Skip to content
bode

Hausa Novels Portal

Chapter 45

Chapter 45

Dangin Ubana Book 1 Complete Hausa Novel 1,201 words 0 views Progress saved
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});
Download Book

nace Mata "Big cola ne fa, ai da baki bud'e wani ba" Sai tace min "Eh Wallahi kan ne ba dad'i kin sanni da shirme" girgiza kaai kawai nayi na shanye Tass, kasantuwar ni masoyiyar coca cola ce. Tunda na Sha Wannan naji idanuna sun fara rufewa tun daga Wannan lokacin na manta kaina ban San a Ina nake ba Kuma ban san a wani Hali nake ciki ba, ji nayi na farka a razane d'ago kaina da zanyi na gan ni a kwance a jikin Usu, a razane na Mike nayi kokarin d'aga kafana naji sun min nauyi kallon kafan nawa nayi naga jini na bin kafana. Usu kuwa Kallo d'aya yamin ya kawar da kansa a kaina hakan ne ya tabbatar min da Usu ya min fyad'e, kuka na fara yi ina ja Masa Allah ya Isa shi da Mardiya bazan tab'a yafe musu ba, hijabi na d'auko Nasa ina tafiya da kyar har na fita bakin fate napep na Tara ya kaini gida, ina Shiga gida naci sa'a Mama na d'akin ta hakan yasa na Shiga ban d'aki na gyara jikina. Fitowa ta Kennan daga ban d'akin Mama ta Shigo d'aki na, ganin irin tafiyar da take ta tsaya Kallo na Tace "Me ya same ki a kafa na ga kina limping?" Cikin inda Inda nace "Mun dan yi accident ne a hanya na sai na d'an buga kafa na" Tace "Subhannallah Baki ji ciwo Sosai bako?" "Eh d'an bugewa nayi kuma nasha magani" "sannu Allah ya sauwaka, Ita Mardiya fa babu abinda ya same ta" ji nayi kamar na fashe da kuka da naji ta anbaci sunan ta amma nayi kokarin dannewa nace "Eh babu abinda ya same ta nice kadai na d'an buge" "toh Allah ya tsare na gaba" Na amsa da "Ameen" sai ta fice. Kwana nayi da zazzab'i chemist d'in unguwar mu na nufa na sayi magunguna nasha shine na samu zazzab'in ya d'an sauka, washe gari kuwa da mamaki na ina kwance a d'aki na ga shigowar Mardiya da Wannan Yarinyar da ta bamu abin Sha. Mikewa nayi saye cike da takaici nace "Ke me ya kawo ki gidan mu? Ke don ke karamar Mara kunya ce har kin iya tako kafar ki Cikin gidan mu har cikin d'akina?" Mardiya tace "Kiyi hakuri Wallahi ban San gidan su Usu bane" Murmushiin takaici nayi nace "Ke d'ince baki San gidan su Usu ba? Bayan gidan su Usu a unguwar nan yake? Mardiya kin cuce ni kin lalata min Rayuwa kin ruguza min tanadin da na dad'e ina yi,laifin me na Miki? Wallahi tallahi bazan tab'a yafe Muku ba" Wacce suka shigo tare ce tayi duguwar tsaki Tace "To sai me in baki yafe ba, kar fa ki d'auka Mun Zo neman yafiyar kine, munzo gidan ku ne don muga yanayin da kike ciki" Ji nayi kaina Yana juyawa na rasa abinda yake min dad'i cikin kuka nace "Dan Allah me na muku me na muku" Mardiya Tace "Wallahi babu abinda Kika Mana, Kin san ance mutunci ya fi kud'i but to me kud'i yafi mutunci, 5 mil ba wasa, zuwa yayi ya same mu, Akan mu taimaka Masa ya cimma burin sa Akan ki, kin San ke d'in akwai kayan Jin dad'i " dariya sukayi suka yi tafi kana ta d'aura da fad'in "Ya mana tayin 5mil each ni ko ina ganin Wannan kud'in bazan bari su wuce ni ba" Ji nayi kukan ma na kasa yi ina kallon su baki a bude nace "Yanzu akan kud'i? Akan kud'i Kika min Haka kefa kawatace?" "mtssw Wannan kuma ke ta shafa na samu kud'i na babu abinda ya Sha min Kai, Kuma idan Kika kuskura kikace Zaki Kai karan mu, ina mai tabbatar miki da sai Bashiir yaji labari, Kuma idan yaji kema kin San ba zai tab'a auren ki ba" Ayrah dariya ta Shiga yi Tace "Sunan wani abu wai fanko, anyways kar ki damu baza mu fad'a Masa ba , Amma idan Kika kuskura muka ji maganar nan a wani wuri sunan ki Sorry, Kinga Nan" wayarta Ciro a jaka ta nuna min Video d'ina da na Usu Ashe sunyi Mana video yanda yake lalata dani, ta d'aura da fad'in "Nasan Mardiya baza ta rasa number sa ba zamu tura Masa" Mardiya Tace "Idan kunne ya ji?" Had'e da rike kunnen ta, Ayrah ta karasa mata zancen nata da "Jiki ya tsira" suka yi dariya had'e da barin d'akin na dad'e a tsaye agun kukan da nake yi ma na kasa yi. Zama nayi na had'a Kai da gwiwa ina kuka Jin an turo kofar ne na yi shiru had'e da d'ago kaina don ganin Wanda ya shigo ina ganin Isha ce ta nufeta da gudu na fad'a jikin ta ina kuka, Allah sarki Isha kawar arziki Nan ta zaunar dani tayi tayi ta rarrashi na, Bayan na fad'a mata abinda aka min har ta fini Shiga tashin hankali, tashi tayi akan zataje ta sanarwa su Mama don a bi min hakki na, na hanata sannan na fad'a mata dalili na da farko taki Amincewa bayan hakurin da nayi ta bata ta fasa fad'a musu ba don ta so ba. Ana saura kwani hud'u bikina Bashir yazo gidan mu, ina ganin yanayin sa, sai da naji gaba na ya Fad'i dama a parlor baba muke Hira Bayan Mun gama gaisawa sai nace "Kana Lafiya kuwa,naga fuskar ka wani irine" "Lafiya na Lau,akwai maganar da nake so muyi dake ne" Na amsa Masa da "ina sauraron ka" yace "so nake ki rakani wani wuri yanzu" Zaro Ido nayi nace "Yanzu da daren nan? A a gaskiya Ni ba inda zanje Mama ba za ta bari na fita ba yanzu" Murmushin gefen baki yayi yace "Amma Kuma kin iya zuwa 'dakin samari ko?" Cikin rashin fahimta nace "Ban fahimce ka ba" Yace "Kar ki rainawa kanki hankali don wallahi kinyi kad'an ki rainan hankali" wayan sa ya ciro ya nuna min Video nan, kuka na fara yi ina fad'in "Wallahi ba da sani akayi ba" Amma yaki yarda da magana ta mikewa yayi yace "A Daren nan Nima ina so ki bani abinda Kika bashi in ba Haka ba goben Nan zan turo a karb'a min kayana da na kowo gidan ku" Durkusawa nayi a akasa da gwiwowina ina rokon sa "Dan Allah Bashir Kar ka min haka, Dan Allah da wanne zanji Dan Allah ka rufa min asiri." Yace "Idan kina so na rufa miki asiri kiyo yadda nace kawai" ganin dagaske yake hakan yasa na share hawayena na Mike had'e da fad'in "Bashir idan baka fasa aure na ba kai ba d'an halak bane, kayi Duk abinda zakayi Amma Ni bazan bika" Cike da mamaki yace "Oh haka kikace, kinje ki ba wa wani ni da zan aure ki ne baza ki bani ba?" "Tunda aure na zakayi sai ka jira idan aka d'aura auren sai na baka kaina Amma wallahi bazan tab'a aikata abinda kake so na aikata ba" Yace "Allah ya sauwake na had'a jini na da Yar iska karuwa" "uhmn naji na gode Amma Allah Shaida nane ban a hayyacina aka yi hakan ba" "Dallah gafara makaryaciya inda fyad'e aka miki ai da kin fad'a a gida ko ni

Table of Contents

Chapters

76 chapters
  1. 1 Chapter 1
  2. 2 Chapter 2
  3. 3 Chapter 3
  4. 4 Chapter 4
  5. 5 Chapter 5
  6. 6 Chapter 6
  7. 7 Chapter 7
  8. 8 Chapter 8
  9. 9 Chapter 9
  10. 10 Chapter 10
  11. 11 Chapter 11
  12. 12 Chapter 12
  13. 13 Chapter 13
  14. 14 Chapter 14
  15. 15 Chapter 15
  16. 16 Chapter 16
  17. 17 Chapter 17
  18. 18 Chapter 18
  19. 19 Chapter 19
  20. 20 Chapter 20
  21. 21 Chapter 21
  22. 22 Chapter 22
  23. 23 Chapter 23
  24. 24 Chapter 24
  25. 25 Chapter 25
  26. 26 Chapter 26
  27. 27 Chapter 27
  28. 28 Chapter 28
  29. 29 Chapter 29
  30. 30 Chapter 30
  31. 31 Chapter 31
  32. 32 Chapter 32
  33. 33 Chapter 33
  34. 34 Chapter 34
  35. 35 Chapter 35
  36. 36 Chapter 36
  37. 37 Chapter 37
  38. 38 Chapter 38
  39. 39 Chapter 39
  40. 40 Chapter 40
  41. 41 Chapter 41
  42. 42 Chapter 42
  43. 43 Chapter 43
  44. 44 Chapter 44
  45. 45 Chapter 45
  46. 46 Chapter 46
  47. 47 Chapter 47
  48. 48 Chapter 48
  49. 49 Chapter 49
  50. 50 Chapter 50
  51. 51 Chapter 51
  52. 52 Chapter 52
  53. 53 Chapter 53
  54. 54 Chapter 54
  55. 55 Chapter 55
  56. 56 Chapter 56
  57. 57 Chapter 57
  58. 58 Chapter 58
  59. 59 Chapter 59
  60. 60 Chapter 60
  61. 61 Chapter 61
  62. 62 Chapter 62
  63. 63 Chapter 63
  64. 64 Chapter 64
  65. 65 Chapter 65
  66. 66 Chapter 66
  67. 67 Chapter 67
  68. 68 Chapter 68
  69. 69 Chapter 69
  70. 70 Chapter 70
  71. 71 Chapter 71
  72. 72 Chapter 72
  73. 73 Chapter 73
  74. 74 Chapter 74
  75. 75 Chapter 75
  76. 76 Chapter 76
(adsbygoogle = window.adsbygoogle || []).push({});