Chapter 32
Chapter 32
cikin gida. Ma'aruf kuwa natsuwar sa ya rasa yace "Wannan fa Yayan kine?" "Eh Yayana Ne" "Amma ya kuke dashi?" "My cousin, meyasa kake tambaya?" "No..... Bakomai naga Kuna Kama ne shiyasa" Murmushi kawai tayi gani kawai tayi ya mike yace zai tafi, ba don taso ba ta rakashi jikin motar sa, sai da taga fitan sa ta koma cikin gida. Kamar wasa Ma'isha tana final year kasantuwar pharmacy 5 years akeyi shi Kuma Haisam saura Masa shekara d'aya ya gama, Meerah kuwa ta dad'e da gamawa har tana aikin ta a medical center dake cikin garin gombe. Bayan Ma'isha tayi graduating Abba ya sa ma mata aiki itama a medical center hakan yasa kullum suna tare da Meerah, Haisam kuwa kullum cikin bibiyar Aysha yake da ta gabatar dashi gun iyayen ta Amma taki kullum amsar d'aya take bashi zan had'a ku idan lokaci yayi. Yau ma hakan Tace Masa "haba Habiby saurin me kake Ne Kam" "Aysha!!! Jikin ta ne yayi sanyi da jin yanda ya Kira sunanta ta amsa da "Na'am" tashi yayi ya zauna daga kwanciyar da yake wayan dake hannun sa ya maida d'ayan kunnen nasa yace "Anya kina Sona kuwa?" "Wannan wace irin tambaya ce Haka, kafi ko wa Sanin irin soyayyar da nake maka Kuma kake min irin Wannan tambayar?" "I doubt much gaskiya in dai dagaske kina sona ki barni na tura su Daddy gidan ku gudun Kar wani ya shige min" "Allah kar ka damu habiby next year fa zaka gama karatun ka kaga Ni Kuma sai Nan da 2 years na maka izini kana gamawa kazo ko da kuwa baka Sanar dani ba in yaso sai na gama a gidana ko" Dad'in maganar natan yaji Amma ya basar yace "Shikenan sai anjima zan Zo gidan" Da sauri Tace "A a kar kazo" Cike da mamaki yace "Meyasa?" "Umm.... Umm... Dama.... Dama Mom ce ta aike Ni zanje gidan kanwarta sai dai idan zamu had'u a Chan" "Okay wani unguwa ne?" "Federal low cost" "Oh unguwar mu nema idan kin Zo let me know" Bai jira yaji abinda zata ce ba ya kashe wayar, d'akin isha ya nufa ya tura kofar yaga wayam Bata nan. Layin ta ya Kira tana picking yace "Yau weekend ina Kika shi ne, tun safe ban ganki ba?" "Wallahi Yaya ina gidan Umma ne" "Shine baza ki fad'a min ba mu je tare?" "Am sorry na Shiga d'azu na ga kana baccine shiyasa" "okay Nima gani Nan zuwa" Ta amsa da "okay" sai ta kashe. Haisam dama da already yayi wanka Kaya kawai yasa ta fice, ya nufi gidan mummy, sai Bayan da iya sane ya tuna ya bar wayan sa a d'akin, ganin yanda Umman sa tayi kyau tayi fresh hakan yasa shi jin dad'i sosai. Umma na zaune a kasa, gata da babban ciki Wanda haihuwa yau ko gobe, Isha ganin tana wahala sosai ta fad'awa mummy zata zauna anan har sai Umma ta haihu Kuma ita kad'ai take aikin ta ga ciki, ita Ma'isha kullum mamaki take meyasa su Daddy basa son Yar aiki a gida. Aysha kuwa ta Kira layin Haisam yafi sau a irga har ta koma gida bai kirata ba , a ranar Kam raba dare yayi Yana rarrashin ta dakyar ya Samu ta hakura. Ma'aruf kuwa Duk sanda yake son ganin Isha Yana zuwa asibiti su gaisa sama sama yayi tafiyar sa ganin ta koma gidan su Umma yasa ya Fara zuwa gidan nasu, shi Sam bai San dalilin da yasa baya son ganin Haisam ba, Kuma hankalin sa ya kasa kwanciya shi duk tunanin sa Soyayya suke, sai da Meerah ta tabbatar Masa da cewar shakuwa ce kawai irin ba Yan uwa da Yan uwa. Wata Rana, cikin dare Isha taji Umma na Kiran sunan ta , da gudu ta fita ganin Umma a cikin jini yasa tayi matukar tsorata gashi Abba baya gari Sannan Kuma karb'an haihuwa ba 'bagaren ta bane, da gudu ta d'auko wayan ta ta Kira Haisam, kasantuwar unguwa d'aya suke bai Kai mintuna goma ba ya Isa da taimakon Sa da Isha suka sa ta a mota, suna Isa asibitin aka tabbatar musu da nakuda ce. _____________________________ Please comment Vote And share Milhaat ce Yar Terawa 🍃*DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhaart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* ```Kungiya d'aya tamkar da dubu.Masu Nazari da Aiki da Ilimi, Burin 'kungiyar a ko da yaushe shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻``` https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ____________________________________ *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM* Page 37&38 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ _Continuation........_ Haisam da Ma'isha na zaune a reception, Haisam Kam kwata kwata ya kasa nutsuwa ya zauna ya tashi ya fara kaiwa Yana kawo wa, ya dawo ya zauna. Ma'isha tausayin sa ya kamata sai ta tuno lokacin da Umma bata da lafiya, cike da kulawa Tace "Yaya please ka zauna Mana addu'ar mu take bukata a yanzu" "Princess wallahi na tsoratane sosai, mata suna wahala sosai wallahi duk Wanda yace zai tozarta mace ko ya wulakanta ta bai san ciwon kansa bane bare Kuma ace uwa" "Uhmn hakane Kam Amma fa ga Wanda ya sani, sabida wani abun idan kaji sai kaji Kamar Duniyar Nan an Tara zallan mahaukatane, kwanaki naji labarin wani ya Mari mahaifiyar sa akan kawai Tace Masa ya aske gashin Kan sa" "kin gani ko to wannan ina zaiga dai dai fisabilillahi" "Allah dai ya rabamu da iyayen mu Lafiya" Ya amsa da "Ameen summa ameen" Tace "Amma Yaya ka fad'a wa mummy zaka zo kuwa?" "A a wallahi a birkice na fito, Amma bara na Kira daddy" "shi da baya Nan?" "Eh gara shi d'in ya fad'a mata" "Toh" Kiran daddy yayi ya Sanar Masa shi Kuma ya Kira mummy ya fad'a Mata, mummy Kiran Haisam d'in tayi, tayi ta fad'a akan bai Sanar Mata ba suna Yara sun kaita asibiti idan ana bukatar wani abu fa, cikin Daren ta bugawa driver kofa kasantuwar yana zaune ne a boys quarters shi da Matar sa, d'auko motar sukayi gidan Umma suka fara nufa ta d'auko Duk wani abunda za a bukata kana suka wuce asibitin. Bayan
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76