Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 49

Chapter 49

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,202 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

Mota" Yar karamar dariya mardiya tayi a dai² Nan sun Isa jikin motar ta, Jingina jikinta tayi a jikin motar tana fuskantar Ayrah had'a hannayen ta tayi kana Tace "To Yar a Karuna Ni ba Gori nake Miki ba ke d'ince kin fiye mita dayawa, and karfa ki manta Ni dake Duk muna cikin matsala, Kud'in da ma na wani kuke ci" ta karasa maganar kasa² , Ayrah gyara tsayuwar ta tayi cikin Muryar tuhuma "Me kike ce?" Kirkirerren dariya tayi kana Tace "Nothing Shiga mu tafi please" Ayrah Tace "Anki a shigan salon ki sake min gori tafiya ta zanyi" ta juya da niyar tafiya, mardiya tayi saurin taro ta tana fad'in "Am sorry am Sorry Qawata ke Baki San wasa bane" tsaki kawai Ayrah tayi tana kokarin tafiya, rike hannun ta "kiyi hakuri Dan Allah , kizo muje gidan Baffan nata kin San karfe 4 zan Koma gun aiki" "Ke da aikin ya dama ba inace Ni gashi haryanzu na kasa samun aikin" "zaki samu Insha Allah, zo mu tafi" a zuciyar ta kuma Tace "Abinda ka shuka shi zaka girba (Niko nace ke d'in ma Allah ya barki da halin kine na wayon ki ko dabarar ki bace tasa Kika samu aiki ba). Motar suka Shiga suna Hira sama² har suka Isa gidan Abba, horn sukayi Mai gadi ganin Mardiya ya gane fuskar ta sabida jiya suka zo da Ma'aruf hakan yasa bai tsaya tambayar su gun wa suka Zo ba ya bud'e musu gate , a parking lot tayi parking motar ta kana suka fito. Cikin gidan suka nufa tun daga nesa suka hango Meerah da Isha, Ayrah Tace "Wai nikam Wannan wasu irin mayune kullum suna tare?" Mardiya Tace "Ni kaina ina mamakin irin qawancen Nan nasu, ban tab'a ganin qawaye irin suba" Wani irin Kallo Ayrah ta mata kana Tace "Kina nufin qawancen mu bai kai nasu ba?" Girgiza kai tayi had'e da dariya kana Tace "Ke dai ayi sha'ani Qawata namu ai ba irin nasu bane" suna maganar suna tafiya. Meerah na hango su ta tsaya chak, yayin da isha ke danne² a wayan ta jin Meerah ta tsaya ne yasa ta juya tana kallon ta had'e da fad'in "lafiya? ya naga kin tsaya mu tafi mana kin San Mummy na jiran mu." Meerah takaicine ya sa ta kasa magana, Isha ganin inda take Kallo hakan yasa ita ma tayi saurin kallon gun da take kallo, baki a bud'e take kallon su, a dai² Nan suka iso kallon kallon suka tsayi yiwa juna, Mardiya ce Tace "Kiyi hakuri Mun Zo gidan ku ba notice and we know that we're not welcome here, Amma Dan Allah inaso ku d'an ara mana Lokacin ku kad'an idan baza ku damu ba please" Cikin 'bacin Rai Meerah Tace "As you can see we are about to go out and you interrupted us so bamu da Lok....... " Isha ce ta katse ta da fad'in "Calm down Meerah let's listen to what they want to say" Meerah Tace "But Isha.... " "Please Meerah kiyi hakuri mu saurare su Kinji?" Shiru tayi had'e da kawar da kanta gefe. Isha Tace "Uhmn ina sauraron ki" Ayrah Tace "Da so samune mu zauna please" tab'e baki tayi had'e da d'aga kafad'a Tace "If you say so why not? mu shiga ciki" Riko hannun Meerah tayi don taga alama bata da niyar motsawa, ba don taso ba ta bi bayan ta, Isha juyowa tayi ganin suna tsaye Tace "ku Shigo Mana" sukayi gaba su Kuma suna biye da su. Mardiya da Ayrah kallon parlor suka tsaya yi ganin yanda aka Tsara gidan, gidan ya had'u iya haduwa sabida kud'i sunyi kuka anan gun, inda d'akinta yake suka nufa, Bayan sun Shiga d'akin ne Isha da Meerah suka zauna a bakin gado kana ta nuna musu sofa dake fuskantar su had'e da fad'in "Bismillah ku zauna" Zama sukayi, Bayan sun zauna ne Isha ta Mike had'e da fad'in "Ina zuwa please" Bata d'au lokaci ba ta Dawo hannunta d'auke da exotic sa glass cup guda biyu a gaban su ta ajiye kana ta koma ta zauna Tace "Bismillah ga abin Sha" A tare sukace "Thanks." Mardiya Tace "Isha nasan na cutar dake da kawar ki ko ince mun cutar daku Dan Allah find a place in your heart and forgive us what we did was very terrible but please Forgive us" Meerah Tace "hmm And what if we decide not to Forgive? Look idan baku da abin fad'a muna da abinyi" Ayrah Tace "Meerah ko kad'an Banga laifin ki ba, kina da right d'in da zaki Fad'i ko ma mene ne sabida an cutar dake, har ga Allah ko nice aka min haka da na dad'e da d'aukan mataki akai but please have a second thought on this" Mardiya Tace "Hakane zancen ki gaskiya ne Ayrah, and Isha please Kar laifina ya shafi Yayan Wallahi yana cikin wani hali bazai jure rashin ki ba" Murmushin gefen baki Isha tayi kana Tace "Da nayi niyar fasa auren nasa Amma zuwan ku yasa na Canza shawara zan auri Yayan ki Amma fa da sharad'i idan kikayi abinda nake so ina mai tabbatar miki da cewar bakina da Ma'aruf ranar Friday mai zuwa babu abinda zai sa a fasa shi sai dai in bana numfashi" Ajiyar zuciya Mardiya tayi kana Tace "Insha Allah Koma mene ne zanyi Wallahi" Meerah Tace "har da rantsuwa da dai ki bari kiji bukatar ta kamun nan ki rantse ko da yake ma baki San illan sa ba mtsww" Ayrah Tace "Isha Insha Allah zamuyi dukkanin abinda kukace muyi, ina da na sanin abinda na aikatawa d'an uwana na jini, na bi hud'ubar mahaifina sannan nayi amfani da maganganun sa na karya da gaskiya, a dalilina Ya Haisam ya kusa rasa ransa yana neman Almost 3 years kenan a kwance, bazan tab'a yafe wa kaina ba" ta karasa maganar cikin kuka. Isha Tace "Uhmn Haka Allah yaso kuma shima insha Allah zai farka ko ba yanzu ba" Ayrah Tace "Allah yasa" Duk suka amsa da ameen. Mardiya Tace "Isha ina sauraron ki mene ne sharad'in naki?" Isha kallon Meerah tayi, Meerah ma ta kalle ta Yar karamar dariya sukayi Wanda na kasa gane dalilin dariyar tasu, hankalin Ayrah da Mardiya yayi mugun tashi, kallon Kallo suka Shiga yiwa juna, Turo kofar da akayi ne yasa dukkannin su kallon kofar don ganin Wanda ya turo kofar. Kuyi hakuri da wannan please,ba yawa,haryanzu jikin ne ba dad'i, dakyar nake samun Daman typing d'in, nagode sosai da Addu'oin ku. _________________________ Masu tambayar complete d'in littafin Nan babu sabida 6th/01/2022 na fara typing, sabon littafine am just typing it. Ina Jin dad'in yanda kuke son book din Allah ya bar Kauna. Milhaat ce Yar Terawa [7/7, 10:02 PM] Miilhaat: 🍃 *DANGIN UBANA*🍃 Story & Written By Milhart Na zo muku da littafi Mai ban tausayi,cike da abun al'ajabi,wannan salon na daban ne. *🌍MANAZARTA* *WRITERS ASSOCIATION📚🖊* *M. W. A* *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIN RAHIM* Page 53&54 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number......

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});