Chapter 8
Chapter 8
wayan yayi ya Mike,ba tare da ya bashi amsar Tambayar da ya Masa ba,har ya Kai bakin kofa Daddy yace "Ka dawo musu da dukiyan su ko Kuma mu had'u a kotu,kuma idan kace zaka bar gari wallahi tallahi duk inda ka shiga a fad'in Duniyar Nan zan Nemo ka" Waigowa yayi, yayi tsaki yace "To hell with you mu had'u a kotun" Sai ya fice, motar sa ya shiga duk hankalin sa a tashe Sai zufa yake ta goge wa da hannun sa, farar shaddan da ke jikinsa duk ya jike, Kai tsaye gidan sa ya nufa, yana parking d'akinsa ya shiga matar sa na ganin sa ta gane ba lafiya don ko sallama baiyi ba ya shige. Cikin sauri tabi bayan sa tarar dashi tayi a d'aki yana kaiwa Yana kawo wa, cikin nuna kulawa da damuwa Tace "Malam lafiya me ya Faru na ganka haka sai safa da marwa kake?" Murya na rawa yace "Rabi akwai matsala, akwai matsala wallahi" "Malam zauna ka fad'a min me ke faruwa?" "Zama? Ai banga ta Zama ba, ina naga ta Zama bayan asirina yana kokarin tonuwa?" "Asirin ka? Ban fahimta ba Malam me kake nufi da hakan?" "Ashe dama Munafukar matar Nan tana raye? Ashe bata mutu ba ita da d'anta?" Cikin rashin fahimta take kallon sa, yace "Dad'i na dake kanki baya ja wallahi ko kad'an Zainabu nake nufi Zainabu na Raye ita da d'anta" Dafe kirjin ta tayi Tace "Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, suna raye Malam? Amma ya akayi ka sani, na d'auka kasa an Kona inda suke?" "eh ni da ido na, na gani to Amma abinda ya d'aure min Kai hakan na nufin fa basu cikin d'akin don Babu yanda za a yi su tsira gas fa nasa aka sa hatta Wanda yasa wutan ya mutu da idona na gani fa" "ka gani ko Malam tun wanchan lokacin na Hanaka Amma kaki ji, yanzu gashi wa gari ya waya" "Rabi yanzu fa ba lokacin wannan bane..... " Nan ya sanar Mata yanda sukayi da Daddy, Rabi Tace "Malam ka maida musu dukiyar su, ai yanzu ka samu fiye da abinda ka samu agun su, idan ka bari ya kaika kotu duk abunda ka Tara za a Basu" "inaaa bazaiyu ba kin San tsawon shekaru nawa na yi ina tara kud'aden Nan kuwa?" " Ni kuwa na sani malam, ko dai barin garin zamuyi ne Kam?" "ai cewa yayi ko na bar gari Sai ya Nemo Ni" "Nikam wane ne haka? Da yake kokarin tozartamu?" "chairman ne fa Mus'ab Aminu" Zaro Ido tayi Tace "Eh lallai malam baka nemi zaman lafiya ba wallahi in dai baza ka maida musu ba, kasan mutumin Nan yanda yake da taimakon al'uma baya bari a cutar da kowa" "Na San da hakan, dole zan nemi mafita amm....." Kwankwasa kofar da akayi ne ya katse maganar da yake niyar yi. Cikin tsawa yace "Waye anan nace Waye ne?" Cikin sanyin murya Tace "Daddy wani mutumine ya kawo sako yace a baka" Rabi Tace "Shigo" Tana Mika Mata ta fita, Yana bud'ewa yaga tsammaci daga kotu kallon paper da yake ne yasa ta karb'a don ta gani girgiza Kai tayi Tace "lallai malam mutumin Nan dagaske yake, ranae Monday fa zaku shiga kotun" Tashi yayi ya fice ba tare da yace Mata uffan ba, ya shiga motar sa kenan ya hango Yan sanda guda biyu, jiki na rawa ya fito Yana kallon su, bayan sun gaisa 'daya daga cikinsu yace "Kaine Malam Hassan Umar?" Murya na rawa yace "Eh eh nine" ID card d'insu suka zaro suka nuna masa, "Yan sanda ne an turo mu da warrant arrest d'inka" "Ni Ni kuma, me me Kuma nayi?" "Idan mukaje office zakaji koma mene ne" Nan take suka zaro handcuffs suna kokarin Sanya Masa a hannun sa, cikin tashin hankali yake Kiran sunan ta "Rabi !! Rabi!!! Da gudu ta fito ita da 'ya'yan ta guda uku, Yaran na kuka rabi ma na kuka, har suka fice dashi suka sashi a mota. Suna zuwa police station suka tarar da Daddy, mummy, Umma, Ma'isha da Haisam duk suna zaune, cike da mamaki yake kallon su, hannu Daddy ya d'aga musu hannu, gani nayi sun cire Masa handcuffs din. Mikewa daddy yayi yace "Malam Hassan tun wuri ka taimaki kanka ka maida musu dukiyan su yanzu zan sa a sake ka idan Kuma kaki wallahi wallahi sai ka Raina kanka" Kallon Umma yayi yace "Zainabu kina jin abinda yake fad'a ko? Ki fad'a Masa gaskiya cewar dukiyar Nan Yaya nane ya bani" Umma fashewa tayi da kuka ta fice daga gun, mummy, Ma'isha da Haisam suka bi bayanta. Daddy ciza le'be yayi yace "Na lura kana da taurin kai, Amma kar ka damu...." Maida kallon sa yayi ga police d'in dake gefen sa yace "A kulle shi Kuma ban yarda a yi bailing sa ba, sannan kar a bari kowa yazo ganin sa ko da kuwa matarsa ce" Yana Kai Nan ya fice. Tarar dasu yayi a jikin mota Umma na kuka mummy na rarrashin sa, a yayin da Haisam ji yake kamar yaje ya shake baffan sa ya mutu ko zaiji sanyin abinda ke damin sa. Daddy yace "Ki daina kuka insha Allah komai zai wuce" "Alhaji dole nayi kaji abinda yake cewa fa, shi ya kashe min miji ya kwace dukiyar sa,sannan nima ya so kashe ni da d'ana Amma yana rayuwar sa hankali kwance" Mummy Tace "Kar ki damu ranar Monday komai zaizo karshe insha Allah, ke dai kawai ki fad'i duk abinda kika sani shine kad'ai zai sa a mishi hukunci dai dai da abinda ya aikata" Haisam yace "Amma mummy bamu da wani hujja, kinsan komai sai da evidence karshe ma a nemi a karyata mu" Daddy yace "matsala d'aya zamu samu shine evidence d'in da shi ya kashe shi Amma duk sauran zaizo Mana da sauki insha Allah, ku shiga mota mu tafi" mikawa Haisam key d'in motar akan ya jaa su, karb'a yayi duk suka shige, Kai tsaye gida suka nufo. Zaune suke a parlor,duk jikin su a sanyaye yake ganin kukan da Umma take yake ci yaki cinyewa Mummy Tace "Kukan na mene ne haka ya Isa Dan Allah" Cikin shesshekar kuka Tace "Wallahi ina ganin sa hankali yayi mugun tashi, tsayuwar da yayi a gabana sai naga kamar Ahmad ne Kai hatta muryar sa ma irin ta Ahmad ce, Hassan ya cuce ni bazan tab'a yafe Masa ba" ta karasa maganar tana kuka, Haisam Tashi yayi ya fice, Kai Tsaye d'akinsa ya nufa da gudu Ma'isha ta bi bayan sa. Daddy girgiza Kai yayi yace "Allah ya kyauta" ya nad'e garen sa ya shige d'akinsa. Ma'isha har cikin d'akin ta bishi, ya zauna a baki gado ya had'a Kai da gwiwa kuka yake sosai Mai sauti, Zama tayi a gefen sa baiji shigowar ta ba sai muryarta da yaji Tace "Ya Haisam." 'daga kansa yayi a hankali ya sauke idanunsa akan ta, kirkirerren Murmushi yayi, wata farar kyalle ta Mika Masa Murmushi ya Kuma yi yasa hannu ya karb'a ya share hawayen sa, bayan ya gama ya Mika Mata yace "Thank you" Murmushi kawai tayi tace "Ya Haisam kuka fa ba naka bane, addu'a ya kamata muyi Allah
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76