Chapter 10
Chapter 10
babu tambaya nasan Munaya ce wannan, fetsararriya anzo a d'ora daga inda aka tsaya kenan?”. Murmushi nayi, Na kar6i Abdurraheem da Munubiya ta d'oramin a cinya, saida Na fara shayar dashi sannan Na kalli innaro, nace, “Innaro inhar kin shirya d'orawa daga inda kika tsaya muje zuwa mana, indai bazaki canjaba Munaya ma har abada zabata canjaba, miye laifin Innarmu danta d'akkoshi yana kuka?, rawa kika tarar tana masa ko wata tsiya? Yo nagama kema haka kikaita ma mutane kuka saikinje jiyyar abbanmu India, halan kema kunyar d'an farince.......”. Bankai k'arshen zancenba innaro ta d'ora hannu bisa ka ta aza mana kuka. Ni da Munubiya muka kuwa kwashe da dariya abinmu, a haka abbanmu ya shigo ya samemu, Innarmu tanata bama innaro hak'uri tak'i saurarenta. Girgiza kai kawai Abba yayi, Dan akan idonsa komi ya faru, hannu ya d'agama Innarmu alamar ta barta, zata fara magana ya girgiza mata kai. Shiru tayi takoma gefe, innaro saita k'ara k'arfin kukanta wanda harya fara jawo hankalin matan gidanmu, saidai babu damar zuwa kallon kwaf tunda a d'akine. Hannun innaro Abba ya kama ya zaunar da ita, cikin kwantar da harshe yace, “haba dai inna, yanzu dan ALLAH abinda akayi yarannan Na k'anana yanzuma shi za'a sake azaman dazasuyi Na wata 1 kacal dawasu kwanaki? Haba inna, minene Dan yaro yayi kuka Ai'sha ta d'akkoshi? Inna ina dad'i irin wad'annan abubuwan haka?”. Share hawaye innaro tayi, tace, “to naji Auwalu, indai nice bazan sake magana akan y'ay'anka da matarka ba....”. “da yafi”. Nafad'a ina murgud'a baki. Hararata Abba da Innarmu sukayi, Abba ya rik'e hannun innaro da sauri saboda k'ok'arin tashi da takeyi, “kiyi hak'uri Dan ALLAH inna, niba haka nake nufiba, da ni da abinda Na mallaka ai duk mallakinkine, nafad'a ne dan kawai a zauna lafiya yarannan sugama wanka kowa takoma gidan mijinta cikin salama, tunda kinga dai da yaran d'akinnan ne kawai irin wannan sa6anin ke shiga, yanzufa kika fito d'akin can kina tsokanar yarinyar Haleematu, mizaisa anan kuma hakan bazata kasanceba?”. “shikenan naji”. Abinda innaro tace kenan kawai ta mik'e ta fice. Abba ya bita da kallon kawai cike da takaici. Gaidashi mukayi, ya amsa yana had'iye 6acin ransa, ya tambayemu ya yara?, duk shiru mukayi muka kasa amsashi saboda kunya. Murmushi yayi, ya kar6i Abdurraheem daya gama shan nono, bayan Innarmu yabi d'akinta d'auke da yaron, dan tunda yamata magana tabar falon ta shige d'akinta. Zaune ya isketa a bakin gado tayi tagumi tana hawaye. Ya zauna kusada ita rungume da Abdurraheem, shiru yay yana kallonta, kusan mintuna biyu ya kwantar da yaron a bayansu yamatsa jikinta sosai yana kwantota jikinsa, “kiyi hak'uri Ai'sha, a halin inna babu wanda baki saniba yanzu, tunkan kizama mata a gareni kinsan wannan, to mizaisa hakan yasakaki kuka a yanzu? wani abin nata harda tsufa yanzu, amma kiyi hak'uri dan ALLAH”. “Ni ba kuka nakeyi saboda abinda inna takeminba, ina kukane saboda rashin jituwar da kullum take k'ara tasiri tsakaninta da yarannan, duk yanda naso hana girmamar irin wad'annan abubuwa n abun ya gagara, bai kamata ace laifina yana shafar jikokinta ba, jinintane fa su, idan ni tace banda asali sukuma ai itace asalinsu ko? wlhy Abbansu banason wad'annan abubuwan, wani lokacin zuciyata takan gaza d'auka”. “kiyi hak'uri, insha ALLAH komai mai wucewane, yakamata kuma zuwa yanzu kufad'a mana Ku su wanene? Kodan yaranki, dangin mahaifiya sunada matuk'ar tasiri a rayuwar yaro, banason zuwa nan gaba su zargi abinda ba haka yakeba, kodan gudun suma y'ay'ansu su taso suyi musu irin wannan tambayar”. Murmushin takaici inna tayi, ta d'ago daga jikinsa tana share hawayenta, suduka kallon Abdurraheem daketa motse-motse da k'afafu yana dungurin bayansu sukayi, Abba yay murmushi yana shafa kansa, sannan ya kalli inna yana fad'in “Ai'sha kodan wad'annan yaran, dolene watan watarana sai tarihinsu ya shafi tsokaci dangane da usilin mahaifiya, dukda nawa za'a kawo saifa naki ya taka rawar gani shima”. Inna tayi murmushi itama tana shafar kumatun Abdurraheem d'in, ta mik'e tsaye tana cewa “karka damu, a bani lokaci, da izinin ALLAH saisun taka tushena da k'afafunsu”. Abba ya d'auki Abdurraheem ya rungume yana fad'in “ALLAH ya tabbatar”. Mukan bamusan wainar da ake toyawaba, muna falo yara suna Neman haukatamu da kukansu, dukfa barci suke, amma Meena Na tashi kamar jira suma duk suka tashi masu kawunan kwakwar.😏 Haushi ya isheni nakusa make Amaturrahman datafi kowa daddagewa, saida Munubiya ta rik'e hannuna, “Sweetheart wai baki da hankaline? Uwarmi zaki daka ananne?”. Cikin tura baki nace, “yo Sweetheart haukatamu zasuyine?”. Daga inna har Abba dake fitowa baki suka gumtse suna dariya, “A lallai akwai aiki babba a gaban mata ashe?”. Inna tafad'a tana kallon Abba. Murmushi yayi shima yace, “babba kuwa Ai'sha”. Sai sukayi dariya. Hakanne yasakamu farga dasu, muka juyo muna kallonsu kowa fuska a tur6une, saboda haushin da yaran suka bamu. %%%%%%%%%%%%%%%% Bayan kammala gyara da Sauban yayi, Galadima ya mik'e zuwa cikin d'akin, zama yay ya kunna dukkan Computers d'in d'akin, saida komai ya dai-daita sannan yafara aikinsa cike da kwarewa, har lokacin sallar la'asar yana a d'akin, shiko gajiyar zaman jirginma bata damesa ba, bedroom d'insa ya dawo yay salla sannan ya sauka k'asa, Samha yabama Umarnin abinda yake buk'ata ya dawo yacigaba da aikinsa. Mintuna kad'an sai gata takawo masa. takan shiga shauk'i idan taga Uncle Sam yana sarrafa Computers d'innan, saitaji tamkar yafi kowa ilimin sarrafa Computer a duniya, amma tasan dole sai ansamu wanda suka fishi, badan karya maketa ba data tsaya taita kallonsa kawai. Shi baimasan tanayiba, hankalinsa nakan aikinsa gaba d'aya, dukda kansa daya fara ciwo kad'an-kad'an burinsa yakai inda yake hari. Saida duhun magriba ya gabato sannan yasamu kansa, yanzu ma a d'akin yay sallar magrib, ya zauna karatun Qur'an har time d'in isha'i yayi. Yana idarwa ya d'ora da shafa'i da wutiri, saboda barcin dake damunsa, soyake ya kwanta da wuri, duk abinda yakeyi kafin barci saida yay k'ok'arin kammalashi da k'yar sannan ya kwanta, dukda tunani da kewar yaransa Na neman 6atar da barcin nashi haka yayta yak'i da shi har barcin yaci Galadima akan tunanin. Samha tazo kawo masa dinner ta iske yanata barci cikin bargo, yama kashe hasken d'akin saina fitilar gefen gadon kawai itakuma haske kad'anne. Ajiye abincin tayi, dukda mawuyacine ya tashi domin cinsa, musamman da saida yamma yamaci d'azun.. (((+)))★(((+)))★(((+))) Yau kwananmu biyu kenan da dawowa gida, nayi waya dasu Samha duka amma banda uban gayya Galadima, bai nemini ba nima ban nemeshiba, Momma kam kullum sau biyu take kira muyi video call itada Abie, safe da yamma duk takan kirani. Muna kwance a gado ni da Munubiya, sai kuma mak'e murya takeyi suna waya itada yaa Marwan, koni dake kusa da ita ba komai nakejiba, nayi murmushin takaici ina juya kwanciyata zuwa d'ayan 6arin, danma Na daina jinta gaba d'aya, wata kwalla ta tararmin a ido, ba bak'in cikin kasancewar y'ar uwata a farin cikin nakeba, a', tausayin kainane ya kamani, maybe ita kad'aice zata koma gidan nata mijin banda ni, Na kalli yaranmu da laraba keta musu shirin barci, Aiyaan da Aryaan nata jagwalgwalasu, saurin d'auke k'ananun kwallar dake Neman zubomin nayi. Ni dai har barci ya d'aukeni bansan lokacin da Munubiya tagama wayarnanba, ban farkaba saida yaran suka farka da kuka, yanzu sabon iskancin da suka tsiro dashi kenan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76
- 77 Chapter 77
- 78 Chapter 78
- 79 Chapter 79
- 80 Chapter 80
- 81 Chapter 81
- 82 Chapter 82
- 83 Chapter 83