Chapter 30
Chapter 30
matsayin karatunsa da abinda suke karanta, dukda ba magana yakeba murmushinsa Na sakasu farin ciki..... .............★ A can kuwa waje, police nata k'ullawa da kwancewa da jiran isowar IG, Dan yace su jirayi zuwansa. Dukda Galadima yana hira da yaran hankalinsa nakan saurarensu ta abinda ke kunnensa. Babu dad'ewa saiga IG ya iso, kar6ar wayar yayi da kansa bayan sungama salute nashi ya zauna, ya kuma kiran Galadima da kansa. Galadima yay picking amma sai yak'i magana yanzunma, hakanne yasaka IG yin magana cikin takaici da fusata, “Kai bamason rainin hankali, kafad'i abinda kawai kakeso duka amaka kabasu yaransu”. K'ala Galadima bai ceba ya yanke wayar. Mamaki ya kama IG, C.P yace, “Sir dadai anyi hak'uri an musu magana kawai suma aji mizasu ce”. Cikin matuk'ar takaici IG ya dangwarar da wayar yana huci da cire hular kansa, da hannu yayma C.P umarnin a kirasun. Da Sauri Aka danna kiran wayar d'aya daga cikin su, dama duksun tattarune a waje d'aya, Dan haka ya saka Hans free duk sunaji. C.P da kansa ya sanar musu buk'atar Galadima, kallon kallo aka dungayi, kowa ya kasa magana, Shidai C.P ya yanke wayar yana fad'in “nanda mintuna 10 zasu kira”. Suna ganin C.P ya yanke wayar suka hau cecekuce da fad'in yaronan yagama raina musu hankali, kaza-kaza dai, wasu suna bada goyon bayan abadashi sai abi tawata hanyar a kar6i camera d'in saboda suna matuk'ar k'aunar yaransu, wasu kuma sunce kar'a sakeshi, Dan haka tamkar tonon sililine agaresu. Sundai kasa samun matsaya har 10minute's ta cika C.P ya sake kira. Ba'a samu Wanda ya iya d'agawaba harta yanke....... (**************************) Zuwa yanzu gidan su Munaya sunsan halin da'ake ciki game da Galadima dakuma maganar fitowar Abba, Dan y'an jarida nata yad'a komai live a gidajen redio da TV, ga masu d'auka a waya y'an gani da ido dasukazo suka kafa suka kuma tsare. Kuka dai Munaya Na shansa, tayi wujigi-wujigi, miji da Uba duk suna cikin matsala, da k'yar inna ta bata tea tasha da kanta, yaranma sai an mata dole take shayar dasu, ta lafe jikin innarsu tanata hawaye daga ita har Munubiya, yaran sai innaro dasu mama rabi'a da sukazo gidan Tun farar safiya ke kula dasu. A can gefe kuma Zarah da Siyama NATA zagayen d'akin Abba Dan son samun damar shigewa su d'auki camera🤦🏻♀. ************************** Alhaji Hallurune yabasu shawarar su d'auka kawai suce su k'arya ake musu Alhaji Auwal baya hannunsu. Wannan shawarar sukabi, da Kansu suka kira C.P suka shaida masa. Sharri Galadima ke musu. Galadima dakejin komai yayi murmushi kawai yana cizar lips. Laptop d'insa ya janyo yafara danne-danne. Daga can C.P ya yanke wayar yana Neman izinin IG domin kiran Galadima shima. IG ya bada izini zuciyarsa Na sakejin zafin Galadima da rainin wayonsa. Saida ta kusa tsinkewa sannan Galadima yay picking, C.P ya sanar dashi amsar da suka bada. Cikin murmushi mai sauti da har su C.P sukeji Galadima yace, “ga za6i biyunan, kodai su fad'i inda yake, kokuma su sakoshi, kokuma shi yasaki video d'in yanda suka saceshi”. Jikin C.P fa kansa yafara sanyi, Dan yafara hango k'amshin gaskiyar Galadima. Bindiga Galadima ya nuna Alhaji Darma da ita, yamasa alamar ya matso gabansa, jikin Alhaji Darma Na rawa ya matso, waya ya mik'a masa, sannan ya danna kiran su C.P yana fad'in a had'ashi dasu yanzunan. Kallon IG C.P yayi, alamar neman izini, IG ya bada damar hakan. Dan danan aka had'a Galadima da su, bindigar hannunsa ya d'ora saman kan Ahmad, maimakon Alhaji Darma, jikin Ahmad yafara rawa, tuni yafara kuka saboda tsoro, tsawa Suka dakama Galadima daga can. Ahmad daketa mazari ya sanya kuka yana fad'in “Dady please and please kubashi abinda yakeso Dan ALLAH, wlhy zai kasheni, wayyo daddy I love you so much”. Tuni Alhaji Bana ya rikice jin muryar d'ansa, Galadima ya cire bindigar daga kan Ahmad ya harbata gefe, k'arar ta tsorata su Ahamad suka rikice da ihu. Rud'ewa su Alhaji Bana sukayi, Dan azatonsu Galadima ya kashe Ahmad ne, su kansa su IG dake waje duk sun tsorata da tunanin ko Galadima ya harbi wanine a cikinsu. Galadima yace, “idan Baku shirya sakinshiba zan kashe Na gaba kuma”. A tare suka hau ihu kowa yana rige-rigen fad'in zasu saki Abba. Galadima ya ta6e baki yana gimtse kiran. Alhaji Bana dai ya suma tuni, saboda tunanin an kashe masa d'a. Saidai suka zuba masa ruwa ya farfad'o, kuka rurus yashiga musu yana kiran sunan Ahmad d'insa, Yakuma rikicewa lokacinda Hajiya Fannah Maman Ahmad ta kirashi. Kasa d'agawa yayi....... **** Galadima yay kiran su IG yana fad'in “inhar suka nakasa Abba ko kawoshi da wani mummunan raune abakin ran d'aya daga cikin y'ay'ansu, Dan haka a matsayinsu Na police su gargad'esu. ********* Antura Police inda suka kwatanta aje a d'akko Abbansu Munaya. A inda aka d'aukeshi suka iskeshi ajiye cikin mota a sume, haka suka d'akkoshi suka taho, kai tsaye asibiti aka wuce dashi domin duba lafiyarsa, dukda babu wani ciwo a jikinsa Na alamar duka sai fashewar baki da kumburin da fuskarta tayi shima bada wani yawa can sosaiba. Galadima sunga komai a TV saboda nunawar da akeyi, hawayen da suka taho masa ya had'iye da k'yar yana sunkuyar dakai danma kar wani cikin yaran kosu Muftahu su fahimci wani Abu, saidai tuni Nuren and Muftahu da Harun sun fahimceshi, Dan sunsa halayyarsa duka, yana da tausayi ainun. Ran Harun A 6ace yake akan bada Abba dasu Alhaji Mansur sukayi, zuciyarsa sai tafarfasa takeyi, gashi kuma a d'aure. Galadima ya mik'e yana bada izinin kowa yaje yay alwala time d'in salla yayi. Idan kuma anyi salla su Farhat su shiga kitchen nema musu abinci. Wannan adalci Na Galadima yanata tasiri a zukatan yaran, harsu gebiral. Duk yanda Galadima yace haka sukayi, har Harun dake d'aure saida aka kwanceshi bisa tsayawar Ameer kansa da bindiga yay alwala. Koda su IG suka nemi yin magana da Galadima saiya jefa musu takardar yana sanar musu time d'in salla yayi, bazai sake saurarensuba sai yayi salla.. Dole sukabi yanda yakeso, suma kuma ya tunatar dasu abinda suka manta. .............................★ Bayan idar da salla da gama girkin su Farhat aka kawo abincin kowa ya d'ebi iya buk'atarsa, yanzuma Galadima bai Ciba, kwanciyarsama yayi cikin kujera ya lumshe ido. Harun dai anji wahala anci yanzu🤣😜. .............................★ Tuni mazan gidan su Munaya suka d'unguma zuwa asibitin Dan duba halin da Abba yake ciki, matan dai da yaran an barsu a gida, sai innaro kawai data Dage sai taje aka tafi da ita. .............................★ Buk'ata ta biyu da Galadima ya kawo bayan idar da salla itace a tura jami'an tsaro suje subama iyalan Abba tsaro a gidansa, hakama a asibiti. Babu musu IG yasaka C.P, shikuma CP yabama D.P.O Umarni, dandanan aka sanar da station d'in yankin su Munaya, aka kuma k'ara dawasu police d'in harda mata da zasu shiga cikin gida. Munaya taji dad'in hakan da Galadima yayi, Dan a tsorace tale dama. Dole kuma Zarah da Siyama suka nutsu, Dan Munaya k'ofar Abba taja zugar y'an uwanta suka shimfid'a tabarma sukayi zaman jugum-jugum d'in a can.🤨👍🏻. ************************ A masarautar gagara badau kam babu abinda kakeji Na tashi sai k'ananun magana. Bayi da kuyangi, dogarai da y'an gidan, manya da yara, kowane hadimi burinsa yafara kaima
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83