Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 70

Chapter 70

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,191 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

"Ameen" " But fa ina son kawartar Nan Wallahi" Kallon bana son rainin hankali Adnan ya Masa kana yace "To wani sabon iskancin naka xaka Fara Kenan" "A a wallahi tallahi sonta nake Kuma da aure" "Hmm lallai fa" " Kana ganin zata amince kuwa?" "Can't tell, but try your luck" Bai Kuma ce masa komai ba har suka Isa inda zasu. Mardiya ce zaune a office d'inta ta Lula duniyar tunani, ajiyar zuciya tayi kana a bayyane Tace "Meyasa nake ji kamar akwai abinda Adnan yake 'boyewa? Anya Adnan baida sa hannu acikin 'batan Ayrah kuwa? Mtswww ko ma mene ne zan bin cika" ta d'auki wayarta ta Fara latsawa. Bayan ta Dawo daga gun aiki ta tarar da su Umma, abba, Daddy, Isha, Mummy da Twins Sannan da Auta suna dinning suna cin abinci suna Hira, manta jiki tayi tana kallon su, ganin yanda suke farin ciki basu da wata damuwa, tsanar Isha ne ya sake ninkuwa a zuciyar ta. "You don't deserve to be happy, yayana ya rasa ransa Amma ko kad'an abun bai dame ki ba, hankalin ki kwance dake da ahalin ki, to wallahi Ni zan Zama sanadin rushewar farin cikin Nan tunda Ayrah ta kasa, Allah sarki Mummy da Daddy, Ina kewar ku sosai Yaya kasance kana son farin ciki Isha sama da komai a duniya Amma Bata damu da Kai" magana take a zuciyar ta tana matsar kwalla, batayi aune ba sai jin murya Umma tayi Tace " 'yata kin Dawo?" Had'e da dafe kafad'ar ta. Umma kallon fuskar ta tayi, cike da tausayi tasa hannu ta share mata Tace "Ki daina Kuka Mardiya, nasan is not easy ki d'auke mu tamkar family d'inki kinji, ki cigaba da musu addu'a kinji" Girgiza Kai tayi cikin Muryar kuka Tace "Nagode Umma" ta fashe da wani irin kuka, Umma rungume ta tayi tana rarrashin ta, Suma kallon su suke suna jin tausayin ta Amma Banda Haisam ya rasa dalilin da yasa ya ji bai yarda da yarinyar Nan ba, cigaba da cin abincin sa yayi hankali kwance, Roku hannun ta Umma tayi har dining table kaita ta jaa mata kujera ta zauna , sannan ta karb'i jakanta ta ajiye mata daga gefe, plate ta d'auka ta sa mata abinci sannan Tace "kici abinci" ta shafa kanta kana ta koma mazaunin ta, shiru wurin yayi baka jin komai sai Karan cokula, abincin take ci Amma Sam bata jin dad'in da, taci Kad'an kana ta mike had'e da fad'in "Nagode, bari na shiga ciki" Mummy Tace "Ki samu kiyi wanka sannan ki Dawo ki same mu a parlor ki daina zama ke Kad'ai" cike da kulawa take maganar, Murmushi Mardiya tayi had'e da fad'in "to mummy." Bayan ta Shiga d'akin ta ruwa ta watsa duk jikinta a Sanyaye , Bayan ta gama ne ta zauna a bakin mirror tana shafa mai, karar wayar ta taji tana ringing, ta duba don ganin wane ne, number ta gani ba suna, tsaki tayi bata d'aga ba an Kira har a karo na uku kana ta d'aga ta Kara a kunnen ta ba tare da tace komai ba daga 'dayan 'bangaren akace "Assalamualaikum" Murya kasa kasa ta and da "wassalam" " Barka da war haka Hajiya Mardiya" Jin an Kira sunanta ta d'an d'aga girar ta kamar yana kallon ta Tace "Yauwa barka dai" tana son gane ko wane ne. "Suna na Abdallah, abokin Adnan" Yar karamar Murmushi tayi had'e da fad'in "Oh Abdallah barka kana lafiya, ya gajiyan ku na d'azu Nagode fa" Shima Murmushin yayi yace "Bakomai, da fatan kina Lafiya?" "Alhamdulillah" "Ya aikin? An taso ko?" "Eh" "Allah ya taimaka dama na Kira ne naji lafiyar ki" "Allah sarki Nagode sosaiii" "Goodnight" Ta amsa da Night. "Ayrah Wai meyasa kike da shegen taurin Kaine?" A tsawce yake maganar kallon sa tayi sama da kasa kana ta kawar da kanta, ajiyar zuciya yayi ya Saira kansa ya lura idan ya mata da zafi bazai tab'a samun kanta ba. Durkusawa yayi a gaban ta ya hard'e Hannayen sa alamun roko kana yace "Ayrah Dan Allah Dan Annabi give me chance na tabbatar miki da cewar ina son ki, so na Haki ka" Kallon sa tayi kana ta murmusa Tace "Naji zan amince da hakan Amma ina da sharad'i" "Ina sauraron ki just name it and Ni zan yi miki shi" Mardiya na Gama shafa mai simple duguwar Riga ta Sanya a Jikin ta kana ta fito parlor kamar yadda mummy ta umurce ta, hirar su suke hankali kwance, sunayi suna dariya. Wuri ta samu ta zauna had'e da fad'in "Mummy na d'auka Kun koma gida fa" Murmusawa Mummy tayi kana Tace "A a yau muna nan, Umman ku ta kafa ta tsare akan dole mu kwana" "har naji dadi zamu Sha Hira kam" Isha ta ce "Sai kace dama tana hirar" " Ina yi man, gashi nazo ayi Dani" "toh you're welcome" Haisam zaman ta a gun duk yasa yaji ransa ya lalace mikewa yayi had'e da Mika yace "Nikam zan kwanta, bacci nake ji, sai da safe" Duk suka amsa da Saida safe, Kallon Isha ya tsaya yi ita ma kallon sa take gira ta d'aga Masa alamun ya dai? Sai da ya tabbatar hankalin su Mummy baya kansu kana murya kasa kasa yace "I Love You" rufe fuskar ta tayi da tafin hannun ta tana Murmushi, Mardiya kuwa duk abinda suke Akan idanun ta, tsaki tayi Wanda yasa Haisam yayi saurin kallon ta, wani irin Kallo ya mata Wanda yasa tayi saurin kawar da kanta, tana jin kirjin ta na duka uku², Isha ta lura da sauyawan fuskan nasa, cikin sanyin Murya Tace "Ya Haisam what happened?" Murmushi yayi mata Kana yace " Nothing ki hau online" Yana Kai Nan ya haura sama bai tsaya jin me zata ce ba, bin Bayan sa tayi da Kallo, kana ta maida kallon ta ga Mardiya wacce ta manta kanta tana kallon Haisam d'in, Isha da d'an karfi Tace "Duk maita Mutum wannan halittan ya fi karfin sa" sai kuma tayi kamar ba ita tayi ba, Abba yaji abinda Tace Sarai Amma bai gane da wa take ba, kawai ya batsar. Mardiya kuwa hararar Isha tayi had'e da mikewa Bata ce musu komai , Babu ma Wanda ya San ta bar gun Isha kuwa Tace a ranta "sai nayi maganin Yar iska dani kike zancen" Datan ta ta bud'e suka cigaba da chat d'insu da Yayan ta, Yana nuna Mata shi sam Baya son zaman Mardiya a gidan, Isha da itama ranta a 'bace yake da Mardiyan sai ta danne 'bacin ran natan tana ta bashi hakuri. "Ayrah kinyi shiru? Fad'a min mene ne sharad'in naki?" "Na'amince zan aure ka" Wani uban tsalle Adnan yayi yana Fad'in "Yessssssss!!! Yaja yes d'in sabida tsantsar farinciki, ita kanta Ayrah abinda Adnan d'in yayi ya bata dariya, sai taji ya burge ta, matse dariyar tayi Tace "Not so soon, Kar kayi farin ciki tsaya kaji sharad'ina tukunna" Zama yayi a gefen ta Yana kallon ta yace "Uhmnn, ina jinki" "Zaka barni na koma gida daga nan sai muyi auren mu" Murmushin gefen baki yayi kana ya mike yace "Zaki koma gida Amma Nima kiji nawa sharad'in" Tana kallon sa don Jin me zai ce.

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});