Chapter 24
Chapter 24
shine ta fad'akar ta kuma Nishad'antar da masoyan ta.🤙🏻``` https://www.facebook.com/107980080946102?referrer=whatsa ____________________________________ *Wannan labarin kirkirarren labarine ban yarda a chanza min labari ba Wanda ya chanza bamu yafe ba.* Ina alfahari da rubutu,sabida alkalami yafi takobi🗡️🗡️🗡️ *BISMILLAHIR RAHAMANIR RAHIM* Page 29&30 _Akwai ingantaccan maganin🌴🌴 gyaran nono na hausa, ga wanda yake da bukatar maganin zai iya tuntubar wannan number...... 08089965176 domin karin bayani, maganin ya samu lambar yabo saboda ingancinsa, yana amfani sosai domin yana ciko da nono yana kuma sanya k'iba dai misali, babu almundahana babu cuta babu cutarwa sahihin magani ne, idan kin shayar sau goma, ina mai tabbatar miki da cewa daga ranar da ki ka fara amfani da maganin zaki ga sauyi, domin yana gyara mace, zawarawa da 'yan mata kuma kada a barku a baya za ku iya mallakar naku maganin domin in ganta kanki, bahaushe yace idan kana da kyau ka kara da wanka!...ga masu bukatar sari ko sayan d'aya muna KANO muna turawa kowane gari 2k kacal zaki mallaki naki kafin ya kare wallahi sai kin ga sauyi.......*SIYAN NAGARI MAI DA KUDI GIDA*! Idan matsalar nono kike fama da ita kukanki ya 'kare da ikon Allah._ _Continuation.........._ Hannun ta ta sauke daga kirjin ta, ta sauke ajiyar zuciya Tace "Kai Yaya ka tsoratani yaushe ka Shigo?" Tashi yayi ya zauna daga kwanciyar da yake yana kallon cikin idonta tabbas ta tsoro ta, yace Mata "Yanzu na Shigo, Ashe dama kin ganni?" Kawar da kanta tayi kamar bata ji abinda yace ta hard'e hannun ta, ba ganin bata da niyar bashi amsa ya taso ya nufe ta, dab da ita ya tsaya ganin har yanzu bata kula shi ba ya hannu ya riko hannayen ta, wani abu taji yarrrr tun daga tsakiyar kanta I'xuwa tsakiyar kafan ta, da sauri ta zare hannun ta. Murmushi yayi yace "Princess wai haryanzu fushi kike dani?" 'dan ja da baya tayi ganin haka Shima ya matsa kusa da ita ta Kuma yin taku biyu ta baya shi Kuma yayi Taku biyu ya iso ta haka sukayi tayi har ta Kai jikin bango, hannu yasa ya riko hab'arta ya juyo kanta ta kalle shi. Idonta cikin nasa, idanun ta sun taro ruwa kiris suke jira su zubo ganin hakan yaji duk ba dad'i kasa da murya yayi yace "I Know I hurt you, Dan Allah ya Isa Haka bana jin dad'in hakan duk kin Canza min kamar ba princess d'ina ba" Hawayen da dama jira suke suka fara bin juna suna sauka da sauri yasa hannu yasa ya fara share mata yana girgiza kansa, ya kuma cewa "Am sorry My princess" Ma'isha runtse idanun ta tayi tana Jin dad'in sunan My princess wani 'bagaren Kuma ji take kamar zuciyar ta zata fashe sabida gani take kalmominsa na yaudara ce kawai. Haisam ganin hawayen Ma'isha ba karamin tada masa hankali yake ba ji yake kamar yasa harshen sa ya lashe hawayen ta yana Kuma ji kamar ya rungumeta a jikin sa ko zata ji saukin abinda take , amma bazai iya hakan ba sabida tun ba halaliyar sa bace. Riko hannun ta yayi ya zaunar da ita a bakin gado, ya durkusa a gaban ta hannun ta d'aya ya rike yasa hannun ta a tsakiyan hanyen sa, murza hannun nata yake a hankali yana kallon ta, banda hawayen dake zubiwa daga idanun ta Babu abinda take yi, har sai da ya ga ta daina kukan ya sake hannun nata sannan ya mike ya zauna a gefen ta. Still yana kallon ta yace "Please ki daina kukan haka bana son ganin ki haka, sannan dama na kawo miki labari ne Mai dad'i Amma na fasa" ya karasa maganar kamar yaro d'an shekara 3. Kirkirerren Murmushi tayi Tace "Na daina kukan fad'a min me ya faru?" "Zan fad'a miki but da sharad'i" "Ina jinka" "Sai kin min alkawarin kin daina fushi dani tukunna zan Sanar dake" " Toh ai Yaya Kaine kake fushi dani bani ba, tunda ko magana ma ka daina min ko da na maka ma amsa mara dad'i nake Samu ko Kuma kaki kulani, Kuma in ba Ni na maka magana ba bakayi min" "I Know, kin 'bata min raai ne wallahi, Amma yanzu komai ya wuce am sorry kinji?" "Hmm Shikenan" Mikewa yayi Tace "Haa'ah ina zuwa Kuma?" "Sallah zanyi kema na San bakiyi ba, so ki tashi kiyi" " Labarin da kace zaka fad'a min Kuma fa?" "zan fad'a miki anjima ki tashi kiyi sallah, bye" ya d'aga mata hannu kana ya fice. Murmushi tayi tana kallon hannun ta da ya rike ta dad'e tana kallon hannun ta tana shafawa da d'ayan hannun nata, sai gani nayi ta Mike firgit ta shige ban d'aki ko me ta tuna oho. Haisam Bayan yaje Masallaci ya dawo ya koma d'akin sa yayi wanka, wando three quarter baki ya saka sannan ya saka Riga armless Shima baki kana ya fito yazo part d'insu Daddy zaman sa ke da wuya daddy ya Shigo da Baki sun Kai su Shida cikin girmawa ya gaidasu suka amsa, Kai tsaye dinning suka wuce, mummy da Umma suka fito daga kitchen da sauran abincin Nan aka Shiga gaishe gaishe, Bayan sun ajiye suka koma d'akin mummy suka fara hirarsu a chan. Bayan su Daddy sun gama cin abinci suka d'an zanta har karfe takwas da rabi kana suka gama meeting d'in, fita sukayi duka a tare har wurin motocin su ya raka su duk suka wuce Amma banda mutum d'aya a tare suka sake shigowa a parlor suka zauna Haisam ya musu sannu suka amsa Nan fa daddy suka fara Hira ba kakkautawa da mutumin nan. Ma'isha kuwa Saida tayi sallar Isha kana ta fito daga d'akin doguwar Riga ce Mara nauyi sannan ta saka baby hijab ta fito parlor ganin su daddy da gudun ta karasa inda suke ta fad'a jikin Daddy tana fad'in "Daddy sannu sa dawo wa" Ya amsa da "Yauwa Daughter." Dariya sukayi mutumin nan da suke tare da daddy yace "Oh daddyn ki kawai Kika gani baki ganni bako?" "Laaah Abba wallahi ban gan ka ba, ina wuni?" Ta d'an duka ya Masa da "Lafiya su Isha manyan mata kaga yarinyar Nan yanda ta girma" Daddy ya amsa da "Wallahi kuwa kasan girman mace" "girman mace ai kamar Taki ake saka musu, ya school d'in dai dafatan ana kokari?" "Eh daddy Alhamdulillah" "Allah ya taimaka" "Ameen nagode Abba" Wanda ta Kira da Abba ne ya Kara maida kallon sa ga Haisam a karo na sau ba adadi ya maida kallon sa ga daddy yace "Yaya ina ta zuci zucin tambayar ka wane ne wannan?" Murmushi daddy yayi yace "Ai shine yaron da nake baka labarin sa kwanaki" "Ohhhh" girgiza kai yayi alamun ya tuna kana ya d'aura da fad'in "Haisam ko?" Yana kallon Haisam d'in, cikin girmawa Haisam yace "Eh yallab'ai" Murmushin gefen Baki yayi yace "Yallab'ai Kuma Haisam Kuma ka Kira Yaya na da Daddy? Ko Ni ban Kai a kirani da Daddy bane?" Ya karasa maganar a sigar wasa, sosa keya Haisam yayi yace "A'a ba Haka bane" Gyara Zama Abba yayi yace Sunana Abdallah Aminu Tahir, d'aga Malam Tahir Mus'ab wannan da kake gani.... Yana nuna daddy haisam ya kalli daddy kana ya maida kallon sa gare shi,ya
Table of Contents
Chapters
- 1 Chapter 1
- 2 Chapter 2
- 3 Chapter 3
- 4 Chapter 4
- 5 Chapter 5
- 6 Chapter 6
- 7 Chapter 7
- 8 Chapter 8
- 9 Chapter 9
- 10 Chapter 10
- 11 Chapter 11
- 12 Chapter 12
- 13 Chapter 13
- 14 Chapter 14
- 15 Chapter 15
- 16 Chapter 16
- 17 Chapter 17
- 18 Chapter 18
- 19 Chapter 19
- 20 Chapter 20
- 21 Chapter 21
- 22 Chapter 22
- 23 Chapter 23
- 24 Chapter 24
- 25 Chapter 25
- 26 Chapter 26
- 27 Chapter 27
- 28 Chapter 28
- 29 Chapter 29
- 30 Chapter 30
- 31 Chapter 31
- 32 Chapter 32
- 33 Chapter 33
- 34 Chapter 34
- 35 Chapter 35
- 36 Chapter 36
- 37 Chapter 37
- 38 Chapter 38
- 39 Chapter 39
- 40 Chapter 40
- 41 Chapter 41
- 42 Chapter 42
- 43 Chapter 43
- 44 Chapter 44
- 45 Chapter 45
- 46 Chapter 46
- 47 Chapter 47
- 48 Chapter 48
- 49 Chapter 49
- 50 Chapter 50
- 51 Chapter 51
- 52 Chapter 52
- 53 Chapter 53
- 54 Chapter 54
- 55 Chapter 55
- 56 Chapter 56
- 57 Chapter 57
- 58 Chapter 58
- 59 Chapter 59
- 60 Chapter 60
- 61 Chapter 61
- 62 Chapter 62
- 63 Chapter 63
- 64 Chapter 64
- 65 Chapter 65
- 66 Chapter 66
- 67 Chapter 67
- 68 Chapter 68
- 69 Chapter 69
- 70 Chapter 70
- 71 Chapter 71
- 72 Chapter 72
- 73 Chapter 73
- 74 Chapter 74
- 75 Chapter 75
- 76 Chapter 76