Chapter 55
Chapter 55
kayan da take tana kallona da mamaki, “Ban ganeba, bakison komawar ne? Dakikemin wannan banzar tambayar?”. Baki Na zum6ura ina fad'in “Nikam dai bazan koma haka siddan ba, sai inhar yazo ya warwarema iyayena komai gameda tubalin daya k'ulla aurenmu a farko, yakuma basu hak'uri”. Kasa magana Munubiya tayi, saima ta zauna a bakin gadon, ita batasan wajen ubanwa Munaya ta d'akko halin taurin kai ba wlhy, ita tama rasa mizata ce mata. Nima d'auke kaina nayi gefe Dan ina kan bakana, ina tausayinsa Dan koba komai ya k'yautatamin a lokacin da nima banida lafiya, kuma ta silata yake kwance yanzu, to ammafa hakan bazai zama yasha a banzaba, kenan ma anan gaba wasu zasu iya aikata hakan ga kowacce mace?. Laraba dataji komai dake faruwa tana niyyar shigowa saita koma da baya gabanta Na fad'uwa, ita bataga laifin Munaya ba, dan wannan shine martaba da sanin ciwon kai, kuma wannan ya tabbatar mata da ba kwad'ayine yasata zama da shiba, amma bata fatan abinda zai girgid'a wannan Auren komai k'ank'antarsa waya ta d'auka ta kira Mom ta sanar mata komai, hankalin mom ya tashi, danba ta wanann hanyar takeson Munaya ta hora Galadima ba, bakuma taso iyayenta su Sani, suma sunada burin d'aukar mata mataki itada Momma, Dan bazasu bar wannan gangancin Na Galadima ya wuce a banzaba.. Momma ta kira tace Dan ALLAH ta kira Munaya tabata hak'uri akan ta koma, Dan babu mai kula da Galadima d'in, insha ALLAHU daga baya wannan maganar za'ayita. Momma ma duksai ta damu, dan har cikin ranta tana k'aunar Munaya, bazataso wata matsala ta tasoba bayan hankalinta ya kwanta akan zamansu. Munaya suna tare da Munubiya har yanzu a d'aki, ta balbaleta da masifa kamar ta daketa, Munubiya tanada hak'uri, shiyyasa idan tana masifa dolene kasan takai k'arshen 6acin rai, Munaya saita zuba mata ido kawai takasa cewa uffan, ana cikin hakane kira ya shigo wayar Munaya. Harzata share saikuma ta d'au tana dubawa, ganin Momma tai saurin d'agawa tana share hawayen da suka zubo mata. Cikeda girmamawa kamar yanda ta saba ta gaisheta. Daga can Momma ta amsa cikin kulawa itama, face, “Kun dawo lafiya d'iyata?”. “Alhmdllh Momma ya jikin Abie”. “Jiki kan Alhmdllh d'iyata, dama Abbanki ne ya kirani akan zaki koma, saboda Muh'd babu lafiya, da farko dai nayi tunanin cewa a barki harsai yazo yafad'a musu laifin daya aikata agaresu, saikuma nayi wani tunani daga baya, kiyi hak'uri ki koma yaud'in Dan ALLAH, saboda Mura bataima Muh'd da sauk'i, namiki alk'awarin zan d'auki mataki da kaina, zan sanar masa Ku tahoma gobe idan ALLAH ya kaimu kinji”. Bazan iyama Momma musuba har abada, Dan nasan bazata cutar daniba, saidai kuma nayi mamakin dama tasan auren Contract mukayine?....... Katsemin tunani tayi da fad'in “d'iyata idan kinga zaki cutu abari kawai, bazan ta6a bari Muh'd ya cutar dakeba wai danni Na haifesa wlhy”. “A'a Momma Na amince”. Daga can Momma ta sauke ajiyar zuciya tana fad'in, “Alhmdllh, d'iyata nagode sosai, ALLAH yay miki albarka kinji”. Idona cike da kwalla Na amsa da amin. Tace Na gaida mata kowa ta Yanke wayar. Munubiya dukda ta fahimci dawa Munaya tayi waya batace da ita uffanba, tacigaba da had'a musu kaya kawai. Ciwonsa ne yasani Na danne zuciyata Na amince, dakuma Kimar mahaifiyarsa danake gani, Dan sun nunamin dukkan k'aunar da inhar Na bitilcemusu banma kaina adalciba nima. yinin ranar gaba d'aya a hidimar shirin komawa mukayisa, ga gajiyar tafiya Na nuk'urk'usarmu, amma ya muka iya, da yamma dole su mama Rabi'a suka dawo domin mana rakiya. A gurguje please🤨😏. ****************** Abin mamaki sai gamu da rusar kuka ni da Munubiya, saikace wasu sabbin amare, bayan nasiha da Abba da baba k'arami, daddy sukai mana Na ajiye musu keys d'in motocinsu, da farko sunce bazasu kar6aba Na sanya musu kuka. Innaro tahau musu fad'a babu k'yau maida hannun k'yauta baya ai, wannan aikin shaid'anne. Albarka dai munshata kam, yayinda zukatan matan gidanmu yakusa babbakewa saboda bak'ar hassadarsu, kowa son samunshi ace d'ansane yayi. Laraba ma harda hawayen sabo, dan bak'aramar girmamawa aka mata a gidannanba, har abada bazata ta6a mantawa da dattako irinna inna ba. Kaf matan gidanmu dasu aka tafi, innarmu da Innaro kawai aka bari, amma hardasu Siyama. Ni suka fara rakawa, ALLAH ya somu muka iske Muftahu yadawo daga yawonsa zai shiga masarautar, da taimakonsa muka shiga, yayi mamakin dawowata, dan Galadima ya sanar masa muna Niger, shi baisan yadawoba ma, hasalima babu Wanda yasan Galadima ya dawo masarautar, tunda ko salla bai fitaba, sai hadimansa kawai. Ba sashenmu akai kainiba, Muftahu ya sanar musu sai an fara kaini wajen mama Fulani sannan, haka al'adar masarautar take. Aikam dai hakan akayi. Tarba ta mutunci mama Fulani tasa akaima dangina, tana nandai yanda kuka Santa da mulkinnan nata da izza, amma ni a yanzu tunda Na fahimci ita ba muguwa bace sai salon nata yake k'ayatar dani. An min dukkan yanda al'adar masaurat ta tanadar, sannan mama Fulani dakanta tamin rakkiya sashena tareda bayi da dangina, ko ina k'al tamkar muna nan. Bayan fitar mama Fulani y'an gidanmu suka kuma shishshiga suna kallo gida wai, dan ranar suna da suka fara zuwa basu sami wannan damarba saboda idon mutane, nidai batasu nakeba, hankalina nakan mijina, burina naje naga halin da yake ciki. Munubiya takuma min nasiha da bani wasu dabaru, tunda su sinzama tsoffin hannu, muko yanzune zamuyi zaman auren tsaftatacce, takuma nunamin nabi komai a hankali, tasan yayi kuskure amma bata hanyar tonama kanmu asiri zan nuna masa kuskurensa ba, kodan matsalar gidanmu ai saina duba, ni macece inada damar juya komai cikin sauk'i, nama iya zama dashi a lokacinda yake ik'irarin auren yarjejeniya bare kuma yanzu daya furta yana sona da bakinsa. Naji dad'in shawarwarinta, nakuma fahimceta sosai, Naimata godiya kuma, da alk'awarin amfani da shawararta insha ALLAH. Hakama mama Rabi'a tak'aramin nasiha da gargad'i mai yawa akan karsuji karsu gani, Na tsare musu mutuncinsu, Dan kowa da tarbiyyar gidansu yake ado. Itama na amsa mata da insha ALLAH zan kiyaye. A y'an gidanmu kam Maman Fauziyya Ce kawai tamin fad'a, amma sauran babu wadda tace nayi mai k'yau ko mummuna, wannan ba matsalarsu baceba, nima ban damuba, Dan wad'anda suka Isa dani sunmin kuma ya wadatar. yayinda zasu tafi rungume juna mukayi da Siyama da Munubiya, Zarah muna hawaye, jimuke tamkar karmu rabu. Dan wlhy yanzu nikam tausayi suke bani, koma miye dai iyayen su mata da k'addara Ce taja musu. Inaji ina gani suka tafi suka barni da kewa, danma laraba Na nan. Suna wucewa laraba ta kalleni, cikin dabarunsu Na tsoffi tace, “koyaya jikin magajin garin?”. Kaina a k'asa nace, “inaga barci yake iya”. Tayi murmushi, Dan kunyar Munaya da kawaicinta Na burgeta, yanda idon yaran yanzu ke a bud'e da rashin kunya a halinyanzu, da watace tuni tanufi d'akin mijin. tace, “yakamata to kiduba koya tashi, da saiki samu kayan k'amshi ki dafasu, insha ALLAH yasha Na kwana biyu sai murar ta barshi”. Godiya Na mata sannan Na mik'e a kunyace Na fita. A falon dazai sadani da sashensa naci karo da Muftahu, barka da zuwa yakuma yimin muka kuma gaisawa amutunce. Yace, “Boss d'in Na ciki kuwa? Dan sarkin k'ofa yace yayi sallama Dan nemamin iso yaji shiru”. Nace, “Ai bashida lafiyane, maybe
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83