Chapter 39
Chapter 39
ayyanawa a ransa, ganin Shirun yayi yawa Ma'isha cikin kuka Tace "Daddy me ya sami yayan, me ya faru haka har ya suma? Kuma naji kace yana aman jini how comes" Daddy kasa magana yayi haka ma abba, dukkanin su basu tunanin kowa sai Umma. Inda Farukh yake ta nufa cikin kuka Tace "Ya Farukh Dan Allah ka fad'a min me ya faru nasan kana gun kasan me ya sa meshi" Nan ya Sanar mata da komai Duk da shi bai San me dangantakar ta da Haisam ba, Umma fashewa tayi da Kuka Kan mummy ta karasa inda take tsaye ta Fad'i a sume, da gudu sukayi kanta, mummy Ce ta fara Kiran sunan "Nurse Nurse" nurses biyune suka karaso inda suke da gudu, gado suka d'auko suka tura ta suka kaita d'akin da yake kusa da Haisam,Nan Nan likitoci sukayi kanta. Abba Zama yayi a kasa ya fashe da kuka, kuka yake Sosai Kamar karamin yaro daddy ne ya durkusa a gaban sa yace "Haba Abdallah mene haka kake kuka Kamar wani karamin yaro, be a man mana." Cikin kuka yace "Dole nayi kuka Yaya Dole nayi kuka, why me? Why me wani laifi nayi wa Allah da yake horani Haka first was fauziya with my four kids and now Zainab and Haisam sannan fa Tana da karamin ciki, Yaya ina tsaron rasu Suma don wallahi idan na rasa su kuma zaku rasani" Daddy yace "Subhannallah haba Abdallah Kar kayi sab'o Mana, Allah Yana sonka Allah Yana jarraba bayin sa da yake so ne, ka d'auki hakan amatsayin kaddarar ka" "I can't Yaya bazan iya ba, fi kowa Sanin halin da nake ciki I was a sad and lonely man over 25 years sai yanzu da na fara samun kwanciyar hankali Kuma ace na rasa wannan am back to square one" Ma'isha kasa jurewa tayi ta bar gun ta na kuka mai tsuma zuciya, Farukh ne yabi bayan ta don ya samu ya kwantar mata da hankali kasantuwar yasan tana da ciwon zuciya. Abba sai surutai yake Kamar ya fara zarewa, mummy itama kukan take daddy ya rasa yadda zaiyi mikewa yayi yana safa da marwa ji yayi Mummy ta fashe da "Ihu Innalillahi wayyo mun Shiga uku da gudu tayi Kan Abba da ya Fad'i Daddy shima yayi kansa yana jijjiga shi yana Kiran sunan sa, nurses d'in da suke Kan Umma ne suka fito da gudu da taimakon Daddy suka kai shi d'akin da mummy ke ciki suka kwantar dashi a gadon dake gefen nata dama d'akin gadaje biyu ne aciki, Nan da nan wani likitan ya shigo shima ya fara duba shi. Mummy kuka take Sosai daddy ne ya rike ta suka fita suka zauna a kan kujera irin Wanda ake ajiye wa a ko wani ward, kwantar da ita yayi Yana d'an bubbuga Bayan ta yace "Ki daina kukan Nan please addu'a suke bukata a yanzu Dan Allah kiyi Shiru" "Alhaji taya za'ayi na daina kuka, son fa da Zainab Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un ga Nan Abdallah shima Wallahi tausayin sa nake ji, a cikin Yan awanni ta fita hayyacin sa" "To ya zamuyi? Haka Allah yaso Dan Allah I need you now kukan ki na tada min hankali Dan Allah Kar ki daina kina karya min zuciya" shiru tayi bata sake cewa komai ba ta cigaba da kukanta, shi Kuma bai daina bubbuga Bayan ta ba a haka har ta d'an samu relief. Likitocin Dake d'akin Su Abba da Umma ne suka fito a tare d'aya daga cikin su yace "Ku kwantar da hankalin ku, Suma sukayi duk su biyun, munyi musu allurar bacci zuwa anjima kadan zasu farka" Daddy ne ya amsa da "Mun gode" sukayi wucewar su, Bayan sun tafine likitocin da ke kan Haisam suka fito su uku, shugaban sune yace "Me ya sami Dr Haisam Haka?" Shiru sukayi d'ayan yace "Ya kamata musan me ke damin sa sabida musan ta yanda zamu 'bullo wa al'amarin" Daddy yace "Nasan Kun San yau ranar d'aurin auren sane ko?" A tare suka amsa da "Eh mun sani" 'dayan ya d'aura da fad'in "maganar zuwa gun dinner sa ma muke aka Sanar da mu an kawo patient Emergency, ga mamakin mu da muka zo muka tarar ashe shine Mara lafiyan" Ajiyar zuciya Daddy yayi yace "Auren ne aka fasa" A tare suka ce "subhannallah Abu baiyi dad'i ba" Sai kuma sukayi shiru suna kallon junan su. Farukh ne yabi bayan Ma'isha inda Meerah take ta nufa Meerah na ganin Isha a haka ta yi saurin tare ta had'e da zaunar da ita tana fad'in "Lafiya Isha? Me ya same ki Haka? Mutuwa akayi ne?" Muka take Banda sunan Haisam babu abinda take kira, cikin kukan ta Sanar da ita abinda Aysha tayi ka karasa maganar da fad'in "I know something was fishy about her,Ya Haisam ya cutar dani Kuma ya cutar da kansa Bayan irin Soyayyar da nake Masa Amma Baya gani Akan sa fa na kamu da ciwon zuciya,Ashe haukata kawai nake akan wata fa ya shiga halin da yake ciki"ta karasa maganar cikin kuka. Farukh Bayan ya karasa inda suke Jin maganar da Ma'isha keyi ya jaa da baya ya tsaya don Jin abinda take fad'a,sai da ya gama jin maganar da take ne ya samu gu ya zauna yace "Isha Yayan ki fa ba mutuwa yayi ba Suma yayi kuma Wallahi shima yana sonki kawai na kasa gane wane dalili ne yasa ya kasa fahimtar hakan, Dan Allah ki daina kukan Kuma Insha Allah hakan da ya faru zai Zama alhairi kinji" Meerah hannu tasa tana share mata hawaye Tace "kinji ko ai na Sha fad'a miki shima yana sonki, da ace kin bi shawarata kin Sanar Masa da Duk wannan bai faru ba" Farukh ne ya amsa da "Wannan hakane Amma kin san bamu muke sarawa kanmu Rayuwa ba we plan but Allah knows what is the best for us, kawai dai sai dai muyi fatan dacewa" Nan sukayi ta mata baki har ta samu ta daina kukan, sai ajiyar zuciya take sabida tayi kuka sosai Farukh pharmacy ya nufa ya Saya mata magani kana ya sayo ruwan sanyi bai dad'e ba ya dawo ya Mika Mata ta Sha, Duk su ukun suka nufi inda Su Daddy suke, suna Isa ganin daddy da mummy a tsaye sai Kuma likitoci biyu a gefen su, Farukh Mika musu hannu yayi suka gaisa yace "Dr Musa, Dr Sani ya jikin Haisam d'in hope everything is okay?" Dr musa yace "Gaskiya Akwai matsala Dr Farukh" Ma'isha Tace "Please Dr Musa wace matsala Kuma Bayan Wanda muke da ita a yanzu? Me ya sami Haisam d'in? Ko dai ya mutu ne kuke 'boye Mana?" Ta Karasa maganar tana matsar kwalla. Dr sani yace "No no bai mutu ba Pharm isha, yana Raye" "So tell me, what's wrong?" Ajiyar zuciya yayi yace "Ya Shiga comma." Ma'isha jaa da baya tayi ta jingina da jikin bango tana girgiza Kai had'e da fad'in "Shikenan Shikenan Shikenan Nima lokacin mutuwa ta tazo" Farukh yace "Haba Isha sai kace ba health practitioner ba? Kin fa San yanda comma take wani aranar ma zai farka wasu Kuma sukan d'auki sama da shekaru 20 suna comma Kuma ana sa ran zasu farka
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76