny Yaya dai?”. Harara innaro ta zuba masa sosai, tana fad'in mikuma kazo min nan?”. Galadima ya murmusa yana maida hankalinsa ga gwaggo Safiyya, gaisheta yayi ta amsa masa cike da kulawa, sannan ta d'ora da godiya da kwarara masa addu'ar fatan alkairi. Yaji dad'i sosai, ya amsa cikin fara'a, sannan yace, “Granny ina furar tsufa?”. “ai bazaka shata ba ”. Nanma murmushin Galadima yayi yana mamakin wannan rikitacciyar tsohuwa. Yace “tunda bazan shaba Ashe kema kuwa bak'yaje India ba”. Zabura innaro tayi, ta maida hankalinta ga Galadima tana fad'in “da gaske kake ko shak'iyancine?”. Mi su Naja'atu zasuyi inba dariya ba, Galadima ma handkerchief ya saka ya rufe bakinsa kawai. Gwaggo Safiyya kanta saida ta dara. Galadima ya gyara zamansa yana fad'in “karki damu Granny ninmu, insha ALLAH tare dake zamu tafi idan zamu koma”. Dad'i ya kama innaro ta shiga sakama Galadima albarka. Shidai murmushi kawai yakeyi. saida yaga sun nutsu sannan yace yazo tafiya dasu Aiyaan ne, babu musu innaro ta mik'e da kanta zuwa gidan danta kawo masa su. Bayan fitarta gwaggo Safiyya tabama Galadima hak'uri akan darun innaro. “karki damu gwaggo, ai dama kowa yasan idan sunkai irin wannan age d'in saida lalla6awa, ALLAH dai yaja mana ransu”. Amin gwaggo Safiyya tafad'a cikin jin dad'i. Tunda 'yan gidansu Munaya sukaji wai Galadima ne da kansa yazo tafiya dasu Aryaan sai zukatansu suka kuma tunzura, kowa tana ganin hakan salon munafurcine, Maman Fauziyya ta kawoma innaro su, dama suna d'akinta, dan mamansu yaa hameed suna dawowa ta d'auki jakkarsu Aiyaan ta kaimata, wai sai dai su zauna wajenta ita d'akinta babu fili. Maman Fauziyya batace komai ba ta kar6i su Aiyaan tana jinjina bak'in hali irinnan jama'ar gidan. Amma kuma yanzu sai gasu sune dajin haushi. Ita dai innaro ko'a kanta ta jawo hannunsu Zainab ta d'akko jakkar kayansu suka taho. Koda sukazo ma sai Galadima yace abar kayan nasu su kad'ai yake buk'ata. ya ajiyema Gwaggo Safiyya da innaro alkairi ya fito rik'e da hannun su Aiyaan daketa murna. Innaro har wajen mota ta rakosu, bata komaba saida taga tafiyarsu. tana komawa gida tahau had'a kayan tafiya, wai gara ta had'a ta huta, duk randa Galadima yazo sai tafiya kawai. Ita dai gwaggo Safiyya dariya kawai tayi, dan maganar Galadima gaskiyace, lamarin innaro yana buk'atar uziri, ta tsufa sosai, kawai dai ALLAH yabata lafiyane, dan da wuya kaga innaro na kukan wani waje namata ciwo irin na tsufa. (masifarta kam dai kunsan ance abinda kayi a k'uruciya shi kake maimaitawa lokacin tsufa, ALLAH ka azurtamu da k'yak'yk'yawar k'uruciya to🤦🏻‍♀). ★★★★)(★)(★★★★ A k'ofar sabon matsakaicin gidan motocin biyu suka tsaya, cikin wad'anda suke a motar baya d'aya ya fito ya bud'e motar farko, hamshak'iyar macece mai ji da mulki da kud'i ta fito, kallo d'aya zaka mata ka tabbatar tagama samun duniya, cikin tsantsar tink'aho da homa take zuk'ar iska tareda taku d'ai-d'ai irin na manyan mata. Cikin sauri aka bud'e mata k'ofar gidan ta shiga guard d'inta na take mata baya. A tsakkiyar tsakar gidan taja tunga, sai hura hanci takeyi tana harare-harare. d'aya a cikin guards nata yace, “ ma'am nan shine d'akin da yake”. Batace uffanba taci gaba da takawa d'ai-dai har zuwa k'ofar d'akin, hannu ta d'aga musu alamar su dakata. Dukkansu baya sukaja domin cika umarninta. Zaune yake a kujera an d'ad'd'aureshi, kallo d'aya zaka masa ka tabbatar a galabaice yake. Shigowarta baisa ya d'aga kai ba balle ya motsa, yasan dai bazai wuce k'artan dasuka kawosa wajen baneba. sai dai jin k'amshin turaren mace yabashi mamaki, hakanne ya sakashi d'ago idanu domin tabbatar da yaren hancinsa. Bakinsa na rawa yace, “Wacece ke?”. Bata bashi amsaba, saima kujera data ja irin wadda yake kai ta dinning ta zauna, k'afa d'aya ta d'ora akan d'aya tana wani cika da batsewa. “yaro baka isa sanin ni wacece ba, Sai dai cigaba da 6atamin aiki zai sakaka sanina”. Murmushi Muftahu yayi, ya

Table of Contents

Chapters

92 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
  77. 77 Chapter 77
  78. 78 Chapter 78
  79. 79 Chapter 79
  80. 80 Chapter 80
  81. 81 Chapter 81
  82. 82 Chapter 82
  83. 83 Chapter 83
  84. 84 Chapter 84
  85. 85 Chapter 85
  86. 86 Chapter 86
  87. 87 Chapter 87
  88. 88 Chapter 88
  89. 89 Chapter 89
  90. 90 Chapter 90
  91. 91 Chapter 91
  92. 92 Chapter 92
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});