Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 58

Chapter 58

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,193 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

shi Yana zaune a inda ya bar shi, Zama tayi yace "Ba Zama zakiyi ba ki d'auki mayafin ki, zamu fita" magana yake ba tare da ya kalli inda take ba Tace "Ina zamu?" 'dago kai yayi kalle ta kana yace "Sayar da ke zanyi" sai ya ki cigaba da danna wayan sa. Tab'e baki tayi ta mike ta shige ciki, bata d'auki lokaci mao tsawo ba ta dawo jikinta sanye yake da hijab, d'ago kansa yayi ya kalle ta, Murmushi yayi kana yace "Kinyi kyau " Murmushi tayi Tace "Thanks" Mikewa yayi yace "Mu tafi ko?" Yayi gaba bai tsaya jin abinda zata ce ba, kallon sa tayi ta girgiza kai kana ta bi Bayan sa. Motar sa ya Shiga baka sidik Mercedes Benz sai sheko take, ganin ta nufo shi ne yayi saurin fita ya zaga ya bud'e mata kofar motar ta Shiga, ya maida ya rufe zagayawa ya kuma yi kana ya Shiga, Yana Shiga bai Tsaya 'bata lokaci ba ya sa wa motar key, tun Kan ya Isa yayi wa Mai gadi horn, da sauri ya wangale kofan Yana musu a Dawo Lafiya, suka fice daga gidan. Kallon ta yayi kana ya maida Kan sa Akan tukin da yake, yace "Isha" cikin wani irin low voice , kallon sa tayi had'e da fad'in "Na'am" "Kina so na kuwa?" "Uhmn Haba Ya ma'aruf wanann wace irin tambaya ce?" "Don't feel bad kawai akwai abinda nake so na fahimta ne" "Uhmnn ina sonka Mana , idan bana son ka me zai sa na aure ka?" Wani dogon ajiyar zuciya yayi bai ce mata komai ba ya cigaba da tukin sa itama ganin bai da niyar magana tayi shiru abin ta. Ganin sun doshi hanyar FTH ne hakan yasa Tace "Kar dai yaji maganar da muke d'azu da meerah?" A zuciyar ta take ayyana hakan. A bayyane kuma Tace "Me Kuma zamuyi a anan?" "Gani nayi kin kwana biyu baki ga Yayan ki ba" Kallon sa kawai tayi tana mamakin Hali irin na Ma'aruf "shi ko irin kishin Nan baya yi Kuma yasan irin soyyayar da nake yi wa Haisam?" Muryar sa taji yana Fad'in "Nasan zakiyi tunaniin ko bana sonki ko Kuma bana kishin ki, Isha Ina son ki Kuma ina kaunar ka babban burina shine na ganki cikin farin ciki da kwanciyar hankali, n aure kine a ganina zan iya Zama wani 'bangaren rayuwar ki Amma Naga alaman hakan bazaiyu ba" A dai dai Nan suka Shiga cikin asibitin sai da yayi parking kana ya kwantar da kansa a Kan kujera yace "Isha" d'ago Kai tayi ta kalle sa kana yace "ko yau d'in nan Haisam ya farka in dai zai karb'i soyyayar ki sannan ya soki kamar yadda kike son sa a shirye nake da na sake ki" zaro Ido tayi tana kallon sa, hannun yasa ya share mata hawayen da ya ke gangarowa daga fuskan ta Wanda ita kanta bata San sun zubo ba kirkirerren murya yayi "Isha I can sacrifice anything for you in this world har da ni kaina" bud'e marfin motar yayi ya fita ya Fara tafiya, ganin ta kasa fita daga motar ne ya dawo da baya ya bud'e mata marfin motar, kallon sa ta tsayayi ya zaro idanun sa had'e da mata gwalo yace "Rankashidad'e am a I safe?" Bata amsa mishi ba sai shesshekar kukan da take, ganin bata da niyar fita hakan yasa ya riko hannun ta suka bar wajen. ICU suka nufa, Zama yayi a waje yana jiran ta, itako Isha tafiya take kamar kwai ya fashe Mata a ciki. Bata dad'e a ciki kamar yadda ta Saba ba, ta fito ta hango shi Yana zaune Yana latsar wayar sa, Kallon sa ta tsayayi a zuciyar ta ce "Ya Allah me nake aikatawa ne haka, Innalillahi wa Inna ilaihirraji'un, Ma'aruf mutumin kirkii ne mai yasa ni bana son sa, gashi kyakkyawa son kowa kin Wanda ya rasa ,Astagfirullah ya Allah ka yafe min" Ma'aruf na d'ago kansa ya hango ta tana kallon sa murmushi yayi ganin irin kallon da take Masa hakan ya nuna hankalin ta baya jikin ta, mikewa yayi cikin tafiyar a nitse ya karaso inda take, ganin bata ma San ya karaso inda take ba yayi tafi, a razane ta kalle shi yace "Kina Lafiya kuwa?" Fashewa tayi da kuka, ta Fad'a jikin sa, rungumar ta yayi sai ta tsinci kanta da shigewa jikin sa, sai faman kuka take tana chusa jikin ta a nasa, Ma'aruf kuwa rikice wa yayi shi a ganin sa wani abunne ya sami Haisam d'in a gigice yake tambayar ta "Isha tell me what happened?" The more yana tambayar ta the more shi cries. " Isha please tell me what happened, me ya faru ne kike kuka haka?" 'dago kanta tayi ta Kalli fuskan sa kana ta Kara rugumar sa tana kuka, "Ya Salam" Ma'aruf yace. Ganin attention d'in Mutane ya faro dawo wa kansu ya janye ta daga jikin sa, hannun ta ya rike suka nufi motar sa, sata yayi a mota kana ya zaga ya Shiga haryanzu bata daina kukan ba. Iska ya hura murya kamar Fad'a yace "Oh My God , could please stop crying, Isha bana jin dad'in ganin ki a haka ki Fad'a min abinda ke damin ki Mana" ta tsorata da yanayin da ta gansa hakan yasa tayi shiru tana kukan kasa kasa, ganin Bata da niyar magana ya sa wa motar key. Kai tsaye gida suka nufa, a parking lot yayi parking, cire key d'in yayi ya shige cikin gida rai a 'bace da sauri tabi bayan sa , ganin yana kokarin haurawa bedroom da sauri ta nufi inda yake ta rungume shi ta baya, tana kuka mai tsuma zuciya, tsayawa yayi chak ya kasa motsi, Yana Jin kukan ta har cikin ransa shima hawayen ya fara zubarwa yana cizan leb'en sa. Cikin Muryar kuka Tace "Am sorry, am sorry Dan Allah ka yafe min" rike hannunta yayi had'e da juyawa yana fuskantar ta yace "Isha Ni fa babu abinda Kika min ki daina kukan Nan haka please" Yana mai share mata hawaye Tace "Bazan daina kuka ba har sai ka yafe min" "Sai na yafe Miki?" Cike da rashin fahimta ya mata tambayar. 'dago kanta yayi yace "Look at me Isha babi abinda Kika min ko da ma kin min to Wallahi na yafe miki duniya da lahira" fashewa Tayi da kuka tana fad'in "Ina son ka mijina Dan Allah ka yafe min, na kasan ce ba mace ta gari ba a gare ka, na kasa sauken hakki ka dake kaina" Shima rungumeta yayi Yana juya ta tamkar suna rawa , Murmushi yayi Mai d'an sauti yace "Wannan shine yasa kike kuka" Kai ta d'aga alamun eh, yace "Kar ki damu when ever you're ready ina Nan ina jiran ki, ban damu ba by The way bamu fa Kai sati ba so take your time Nasan abinda kike ji" Janye ta yayi daga jikinsa yana kallon fuskan ta jaaan hancin ta yayi yace "Cry cry baby Duk kin tada min hankali na d'auka wani abune ya Faru" Cikin shesshekar kuka Tace "Yanzu Dan Allah baka fushi dani?" Murmushi yayi yace "ko kad'an" Kallon kallon suka shigayiwa junan su, ko wannnen su

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});